ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Babu Wanda Zai Fice Daga NNPP Da Zai Girgiza Siyasar Kwankwaso – Kofa

by Sadiq
4 years ago
Zaben 2019

Tsohon Dan Majalisar Tarayya na Kananan Hukumomin Kiru da Bebeji, Abdulmuminu Jibril Kofa, ya ce a matakin da ake babu wani dan siyasa da zai fice daga jam’iyyar NNPP da zai girgiza siyasar Kwankwaso.

Yayin wata hira da gidan talabijin na Channels, Kofa, ya bayyana zamansa mai magana da yawun yakin neman zaben dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar NNPP.

  • Da Dumi-Dumi: ‘Yansanda Sun Cafke Wani Dan Bindiga Dan Shekara 20 A Kaduna
  • Za Mu Sa Kafar Wando Daya Da Masu Fasa Bututun Mai

A kan batun sauyin sheka da ake tunanin Sanata Ibrahim Shekarau zai yi daga NNPP zuwa wata jam’iyyar, Kofa ya ce ko Sanatan ya sauya sheka, jam’iyyarsu za ta kai labari a 2023.

ADVERTISEMENT

Kofa, ya ce a 2019 an ga aya a zaben Kano, inda duk manyan ‘yan siyasa suka tare a APC, amma Rabiu Kwankwaso ya nuna musu nauyinsa, don haka babu wani wanda zai iya kada NNPP, domin Kwankwaso ya rike siyasar Kano, a cewarsa.

“A 2019 abun takaici, dukkaninmu sai mu ka bi Ganduje, Shekarau, Kabiru Gaya, Barau Jibrin, Kawu Sumaila, duk wani babba a Kano ya bi Ganduje, Me ya faru? Kwankwaso shi kadai a gefe guda, ya doke mu a zaben gwamna. Abin da ya faru a zaben, abin da aka gani ne, amma a gaskiya ya ci zabe.

LABARAI MASU NASABA

PRP Ta Musanta Zargin Cewa Kwankwaso Ya Sayi Fom 69 Domin Kwace Jam’iyyar

Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP

“Saboda haka idan ana zawarcin Shekarau, me ake nema ne, na gagara fahimtar wannan. Babu wanda zai bar NNPP a Kano da zai jijjiga Kwankwaso.”

Kamar yadda gidan rediyon Nasara da ke Kano ya wallafa, ya ce, Kofa wanda ya wakilci Kiru da Bebeji a majalisar tarayya ya ce hakan bai nufin yana kokarin cin mutuncin tsohon gwamna Shekarau, illa martani ga rade-radin da ake yi na cewa Malam Shekarau na neman barin NNPP, yayin da wasu ke zargin ya sa labule da sauran ‘yan takarar 2023.

A makon da ya gabata ne dai rahotanni suka karade kafafen watsa labarai cewa Shekarau zai fice daga NNPP sakamakon gaza cika masa wasu alkawura, abin da Kwankwaso ya ce sam ba haka bane, kuma babu wata matsala a tsakaninsu.

MASU ALAKA

2023: Gwarazan Jam’iyyu A Karon Battar Zaben Shugaban Kasa
Siyasa

PRP Ta Musanta Zargin Cewa Kwankwaso Ya Sayi Fom 69 Domin Kwace Jam’iyyar

June 22, 2026
Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP
Siyasa

Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP

June 22, 2026
ADC Ta Sake Tabbatar Da Ibrahim Khalil A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano Na 2027
Siyasa

ADC Ta Sake Tabbatar Da Ibrahim Khalil A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano Na 2027

June 21, 2026
Next Post
Da Dumi-Dumi: An Kori Shugaban Jam’iyyar APC Na Jihar Enugu Daga Jam’iyyar

Da Dumi-Dumi: An Kori Shugaban Jam'iyyar APC Na Jihar Enugu Daga Jam'iyyar

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.