ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dansandan Da Ya Ki Karbar Cin Hancin Miliyan 150 Ya Samu Shatara Ta Arziki

by Sulaiman and Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
cin hanci

Duk da hali na matsin rayuwa da wahalhalu da ake fama da su da gobe, bai hana wasu mutanen kirki aikata ayyukan kirki ba, kamar yadda aka samu wani jami’in dansanda da ya ki kabar cin hancin zunzurutun kudi har Naira miliyan 150, wanda kuma a dalilion haka ne ya samu kyautar fili a Babban Birnin Tarayya Abuja.

Dama masu iya magana na cewa a ko da yaushe na Allah ba sa karewa, kuma shi dai alheri danko ne ba ya faduwa kasa banza.

  • An Jinjinawa Matakan Kare Hakkin Bil Adama Na Kasar Sin Yayin Zaman Taron MDD
  • Kanana Hukumomin Kano Da Jigawa 23 Na Kan Gaba Wajen Fuskantar Ambaliyar Ruwa – NEMA

Rahotanni sun bayyana cewa, an karrama wannan Sufetan ‘yansanda mai suna (SP) Ibrahim Ezekiel Sini, ta hanyar bashi kyautar fili a Abuja. Wannan dansanda ya ki karbar cin hancin Naira miliyan 150 ne daga hannun wani dan kasuwa a Legas mai suna Akintoye Akindele, wanda kuma shi ne ya kafa ‘Platform Capital.

ADVERTISEMENT

Kwamishinan ‘Yansandan Babban Birnin Tarayya Abuja, CP Benneth Igweh, wanda ya ba da kyautar filin a madadin abokan aikin ‘yansandan, ya ce halin da SP Sini nuna ya sa rundunar ‘yansandan Nijeriya (NPF) alfahari.

Har ila yau, daya daga cikin wadanda suka shirya taron karramawar, Prince Chukwuemeka Okoye, Shugaban Kamfanin Begas Homes, ya ce halin da SP Sini ya nuna zama abin koyi kuma ya kamata ya zaburar da sauran jama’a da ‘yan Nijeriya su lura cewa rundunar ‘yansandan Nijeriya tana da mutane masu gaskiya da rikon amana.

LABARAI MASU NASABA

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

A cewar sa, “Wannan hali da SP Sini ya nuna ba wai kawai ya kara wa kansa da kuma rundunar ‘yansandan Nijeriya kwarin guiwa ba ne, har ma da karfafa gwiwar wasu da dama da su tsaya tsayin daka wajen yaki da cin hanci da rashawa da kuma bin ka’idojin da’a. Wannan dabi’a tasa za ta ci gaba da zama abar yabawa, gami da nuni da cewa duk tsanani ana samun mutanen kirki.

“Ba a yi wannan karramawa kawai don yaba kyawawan halayen Sufeto Ibrahim Sini ba, sai don a yi nuna ga al’umma su yaba wa daidaikun mutane masu nagarta da halin kirki.

“Muna so mu nuna cewa rundunar ‘yansandan NIjeriya tana da jami’ai da suka kware, kuma suna da kwarin gwiwa wajen gudanar da aikin dansanda mai ma’ana kuma su zama abin koyi.”

Yayin da yake yaba wa halin Sini, Okoye ya ce taron na daya daga cikin sauran hanyoyin nuna godiya da suke da shi don halayensa na yabawa.

An ce dan kasuwar a cikin tuhumar ya yi watsi da zargin da aka yi masa na ya fata ba da ajiye Naira miliyan 50 a matsayin cin hanci ga tawagar masu binciken IGP wanda ke karkashin jagorancin SP Sini.
Ya kara da cewa “Kin karbar Naira miliyan 150 ya nuna tsoron Allah, gudun duniya da kuma kwarewar aiki, duk wadannan halaye ne da jami’i Ibrahim ya nuna.”

Idan dai za a iya tunawa, Akindele, wanda wata babbar kotun tarayya da ke birnin tarayya ta tsare a gidan yari na Kuje, ana zarginsa da bai wa dansandan cin hancin Naira miliyan 150 domin ya janye binciken da yake yi akansa.

A cewar tuhume-tuhumen, an bayar da cin hancin ne ga ‘yansanda domin ba shi izinin tserewa kasar waje da kuma rubuta masa rahoto mai kyau bayan bincike.

An kama Akindele ne akan wata takardar korafi da Summit Oil International Limited ya mika wa shugaban ‘yansanda da ake zarginsa da damfarar kamfanin kudi Dala miliyan 5,636,397 da kuma wasu Naira miliyan 73,543,764.

A halin da ake ciki, SP Sini ya ce dalilin da ya sa ya ki amincewa da kudin cin hancin shi ne saboda ya gwammace ya samu natsuwa, ya ci gaba da yin gaskiya ga aiki da kare mutuncin rundunar ‘yansandan Nijeriya da kuma kiyaye mutuncinsa da na iyalansa.

cin hanci
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya
  • Sulaiman
    Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari
  • Sulaiman
    Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana
  • Sulaiman
    Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili
cin hanci
Rabi'u Ali Indabawa
+ posts Bio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    ’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    ’Yansanda Sun Cafke Mutun Biyu Da Ake Zargi Da Fashi Da Makami A Adamawa
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

MASU ALAKA

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF
Rahotonni

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin
Rahotonni

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026
Labarai

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
Next Post
Ƙarancin Wayewa da Samar Da Labaru Masu Kyau Ke Durƙusar Da Kannywood

Ƙarancin Wayewa da Samar Da Labaru Masu Kyau Ke Durƙusar Da Kannywood

LABARAI MASU NASABA

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026
Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.