• English
  • Business News
Friday, September 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Darussa Ga Nijeriya Daga Zaben Kasar Kenya

by Sulaiman
3 years ago
in Siyasa
0
kenya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Bayan makwanni ana zullumi a halin yanzu an kammala zaben game gari na kasar Kenya, inda William Ruto, mai shekara 55 a duniya, wanda kuma shi ne mataimakim shugaban kasar tun daga shekarar 2013 zuwa yanzu shi ne kuma shugaban jami’yya mai mulki ta ‘United Democratic Alliance’ ya samu nasarar lashe zaben kujerar shugaban kasar.

Ya samu nasara ne a kan Raila Odinga, mai shekara 77 a duniya wanda ya taba rike mukamin Firayministan kasar Kenya a tsakanin 2008–2013, shi ne kuma shugaban jamji’yyar ‘Orange Democratic Mobement’ a zaben da aka fafata matuka.

  • EFCC Ta Cafke Daraktan Hukumar Bunkasa Niger Delta Kan Zargin Badakalar Biliyan 25

Sauran wadanda suka tsaya takarar a zaben sun hada da Dabid Waihiga Mwaure, shugaban jam’iyyar ‘Agano Party’ da George Wajackoyah, na jam’iyyar ‘Roots Party of Kenya’.

Hukumar zaben Kenya ‘Independent Electoral and Boundaries Commission’ (IEBC) ta sanar da cewa, Ruto ya lashe zaben ne da kashi 50.5 na kuri’un da aka kada da suka kai Miliyan bakwai da digo daya (7.1 million) yayin da wanda yake biye da shi, Odinga, ya tashi da kashi 48.9 wato kuri’u Miliyan shida da digo tara (6.9 million).

Wani abin takaici duk kuwa ba wai ba a yi tsammanin faruwar haka ba ne, shi ne yadda zaben ya bar baya da kura, musamman yadda kakaddamar da ta tasho a tsakanin hukumar zaben da kuma irin tashin hankalin da ya biyo bayan zaben a wasu sassan kasar.

Labarai Masu Nasaba

Arewa Ba Zata Ƙarɓi Mulki A 2027 Ba, Gwamna  Bago

Tarihin Ƴan Majalisar Farko Kafin Da Kuma Zamanin Mulkin Mallaka (3)

Hudu daga cikin bakwai na manyan jami’an zaben kasar sun yi watsi da sakamakon zaben, wannan yana zuwa ne duk da yawan hukumomin da suka sa ido a kan yadda aka gudanmar da zaben ciki kuwa har da jami’an Majalisar Dinkin Duniya wadanda rahoton su ya nuna cewa an yi zaben cikin kwanciyar hankali.
Abubuwan lura tare da daukar darasi a zaben kasar ta Kenya suna da yawa a zaben da ya gudana ranar 9 ga watan Agusta.

Zaben wanda ya kasance na samar da shugaban kasa na 5 tunda kasar ta samu ‘yancin kai a shekarar 1963, sun kuma zabi gwamnoni, ‘yan majalisar kasa da za su jagoranci majalisa ta 47 a tsarin majalisar kasar.
Shugaba Uhuru Kenyatta bai kasance a cikin masu takara ba kamar yadda Shugaba Muhammadu Buhari ba zai shiga zaben Nijeriya na 2023 ba.

Yanayin yakin neman zaben bai kasance a kan abubuwan da suka shafi yi wa kasa aiki ba amma lamarin ya karkata ne tsakanin Odinga da Ruto inda suka mayar da hankali a matsayin kabila da asalin junansu, amma duk da haka an sanya muhawara a tsakanin ‘yan takarar.

Muhawarar ta samu cikas yayin da Odinga da kuma Wajackoyah suka janye daga shirin.
Odinga ya ce ba zai yi muhawara da Ruto ba, a bisa zargin cewa, ba shi da mutunci. Shi kuma Wajackoyah ya nemi a hada shi ne da ‘yan takarar shugabancin kasar su biyu a lokaci daya, bukatar da ta samu karbuwa a wajen masu shirya muhawarar.

Duk da haka rahotanni sun nuna cewa, an gudanar da zabubbukan cikin kwanciyar hankali a kasar duk cewa kuma an samu wuraren da aka dage zaben saboda matsalolin tsaro.
An kuma samu tsaikon kada kuri’a a wasu runfunar zaben saboda matsalar da aka fuskanta daga na’urar tantance masu kada kuri’a wanda ake kira ‘Kenya Integrated Elections Management Systems (KIEMS)’.

Hakan ta sanya hukumar IEBC ta bayar da izinin dakatar da amfani da na’urar a wasu runfunan zaben a yankunan Kakamega da Makueni yayin da ba a samu fara kada kuri’a a daidai karfe 6 na safen da aka ayyana ba saboda matsalar na’urar da aka samu.

Zuwa karfe 12 a ranar zaben, mutum 6,567,859 sun samu nasarar kada kuri’arsu wanda ke nuna kusan kashi 30 na wadanda suka yi rajistar kenan. Awa daya kuma kafin a rufe runfunan zaben na karfe 5 na yamma an samu mutum fiye da 12,065,803 da suka kada kuri’unsu, kashi 56.17 ke nan na wadanda suka yi rajistar zaben a kasar.
A ranar 10 ga watan Agusta 2022, hukumar zabe ta IEBC ta sanar da cewa, na’ura ta tabbatar da ‘yan Kenya Miliyan 14 suka kada kuri’arsu wanda hakan ke nuna kashi 64.6 kenan na wadanda suka yi rajistar zaben gaba daya.

Shugabar hukumar zaben IEBC, Wafula Chebukati, ta zargi wakilan jam’iyyu da yi wa tsarin tattara kuri’un zaben zagon kasa.

Kamar dai Nijeriya, Kenya na amfani da na’ura a matakai uku na zabe da suka hada da yin rajistar masu zabe da tantance masu kada kuri’a da kuma matakin aika da sakamakon zabe. Amma kuma ba kamar Nijeriya ba a Kenya ‘yan kasar da ke a kasashen waje na da ikon kada kuri’a a zabukkan da ake gudarnarwa suna kuma da ‘yan takara masu zaman kansu (Independent candidates).

Kwanaki uku bayan kammala zaben an samu nasarar tattara kashi 99.94 na sakamakin ta hanyar na’ura mai kwakwalwa sai dai kadan daga cikin wadanda basu shigo hannu ba suka rage da ba a tantance tare da sanar da su ba.

Duk da haka ne a ranar Litinin 15 ga watan Agusta hukumar zabe ta sanar da wanda ya lashe zaben.
Nan take Ruto ya amince da sakamakon tare da yin alakwarin jagorantar kowa da kowa a kasar a tare nuna banbanci ba, yayin da kuma Odinga ya yi watsi da sakamakoin zaben inda ya yi zargin an saba tanade-tanaden kundin tsarin mulki kuma sakamakon ya haramta, abin burgewa a nan shi ne ya nufi kotu ne don kalubalantar sakamakon zaben maimakon tayar da hankali al’umma.

A shekarar 2027 kasar ta fuskanci tarzomar zabe inda aka yi asarar rayukan mutum fiye da 1000 a wani rikicin kuma a shekatrar 2017 an yi asarar rayukar mutum 100, a kan haka mutane da dama ke fatan a samu nasara a zaben na wannan shekarar.

A mastayinmu na gidan jarida muna kira ga al’umma kasar Kenya su kai zuciya nesa, hakan na da muhimmanci ga dukkan masu ruwa da tsaki a kan su bi doka tare da ganin an gudanar da komai ba tare da an yi magudi ba.
Muna kira ga dukkan masu ruwa da tsaki a harkokin zaben Nijeriya su gudanar da abin da ya dara na kasar Kenya na tabbatar da an yi sahihin zabe a 2023.

Abin lura a nan kuma shi ne INEC na daga cikin hukumomin kasa da kasa da suka sa ido a yadda aka gudanar da zaben na Kenya. Tabbas an yaba mata a kan yadda ta gudanar da zaben jihohin Ekiti da na Osun to yakamata ta kara kaimi wajen inganta ayyyukanta a zaben 2023.

Muna kuma fatan ‘yan takarar shugabancin kasa za su yi koyi da takwarorinsu na Kenya ta hanyar tabbatar da su da magoya bayansu sun rungumi tafarkin zaman lafiya, kafin, yayin da lokacin da aka kammala zaben 2023.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Shugaban NIS Isah Jere Ya Sanar Da Ƙarin Girma Ga Jami’ai 4,526

Next Post

Yadda Zamfarawa Suka Karbi Tuban Kasurgumin Dan Bindiga Bello Turji

Related

Arewa Ba Zata Ƙarɓi Mulki A 2027 Ba, Gwamna  Bago
Siyasa

Arewa Ba Zata Ƙarɓi Mulki A 2027 Ba, Gwamna  Bago

4 days ago
Tarihin Ƴan Majalisar Farko Kafin Da Kuma Zamanin Mulkin Mallaka (3)
Siyasa

Tarihin Ƴan Majalisar Farko Kafin Da Kuma Zamanin Mulkin Mallaka (3)

5 days ago
APC Na Ƙoƙarin Tarwatsa Mu Ne Saboda Kar Mu Ƙwaci Mulki A 2027 – ADC
Siyasa

APC Na Ƙoƙarin Tarwatsa Mu Ne Saboda Kar Mu Ƙwaci Mulki A 2027 – ADC

6 days ago
PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya
Siyasa

PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya

6 days ago
INEC Ta Amince Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC
Manyan Labarai

INEC Ta Amince Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

1 week ago
APC Ce Ke Kai Mana Hari Saboda Siyasa – Malami
Manyan Labarai

APC Ce Ke Kai Mana Hari Saboda Siyasa – Malami

1 week ago
Next Post
turji

Yadda Zamfarawa Suka Karbi Tuban Kasurgumin Dan Bindiga Bello Turji

LABARAI MASU NASABA

Firaministan Sin Zai Halarci Babban Taron Mahawara Na MDD Karo Na 80

Firaministan Sin Zai Halarci Babban Taron Mahawara Na MDD Karo Na 80

September 19, 2025
Shugaba Xi ya zanta ta wayar tarho da takwaransa na Amurka

Shugaba Xi ya zanta ta wayar tarho da takwaransa na Amurka

September 19, 2025
Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

September 19, 2025
Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

September 19, 2025
Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Bunkasa Ci Gaban Mata

Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Bunkasa Ci Gaban Mata

September 19, 2025
Ofishin Yada Labarai Na Majalisar Gudanarwar Kasar Sin Ya Fitar Da Takardar Bayani Mai Taken “Nasarar Aiwatar Da Manufar JKS A Xinjiang A Sabon Zamani”

Ofishin Yada Labarai Na Majalisar Gudanarwar Kasar Sin Ya Fitar Da Takardar Bayani Mai Taken “Nasarar Aiwatar Da Manufar JKS A Xinjiang A Sabon Zamani”

September 19, 2025
kenya

Tarihin Ahmadu Bello Sardaunan Sakkwato Firimiyan Arewa

September 19, 2025
Xi Jinping Ya Aika Wasikar Taya Murnar Cika Shekaru 100 Da Kafuwar Jam’iyyar Zhigong Ta Sin

Xi Jinping Ya Aika Wasikar Taya Murnar Cika Shekaru 100 Da Kafuwar Jam’iyyar Zhigong Ta Sin

September 19, 2025
An Dakatar Da Shugabannin Makarantun Sakandire 6 A Sakkwato Kan Rashin Bin Dokokin Aiki

An Dakatar Da Shugabannin Makarantun Sakandire 6 A Sakkwato Kan Rashin Bin Dokokin Aiki

September 19, 2025
Wata Mata Ta Ƙona Al’aurar Ƙaramar Yarinya A Bauchi

Wata Mata Ta Ƙona Al’aurar Ƙaramar Yarinya A Bauchi

September 19, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.