Kungiyar kwallon kafa ta Liverpool ta ki amincewa da tayin da Barcelona ta yi na yin magana da dan wasan gaba Luis Diaz, majiyoyin kulob din sun shaida wa BBC cewa dan wasan kasar Colombian, Diaz kuma daya daga cikin manyan ‘yan wasan Liverpool da suka lashe kofin Firimiya a bana, ba na sayarwa ba ne.
Dan wasan mai shekaru 28 ya koma Liverpool ne daga Porto a watan Janairun 2022 kuma yana da kwantiragi da kungiyar har zuwa shekarar 2027, ya zura kwallaye 13 sannan ya taimaka aka zura kwallaye bakwai a gasar yayin da Liverpool ta lashe kofin da maki 10 tsakaninta da Arsenal, Diaz ya ja hankalin Manchester City a bazarar da ta gabata kuma yana da masoya a Saudi Arabiya.
- Sojoji Sun Daƙile Harin Ƴan Ta’adda, Sun Kashe Wasu Da Yawa A Borno
- Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutum 2 Sun Sace 2 A Wurin Haƙar Ma’adanai
Daraktan wasanni na Liverpool Richard Hughes da shugaban kungiyar Fenway Sports Group Michael Edwards zasuyi kokarin sabunta kwantiragin ‘yan wasan da Arne Slot ke jagoranta a farkon kasuwar musayar ‘yan wasa, a makon da ya gabata zakarun gasar Firimiyar suka kammala cinikin dan wasan baya na kasar Holland Jeremie Frimpong daga Bayer Leverkusen akan kudi £29.5m.
A watan Afrilu, fitaccen dan wasan gaba Mohamed Salah ya kawo karshen cece-kuce game da makomarsa ta hanyar sanya hannu kan sabon kwantiragin shekaru biyu don ci gaba da zama a Anfield har zuwa shekarar 2027, yayin da kyaftin din Virgil van Dijk ya kulla sabuwar yarjejeniya a wannan watan.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp