ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dansandan Da Ya Ki Karbar Cin Hancin Miliyan 150 Ya Samu Shatara Ta Arziki

by Sulaiman and Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
cin hanci

Duk da hali na matsin rayuwa da wahalhalu da ake fama da su da gobe, bai hana wasu mutanen kirki aikata ayyukan kirki ba, kamar yadda aka samu wani jami’in dansanda da ya ki kabar cin hancin zunzurutun kudi har Naira miliyan 150, wanda kuma a dalilion haka ne ya samu kyautar fili a Babban Birnin Tarayya Abuja.

Dama masu iya magana na cewa a ko da yaushe na Allah ba sa karewa, kuma shi dai alheri danko ne ba ya faduwa kasa banza.

  • An Jinjinawa Matakan Kare Hakkin Bil Adama Na Kasar Sin Yayin Zaman Taron MDD
  • Kanana Hukumomin Kano Da Jigawa 23 Na Kan Gaba Wajen Fuskantar Ambaliyar Ruwa – NEMA

Rahotanni sun bayyana cewa, an karrama wannan Sufetan ‘yansanda mai suna (SP) Ibrahim Ezekiel Sini, ta hanyar bashi kyautar fili a Abuja. Wannan dansanda ya ki karbar cin hancin Naira miliyan 150 ne daga hannun wani dan kasuwa a Legas mai suna Akintoye Akindele, wanda kuma shi ne ya kafa ‘Platform Capital.

ADVERTISEMENT

Kwamishinan ‘Yansandan Babban Birnin Tarayya Abuja, CP Benneth Igweh, wanda ya ba da kyautar filin a madadin abokan aikin ‘yansandan, ya ce halin da SP Sini nuna ya sa rundunar ‘yansandan Nijeriya (NPF) alfahari.

Har ila yau, daya daga cikin wadanda suka shirya taron karramawar, Prince Chukwuemeka Okoye, Shugaban Kamfanin Begas Homes, ya ce halin da SP Sini ya nuna zama abin koyi kuma ya kamata ya zaburar da sauran jama’a da ‘yan Nijeriya su lura cewa rundunar ‘yansandan Nijeriya tana da mutane masu gaskiya da rikon amana.

LABARAI MASU NASABA

Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?

Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa ONSA Kan Shirin Horon Masu Tsaron Daji ‘Forest Guards’

A cewar sa, “Wannan hali da SP Sini ya nuna ba wai kawai ya kara wa kansa da kuma rundunar ‘yansandan Nijeriya kwarin guiwa ba ne, har ma da karfafa gwiwar wasu da dama da su tsaya tsayin daka wajen yaki da cin hanci da rashawa da kuma bin ka’idojin da’a. Wannan dabi’a tasa za ta ci gaba da zama abar yabawa, gami da nuni da cewa duk tsanani ana samun mutanen kirki.

“Ba a yi wannan karramawa kawai don yaba kyawawan halayen Sufeto Ibrahim Sini ba, sai don a yi nuna ga al’umma su yaba wa daidaikun mutane masu nagarta da halin kirki.

“Muna so mu nuna cewa rundunar ‘yansandan NIjeriya tana da jami’ai da suka kware, kuma suna da kwarin gwiwa wajen gudanar da aikin dansanda mai ma’ana kuma su zama abin koyi.”

Yayin da yake yaba wa halin Sini, Okoye ya ce taron na daya daga cikin sauran hanyoyin nuna godiya da suke da shi don halayensa na yabawa.

An ce dan kasuwar a cikin tuhumar ya yi watsi da zargin da aka yi masa na ya fata ba da ajiye Naira miliyan 50 a matsayin cin hanci ga tawagar masu binciken IGP wanda ke karkashin jagorancin SP Sini.
Ya kara da cewa “Kin karbar Naira miliyan 150 ya nuna tsoron Allah, gudun duniya da kuma kwarewar aiki, duk wadannan halaye ne da jami’i Ibrahim ya nuna.”

Idan dai za a iya tunawa, Akindele, wanda wata babbar kotun tarayya da ke birnin tarayya ta tsare a gidan yari na Kuje, ana zarginsa da bai wa dansandan cin hancin Naira miliyan 150 domin ya janye binciken da yake yi akansa.

A cewar tuhume-tuhumen, an bayar da cin hancin ne ga ‘yansanda domin ba shi izinin tserewa kasar waje da kuma rubuta masa rahoto mai kyau bayan bincike.

An kama Akindele ne akan wata takardar korafi da Summit Oil International Limited ya mika wa shugaban ‘yansanda da ake zarginsa da damfarar kamfanin kudi Dala miliyan 5,636,397 da kuma wasu Naira miliyan 73,543,764.

A halin da ake ciki, SP Sini ya ce dalilin da ya sa ya ki amincewa da kudin cin hancin shi ne saboda ya gwammace ya samu natsuwa, ya ci gaba da yin gaskiya ga aiki da kare mutuncin rundunar ‘yansandan Nijeriya da kuma kiyaye mutuncinsa da na iyalansa.

cin hanci
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?
  • Sulaiman
    Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Iran Da Su Aiwatar Da Cikakkiyar Takardar Bayanin Fahimtar Juna Da Aka Cimma
  • Sulaiman
    Sin Ta Yi Kira Da A Cike Gibin Cin Gajiyar Fasahar AI
  • Sulaiman
    Ministan Lafiya Na DRC Ya Gode Wa Sin Bisa Tura Kwararrun Likitoci Kasar Don Tallafa Wa Dakile Ebola
cin hanci
Rabi'u Ali Indabawa
+ posts Bio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Adadin Mutanen Da Tsananin Zafi Ya Kashe A Turai Ya Haura Dubu 1,300 —WHO
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Gwamnatin Tarayya Ta Bayyana Dalilanta Na Sake Fasalin Hukumar NYSC
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Sarkin Zazzau Ya Umarci A Soke Wasu Al’adu Da Ke Kawo Wa Aure Cikas

MASU ALAKA

Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?
Ra'ayi Riga

Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?

July 9, 2026
Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa ONSA Kan Shirin Horon Masu Tsaron Daji ‘Forest Guards’
Tsaro

Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa ONSA Kan Shirin Horon Masu Tsaron Daji ‘Forest Guards’

July 9, 2026
Auto Draft
Labarai

TCN Ta Kammala Gyaran Layin Wutar Lantarkin Zaria–Funtua 132kV

July 9, 2026
Next Post
Ƙarancin Wayewa da Samar Da Labaru Masu Kyau Ke Durƙusar Da Kannywood

Ƙarancin Wayewa da Samar Da Labaru Masu Kyau Ke Durƙusar Da Kannywood

LABARAI MASU NASABA

Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?

Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?

July 9, 2026
Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa ONSA Kan Shirin Horon Masu Tsaron Daji ‘Forest Guards’

Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa ONSA Kan Shirin Horon Masu Tsaron Daji ‘Forest Guards’

July 9, 2026
Auto Draft

TCN Ta Kammala Gyaran Layin Wutar Lantarkin Zaria–Funtua 132kV

July 9, 2026
Auto Draft

DSS Ta Kama ‘Yar Jarida Zainab Sodiq Kan Zargin Mallakar Drone Ba Tare da Cikakkun Takardu ba

July 9, 2026
Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa NSA Kan Shirin Samar Da Dakarun Tsaron Daji

Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa NSA Kan Shirin Samar Da Dakarun Tsaron Daji

July 9, 2026
Shaidar EFCC Ya Ce Sirika Bai Sanya Hannu A Takardun Kwangilar Naira Biliyan 2 Ba

Shaidar EFCC Ya Ce Sirika Bai Sanya Hannu A Takardun Kwangilar Naira Biliyan 2 Ba

July 9, 2026
’Yan Bindiga Sun Kashe Farfesa Har Lahira A  Jihar Benuwai

’Yan Bindiga Sun Kashe Farfesa Har Lahira A Jihar Benuwai

July 9, 2026
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Mutane A Kaduna Da Filato

Sojoji Sun Hallaka Shugaban ’Yan Bindiga, Sun Daƙile Hare-hare A Zamfara

July 9, 2026
Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Iran Da Su Aiwatar Da Cikakkiyar Takardar Bayanin Fahimtar Juna Da Aka Cimma

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Iran Da Su Aiwatar Da Cikakkiyar Takardar Bayanin Fahimtar Juna Da Aka Cimma

July 8, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Cike Gibin Cin Gajiyar Fasahar AI

Sin Ta Yi Kira Da A Cike Gibin Cin Gajiyar Fasahar AI

July 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.