• English
  • Business News
Sunday, August 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dangantakar Sin Da Afrika Ta Kai Wani Mataki Da Babu Wanda Zai Iya Lalatawa

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Ana Gab Da Kammala Ginin Hedkwatar Africa CDC Da Sin Ta Dauki Nauyinsa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yayin da ake gab da adabo da shekarar 2022, jajirtattun injiniyoyin Sin da Afrika, sun himmantu ba dare ba rana, domin ganin kammaluwar ginin hedkwatar cibiyar kandagarki da yaki da yaduwar cututtuka ta Afrika wato Afrika CDC.

Duniya ta shaida yadda annoba a wuri kan iya yaduwa cikin kankanin lokaci har ma ta zama barazana ga duniya baki daya. Yadda irin wadannan annoba ke barkewa a Afrika, na bukatar shiri da dauki na gaggawa.

  • Babban Jami’in Africa CDC Ya Jinjinawa Kasar Sin Bisa Hadin Gwiwarta A Fannin Sarrafa Rigakafin COVID-19 A Afirka

Yadda Sin ta dauki nauyin ginin hedkwatar cibiyar kandagarki da dakile yaduwar cututtuka ta Afrika, gagarumar gudunmawa ce da za ta taimaka wajen kyautata lafiyar al’ummar nahiyar, inda za su shafe lokaci mai tsawo suna cin moriyarsa. Haka kuma, ya sake nuna cewa a ko da yaushe, Sin tana tare da al’ummar Afrika, kuma a shirye take ta share musu hawaye.

Bayan taron ministocin kungiyar FOCAC a shekarar 2018 ne kasar Sin ta bayyana aniyarta ta daukar nauyin ginin hedkwatar cibiyar Africa CDC, tare da sanya dukkan kayayyakin da ake bukata a ciki.

A watan Yulin 2020 ne kuma aka rattaba hannu kan yarjejeniyar ginin. Zuwan aski gaban goshi, ya shaida mana cewa kasar Sin na gudanar da wannan aiki ne yayin da take fama da aikin yaki da cutar COVID-19 a gida da kuma yanayi na rashin tabbas da ake fama da shi a duniya. Wato duk da wadannan kalubale, ba ta yi kasa a gwiwa ko dakatar da aikin ba, sai ma dukufa da ta yi don ganin an kammala shi kamar yadda aka tsara.

Labarai Masu Nasaba

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

Hakika kasar Sin ta amsa sunanta na babbar kasa kuma babbar yaya, wadda ke burin ganin ci gaban ’yan uwanta kasashe masu tasowa, inda a ko da yaushe, take nacewa wajen aiwatar da ayyuka na gani na fada, masu amfani da al’ummar Afrika ke matukar bukata. Wannan ya kai dangantakar sassan biyu wani matsayi da ba za a iya lalatawa ba.

Mun riga mun san cewa, annoba ba ta san iyakar kasa ko jinsi ba, don haka, tana iya bulla a ko ina. Sai dai, yadda aka shiryawa tunkararta zai ba da damar cin galaba a kanta. Taimakon kasar Sin na ginin hedkwatar da samar da kayayyaki a cikinsa, zai karawa nahiyar Afrika karfin tunkara da yaki da duk wata annoba da ka iya bullowa nan gaba, lamarin da zai rage asarar rayuka da ma dogaro da kasashen waje ta fuskar samar da magunguna ko riga kafi ba, domin mun ga yadda kasashe dake kiran kansu manya, suka yi ta boye alluran riga kafin COVID-19 domin amfanin kansu ba tare da tunawa da wadanda ba su da karfi ba. Haka zalika, wannan cibiya na iya zama wani dandali da kwararrun Sinawa za su taimaka wajen bunkasa kwarewar takwarorinsu na Afrika. (Fa’iza Mustapha)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

DA DUMI-DUMI: An Sace Mutum 16 A Wani Sabon Hari Da Aka Kai Jihar Kaduna

Next Post

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 8 A Borno

Related

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu
Daga Birnin Sin

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

3 hours ago
Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO
Daga Birnin Sin

Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

4 hours ago
CMG Ya Kaddamar Da Gangamin Tattara Fina-Finai Da Talabijin Da Aka Samar Bisa AI A Los Angeles
Daga Birnin Sin

CMG Ya Kaddamar Da Gangamin Tattara Fina-Finai Da Talabijin Da Aka Samar Bisa AI A Los Angeles

5 hours ago
Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba
Daga Birnin Sin

Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba

6 hours ago
Bangaren Kasuwancin “E-Commerce” Na Kasar Sin Ya Karu Sosai A Watanni 7 Na Farkon Bana
Daga Birnin Sin

Bangaren Kasuwancin “E-Commerce” Na Kasar Sin Ya Karu Sosai A Watanni 7 Na Farkon Bana

7 hours ago
Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama
Daga Birnin Sin

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

1 day ago
Next Post
Sojoji Sun Kai Hari Sansanonin IPOB Sun Kwato Bama-Bamai Da Bindigu A Ebonyi Da Enugu

Sojoji Sun Kashe 'Yan Ta'adda 8 A Borno

LABARAI MASU NASABA

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

August 23, 2025
Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

August 23, 2025
CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

August 23, 2025
Yadda Ake Alale

Yadda Ake Alale

August 23, 2025
Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

August 23, 2025
Matsalar Al’ada Da Ciwon Mara Ga Mata

Matsalar Al’ada Da Ciwon Mara Ga Mata

August 23, 2025
CMG Ya Kaddamar Da Gangamin Tattara Fina-Finai Da Talabijin Da Aka Samar Bisa AI A Los Angeles

CMG Ya Kaddamar Da Gangamin Tattara Fina-Finai Da Talabijin Da Aka Samar Bisa AI A Los Angeles

August 23, 2025
Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba

Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba

August 23, 2025
Bangaren Kasuwancin “E-Commerce” Na Kasar Sin Ya Karu Sosai A Watanni 7 Na Farkon Bana

Bangaren Kasuwancin “E-Commerce” Na Kasar Sin Ya Karu Sosai A Watanni 7 Na Farkon Bana

August 23, 2025
Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

August 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.