ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dangantakar Sin Da Afrika Ta Kai Wani Mataki Da Babu Wanda Zai Iya Lalatawa

by CMG Hausa
4 years ago
Sin

Yayin da ake gab da adabo da shekarar 2022, jajirtattun injiniyoyin Sin da Afrika, sun himmantu ba dare ba rana, domin ganin kammaluwar ginin hedkwatar cibiyar kandagarki da yaki da yaduwar cututtuka ta Afrika wato Afrika CDC.

Duniya ta shaida yadda annoba a wuri kan iya yaduwa cikin kankanin lokaci har ma ta zama barazana ga duniya baki daya. Yadda irin wadannan annoba ke barkewa a Afrika, na bukatar shiri da dauki na gaggawa.

  • Babban Jami’in Africa CDC Ya Jinjinawa Kasar Sin Bisa Hadin Gwiwarta A Fannin Sarrafa Rigakafin COVID-19 A Afirka

Yadda Sin ta dauki nauyin ginin hedkwatar cibiyar kandagarki da dakile yaduwar cututtuka ta Afrika, gagarumar gudunmawa ce da za ta taimaka wajen kyautata lafiyar al’ummar nahiyar, inda za su shafe lokaci mai tsawo suna cin moriyarsa. Haka kuma, ya sake nuna cewa a ko da yaushe, Sin tana tare da al’ummar Afrika, kuma a shirye take ta share musu hawaye.

ADVERTISEMENT

Bayan taron ministocin kungiyar FOCAC a shekarar 2018 ne kasar Sin ta bayyana aniyarta ta daukar nauyin ginin hedkwatar cibiyar Africa CDC, tare da sanya dukkan kayayyakin da ake bukata a ciki.

A watan Yulin 2020 ne kuma aka rattaba hannu kan yarjejeniyar ginin. Zuwan aski gaban goshi, ya shaida mana cewa kasar Sin na gudanar da wannan aiki ne yayin da take fama da aikin yaki da cutar COVID-19 a gida da kuma yanayi na rashin tabbas da ake fama da shi a duniya. Wato duk da wadannan kalubale, ba ta yi kasa a gwiwa ko dakatar da aikin ba, sai ma dukufa da ta yi don ganin an kammala shi kamar yadda aka tsara.

LABARAI MASU NASABA

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Hakika kasar Sin ta amsa sunanta na babbar kasa kuma babbar yaya, wadda ke burin ganin ci gaban ’yan uwanta kasashe masu tasowa, inda a ko da yaushe, take nacewa wajen aiwatar da ayyuka na gani na fada, masu amfani da al’ummar Afrika ke matukar bukata. Wannan ya kai dangantakar sassan biyu wani matsayi da ba za a iya lalatawa ba.

Mun riga mun san cewa, annoba ba ta san iyakar kasa ko jinsi ba, don haka, tana iya bulla a ko ina. Sai dai, yadda aka shiryawa tunkararta zai ba da damar cin galaba a kanta. Taimakon kasar Sin na ginin hedkwatar da samar da kayayyaki a cikinsa, zai karawa nahiyar Afrika karfin tunkara da yaki da duk wata annoba da ka iya bullowa nan gaba, lamarin da zai rage asarar rayuka da ma dogaro da kasashen waje ta fuskar samar da magunguna ko riga kafi ba, domin mun ga yadda kasashe dake kiran kansu manya, suka yi ta boye alluran riga kafin COVID-19 domin amfanin kansu ba tare da tunawa da wadanda ba su da karfi ba. Haka zalika, wannan cibiya na iya zama wani dandali da kwararrun Sinawa za su taimaka wajen bunkasa kwarewar takwarorinsu na Afrika. (Fa’iza Mustapha)

Sin
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya
Daga Birnin Sin

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

July 16, 2026
Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030
Daga Birnin Sin

Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 16, 2026
Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara
Daga Birnin Sin

Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

July 16, 2026
Next Post
Sojoji Sun Kai Hari Sansanonin IPOB Sun Kwato Bama-Bamai Da Bindigu A Ebonyi Da Enugu

Sojoji Sun Kashe 'Yan Ta'adda 8 A Borno

LABARAI MASU NASABA

Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano

Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano

July 17, 2026
Yadda NDLEA Ke Fatattakar Dillalan Miyagun Kwayoyi Na Kudancin Amurka

Yadda NDLEA Ke Fatattakar Dillalan Miyagun Kwayoyi Na Kudancin Amurka

July 17, 2026
Gwamnan Da Bai Taba Samun Mulkin Jihar Kano Ba

Gwamnan Da Bai Taba Samun Mulkin Jihar Kano Ba

July 17, 2026
An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi

An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi

July 17, 2026
NPA Ta Tara Kudin Shiga Naira Biliyan 758.2 A 2024

Dalilin Da Ya Sa Kungiyar NCTR Ta Jinjina Wa Shugaban NPA

July 17, 2026
Yunkurin Dauda Lawal Na Bunkasa Bangaren Ma’adanan Jihar Zamfara

Yunkurin Dauda Lawal Na Bunkasa Bangaren Ma’adanan Jihar Zamfara

July 17, 2026
Gbajabiamila Ya Maka Daraktan Bogi Na PFIPC Kotu, Ya Nemi Diyyar Biliyan 15

Gbajabiamila Ya Maka Daraktan Bogi Na PFIPC Kotu, Ya Nemi Diyyar Biliyan 15

July 17, 2026
Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

July 17, 2026
Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

July 17, 2026
Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

July 16, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.