ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dangantakar Sin Da Afrika Ta Kai Wani Mataki Da Babu Wanda Zai Iya Lalatawa

by CMG Hausa
3 years ago
Sin

Yayin da ake gab da adabo da shekarar 2022, jajirtattun injiniyoyin Sin da Afrika, sun himmantu ba dare ba rana, domin ganin kammaluwar ginin hedkwatar cibiyar kandagarki da yaki da yaduwar cututtuka ta Afrika wato Afrika CDC.

Duniya ta shaida yadda annoba a wuri kan iya yaduwa cikin kankanin lokaci har ma ta zama barazana ga duniya baki daya. Yadda irin wadannan annoba ke barkewa a Afrika, na bukatar shiri da dauki na gaggawa.

  • Babban Jami’in Africa CDC Ya Jinjinawa Kasar Sin Bisa Hadin Gwiwarta A Fannin Sarrafa Rigakafin COVID-19 A Afirka

Yadda Sin ta dauki nauyin ginin hedkwatar cibiyar kandagarki da dakile yaduwar cututtuka ta Afrika, gagarumar gudunmawa ce da za ta taimaka wajen kyautata lafiyar al’ummar nahiyar, inda za su shafe lokaci mai tsawo suna cin moriyarsa. Haka kuma, ya sake nuna cewa a ko da yaushe, Sin tana tare da al’ummar Afrika, kuma a shirye take ta share musu hawaye.

ADVERTISEMENT

Bayan taron ministocin kungiyar FOCAC a shekarar 2018 ne kasar Sin ta bayyana aniyarta ta daukar nauyin ginin hedkwatar cibiyar Africa CDC, tare da sanya dukkan kayayyakin da ake bukata a ciki.

A watan Yulin 2020 ne kuma aka rattaba hannu kan yarjejeniyar ginin. Zuwan aski gaban goshi, ya shaida mana cewa kasar Sin na gudanar da wannan aiki ne yayin da take fama da aikin yaki da cutar COVID-19 a gida da kuma yanayi na rashin tabbas da ake fama da shi a duniya. Wato duk da wadannan kalubale, ba ta yi kasa a gwiwa ko dakatar da aikin ba, sai ma dukufa da ta yi don ganin an kammala shi kamar yadda aka tsara.

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Hakika kasar Sin ta amsa sunanta na babbar kasa kuma babbar yaya, wadda ke burin ganin ci gaban ’yan uwanta kasashe masu tasowa, inda a ko da yaushe, take nacewa wajen aiwatar da ayyuka na gani na fada, masu amfani da al’ummar Afrika ke matukar bukata. Wannan ya kai dangantakar sassan biyu wani matsayi da ba za a iya lalatawa ba.

Mun riga mun san cewa, annoba ba ta san iyakar kasa ko jinsi ba, don haka, tana iya bulla a ko ina. Sai dai, yadda aka shiryawa tunkararta zai ba da damar cin galaba a kanta. Taimakon kasar Sin na ginin hedkwatar da samar da kayayyaki a cikinsa, zai karawa nahiyar Afrika karfin tunkara da yaki da duk wata annoba da ka iya bullowa nan gaba, lamarin da zai rage asarar rayuka da ma dogaro da kasashen waje ta fuskar samar da magunguna ko riga kafi ba, domin mun ga yadda kasashe dake kiran kansu manya, suka yi ta boye alluran riga kafin COVID-19 domin amfanin kansu ba tare da tunawa da wadanda ba su da karfi ba. Haka zalika, wannan cibiya na iya zama wani dandali da kwararrun Sinawa za su taimaka wajen bunkasa kwarewar takwarorinsu na Afrika. (Fa’iza Mustapha)

Sin
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
Daga Birnin Sin

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
Daga Birnin Sin

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos
Daga Birnin Sin

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Next Post
Sojoji Sun Kai Hari Sansanonin IPOB Sun Kwato Bama-Bamai Da Bindigu A Ebonyi Da Enugu

Sojoji Sun Kashe 'Yan Ta'adda 8 A Borno

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.