• English
  • Business News
Tuesday, September 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dansandan Da Ya Ki Karbar Cin Hancin Miliyan 150 Ya Samu Shatara Ta Arziki

by Sulaiman and Rabi'u Ali Indabawa
1 year ago
in Labarai
0
cin hanci
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Duk da hali na matsin rayuwa da wahalhalu da ake fama da su da gobe, bai hana wasu mutanen kirki aikata ayyukan kirki ba, kamar yadda aka samu wani jami’in dansanda da ya ki kabar cin hancin zunzurutun kudi har Naira miliyan 150, wanda kuma a dalilion haka ne ya samu kyautar fili a Babban Birnin Tarayya Abuja.

Dama masu iya magana na cewa a ko da yaushe na Allah ba sa karewa, kuma shi dai alheri danko ne ba ya faduwa kasa banza.

  • An Jinjinawa Matakan Kare Hakkin Bil Adama Na Kasar Sin Yayin Zaman Taron MDD
  • Kanana Hukumomin Kano Da Jigawa 23 Na Kan Gaba Wajen Fuskantar Ambaliyar Ruwa – NEMA

Rahotanni sun bayyana cewa, an karrama wannan Sufetan ‘yansanda mai suna (SP) Ibrahim Ezekiel Sini, ta hanyar bashi kyautar fili a Abuja. Wannan dansanda ya ki karbar cin hancin Naira miliyan 150 ne daga hannun wani dan kasuwa a Legas mai suna Akintoye Akindele, wanda kuma shi ne ya kafa ‘Platform Capital.

Kwamishinan ‘Yansandan Babban Birnin Tarayya Abuja, CP Benneth Igweh, wanda ya ba da kyautar filin a madadin abokan aikin ‘yansandan, ya ce halin da SP Sini nuna ya sa rundunar ‘yansandan Nijeriya (NPF) alfahari.

Har ila yau, daya daga cikin wadanda suka shirya taron karramawar, Prince Chukwuemeka Okoye, Shugaban Kamfanin Begas Homes, ya ce halin da SP Sini ya nuna zama abin koyi kuma ya kamata ya zaburar da sauran jama’a da ‘yan Nijeriya su lura cewa rundunar ‘yansandan Nijeriya tana da mutane masu gaskiya da rikon amana.

Labarai Masu Nasaba

Sojoji Sun Harbe Wasu ‘Yan Ta’adda 2 A Taraba

Tinubu Ya Taya Amusan Da Gumel Murnar Samun Nasarori A Ɓangarori Daban-daban

A cewar sa, “Wannan hali da SP Sini ya nuna ba wai kawai ya kara wa kansa da kuma rundunar ‘yansandan Nijeriya kwarin guiwa ba ne, har ma da karfafa gwiwar wasu da dama da su tsaya tsayin daka wajen yaki da cin hanci da rashawa da kuma bin ka’idojin da’a. Wannan dabi’a tasa za ta ci gaba da zama abar yabawa, gami da nuni da cewa duk tsanani ana samun mutanen kirki.

“Ba a yi wannan karramawa kawai don yaba kyawawan halayen Sufeto Ibrahim Sini ba, sai don a yi nuna ga al’umma su yaba wa daidaikun mutane masu nagarta da halin kirki.

“Muna so mu nuna cewa rundunar ‘yansandan NIjeriya tana da jami’ai da suka kware, kuma suna da kwarin gwiwa wajen gudanar da aikin dansanda mai ma’ana kuma su zama abin koyi.”

Yayin da yake yaba wa halin Sini, Okoye ya ce taron na daya daga cikin sauran hanyoyin nuna godiya da suke da shi don halayensa na yabawa.

An ce dan kasuwar a cikin tuhumar ya yi watsi da zargin da aka yi masa na ya fata ba da ajiye Naira miliyan 50 a matsayin cin hanci ga tawagar masu binciken IGP wanda ke karkashin jagorancin SP Sini.
Ya kara da cewa “Kin karbar Naira miliyan 150 ya nuna tsoron Allah, gudun duniya da kuma kwarewar aiki, duk wadannan halaye ne da jami’i Ibrahim ya nuna.”

Idan dai za a iya tunawa, Akindele, wanda wata babbar kotun tarayya da ke birnin tarayya ta tsare a gidan yari na Kuje, ana zarginsa da bai wa dansandan cin hancin Naira miliyan 150 domin ya janye binciken da yake yi akansa.

A cewar tuhume-tuhumen, an bayar da cin hancin ne ga ‘yansanda domin ba shi izinin tserewa kasar waje da kuma rubuta masa rahoto mai kyau bayan bincike.

An kama Akindele ne akan wata takardar korafi da Summit Oil International Limited ya mika wa shugaban ‘yansanda da ake zarginsa da damfarar kamfanin kudi Dala miliyan 5,636,397 da kuma wasu Naira miliyan 73,543,764.

A halin da ake ciki, SP Sini ya ce dalilin da ya sa ya ki amincewa da kudin cin hancin shi ne saboda ya gwammace ya samu natsuwa, ya ci gaba da yin gaskiya ga aiki da kare mutuncin rundunar ‘yansandan Nijeriya da kuma kiyaye mutuncinsa da na iyalansa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Cin HanciGaskiyahali nagari
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Ɗage Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Bauchi

Next Post

Ƙarancin Wayewa da Samar Da Labaru Masu Kyau Ke Durƙusar Da Kannywood

Related

Sojoji
Labarai

Sojoji Sun Harbe Wasu ‘Yan Ta’adda 2 A Taraba

26 minutes ago
Buhari Ya Taya Amusan Murnar Lashe Zinari A Gasar Tsere Ta Duniya
Labarai

Tinubu Ya Taya Amusan Da Gumel Murnar Samun Nasarori A Ɓangarori Daban-daban

1 hour ago
NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano
Manyan Labarai

NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano

4 hours ago
Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci
Ra'ayi Riga

Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci

4 hours ago
DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu
Da ɗumi-ɗuminsa

DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu

6 hours ago
Jigilar Mai: Me Ya Haddasa Rikicin Dangote Da Ƙungiyar NUPENG?
Labarai

Jigilar Mai: Me Ya Haddasa Rikicin Dangote Da Ƙungiyar NUPENG?

9 hours ago
Next Post
Ƙarancin Wayewa da Samar Da Labaru Masu Kyau Ke Durƙusar Da Kannywood

Ƙarancin Wayewa da Samar Da Labaru Masu Kyau Ke Durƙusar Da Kannywood

LABARAI MASU NASABA

Sojoji

Sojoji Sun Harbe Wasu ‘Yan Ta’adda 2 A Taraba

September 16, 2025
Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

September 16, 2025
Buhari Ya Taya Amusan Murnar Lashe Zinari A Gasar Tsere Ta Duniya

Tinubu Ya Taya Amusan Da Gumel Murnar Samun Nasarori A Ɓangarori Daban-daban

September 16, 2025
Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire

Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire

September 16, 2025
NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano

NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano

September 16, 2025
Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci

Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci

September 16, 2025
DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu

DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu

September 16, 2025
Dan Sanda Ya Kashe Abokin Aikinsa Da Almakashi Har Lahira A Kebbi

Wata Ta Kashe ’Yar Uwarta Kan Bashin Naira 800 A Ondo

September 16, 2025
Jigilar Mai: Me Ya Haddasa Rikicin Dangote Da Ƙungiyar NUPENG?

Jigilar Mai: Me Ya Haddasa Rikicin Dangote Da Ƙungiyar NUPENG?

September 16, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

‘Yan Bindiga Sun Yi Wa Hakimi Yankan Rago A Zamfara

September 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.