• English
  • Business News
Friday, August 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dansandan Da Ya Ki Karbar Cin Hancin Miliyan 150 Ya Samu Shatara Ta Arziki

by Sulaiman and Rabi'u Ali Indabawa
1 year ago
in Labarai
0
cin hanci
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Duk da hali na matsin rayuwa da wahalhalu da ake fama da su da gobe, bai hana wasu mutanen kirki aikata ayyukan kirki ba, kamar yadda aka samu wani jami’in dansanda da ya ki kabar cin hancin zunzurutun kudi har Naira miliyan 150, wanda kuma a dalilion haka ne ya samu kyautar fili a Babban Birnin Tarayya Abuja.

Dama masu iya magana na cewa a ko da yaushe na Allah ba sa karewa, kuma shi dai alheri danko ne ba ya faduwa kasa banza.

  • An Jinjinawa Matakan Kare Hakkin Bil Adama Na Kasar Sin Yayin Zaman Taron MDD
  • Kanana Hukumomin Kano Da Jigawa 23 Na Kan Gaba Wajen Fuskantar Ambaliyar Ruwa – NEMA

Rahotanni sun bayyana cewa, an karrama wannan Sufetan ‘yansanda mai suna (SP) Ibrahim Ezekiel Sini, ta hanyar bashi kyautar fili a Abuja. Wannan dansanda ya ki karbar cin hancin Naira miliyan 150 ne daga hannun wani dan kasuwa a Legas mai suna Akintoye Akindele, wanda kuma shi ne ya kafa ‘Platform Capital.

Kwamishinan ‘Yansandan Babban Birnin Tarayya Abuja, CP Benneth Igweh, wanda ya ba da kyautar filin a madadin abokan aikin ‘yansandan, ya ce halin da SP Sini nuna ya sa rundunar ‘yansandan Nijeriya (NPF) alfahari.

Har ila yau, daya daga cikin wadanda suka shirya taron karramawar, Prince Chukwuemeka Okoye, Shugaban Kamfanin Begas Homes, ya ce halin da SP Sini ya nuna zama abin koyi kuma ya kamata ya zaburar da sauran jama’a da ‘yan Nijeriya su lura cewa rundunar ‘yansandan Nijeriya tana da mutane masu gaskiya da rikon amana.

Labarai Masu Nasaba

Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

’Yansanda Sun Kama Jagororin ‘Yan Bindiga A Abuja, Sun Ƙwato Makamai Da ₦7.4m

A cewar sa, “Wannan hali da SP Sini ya nuna ba wai kawai ya kara wa kansa da kuma rundunar ‘yansandan Nijeriya kwarin guiwa ba ne, har ma da karfafa gwiwar wasu da dama da su tsaya tsayin daka wajen yaki da cin hanci da rashawa da kuma bin ka’idojin da’a. Wannan dabi’a tasa za ta ci gaba da zama abar yabawa, gami da nuni da cewa duk tsanani ana samun mutanen kirki.

“Ba a yi wannan karramawa kawai don yaba kyawawan halayen Sufeto Ibrahim Sini ba, sai don a yi nuna ga al’umma su yaba wa daidaikun mutane masu nagarta da halin kirki.

“Muna so mu nuna cewa rundunar ‘yansandan NIjeriya tana da jami’ai da suka kware, kuma suna da kwarin gwiwa wajen gudanar da aikin dansanda mai ma’ana kuma su zama abin koyi.”

Yayin da yake yaba wa halin Sini, Okoye ya ce taron na daya daga cikin sauran hanyoyin nuna godiya da suke da shi don halayensa na yabawa.

An ce dan kasuwar a cikin tuhumar ya yi watsi da zargin da aka yi masa na ya fata ba da ajiye Naira miliyan 50 a matsayin cin hanci ga tawagar masu binciken IGP wanda ke karkashin jagorancin SP Sini.
Ya kara da cewa “Kin karbar Naira miliyan 150 ya nuna tsoron Allah, gudun duniya da kuma kwarewar aiki, duk wadannan halaye ne da jami’i Ibrahim ya nuna.”

Idan dai za a iya tunawa, Akindele, wanda wata babbar kotun tarayya da ke birnin tarayya ta tsare a gidan yari na Kuje, ana zarginsa da bai wa dansandan cin hancin Naira miliyan 150 domin ya janye binciken da yake yi akansa.

A cewar tuhume-tuhumen, an bayar da cin hancin ne ga ‘yansanda domin ba shi izinin tserewa kasar waje da kuma rubuta masa rahoto mai kyau bayan bincike.

An kama Akindele ne akan wata takardar korafi da Summit Oil International Limited ya mika wa shugaban ‘yansanda da ake zarginsa da damfarar kamfanin kudi Dala miliyan 5,636,397 da kuma wasu Naira miliyan 73,543,764.

A halin da ake ciki, SP Sini ya ce dalilin da ya sa ya ki amincewa da kudin cin hancin shi ne saboda ya gwammace ya samu natsuwa, ya ci gaba da yin gaskiya ga aiki da kare mutuncin rundunar ‘yansandan Nijeriya da kuma kiyaye mutuncinsa da na iyalansa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Cin HanciGaskiyahali nagari
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Ɗage Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Bauchi

Next Post

Ƙarancin Wayewa da Samar Da Labaru Masu Kyau Ke Durƙusar Da Kannywood

Related

Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba
Labarai

Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

43 minutes ago
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Jagororin ‘Yan Bindiga A Abuja, Sun Ƙwato Makamai Da ₦7.4m

3 hours ago
Likitoci Sun Gano Wuka Da Aka Burma A Kirjin Wani Mutum Tsawon Shekara 8 
Labarai

Likitoci Sun Gano Wuka Da Aka Burma A Kirjin Wani Mutum Tsawon Shekara 8 

4 hours ago
Hukumar Kwastam Ta Kama Kayan Maye Na Miliyan 680 A Katsina
Labarai

Hukumar Kwastam Ta Kama Kayan Maye Na Miliyan 680 A Katsina

5 hours ago
Za A Yi Ruwan Sama Na Kwanaki 3 A Jere A Wasu Jihohin Nijeriya – NiMet
Labarai

Za A Yi Ruwan Sama Na Kwanaki 3 A Jere A Wasu Jihohin Nijeriya – NiMet

5 hours ago
An Ceto Mutane 41, 4 Sun Rasu A Hatsarin Kwale-Kwale A Sakkwato
Labarai

An Ceto Mutane 41, 4 Sun Rasu A Hatsarin Kwale-Kwale A Sakkwato

8 hours ago
Next Post
Ƙarancin Wayewa da Samar Da Labaru Masu Kyau Ke Durƙusar Da Kannywood

Ƙarancin Wayewa da Samar Da Labaru Masu Kyau Ke Durƙusar Da Kannywood

LABARAI MASU NASABA

Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

August 22, 2025
Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

August 22, 2025
Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025

Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025

August 22, 2025
Ruben Dias Ya Rattaba Hannu Kan Sabon Kwantiragi A Manchester City

Ruben Dias Ya Rattaba Hannu Kan Sabon Kwantiragi A Manchester City

August 22, 2025
Manyan Jami’an JKS Sun Ziyarci Jami’ai Da Mazauna Birnin Lhasa

Manyan Jami’an JKS Sun Ziyarci Jami’ai Da Mazauna Birnin Lhasa

August 22, 2025
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi

’Yansanda Sun Kama Jagororin ‘Yan Bindiga A Abuja, Sun Ƙwato Makamai Da ₦7.4m

August 22, 2025
Likitoci Sun Gano Wuka Da Aka Burma A Kirjin Wani Mutum Tsawon Shekara 8 

Likitoci Sun Gano Wuka Da Aka Burma A Kirjin Wani Mutum Tsawon Shekara 8 

August 22, 2025
Jihar Xizang Ta Baiwa Duniya Mamaki Da “Canji Mai Girma” Da Ta Samu a Cikin Shekaru 60 Da Suka Gabata 

Jihar Xizang Ta Baiwa Duniya Mamaki Da “Canji Mai Girma” Da Ta Samu a Cikin Shekaru 60 Da Suka Gabata 

August 22, 2025
Hukumar Kwastam Ta Kama Kayan Maye Na Miliyan 680 A Katsina

Hukumar Kwastam Ta Kama Kayan Maye Na Miliyan 680 A Katsina

August 22, 2025
Za A Yi Ruwan Sama Na Kwanaki 3 A Jere A Wasu Jihohin Nijeriya – NiMet

Za A Yi Ruwan Sama Na Kwanaki 3 A Jere A Wasu Jihohin Nijeriya – NiMet

August 22, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.