• English
  • Business News
Monday, September 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dole Arewa Ta Yi Magana Da Murya Ɗaya Kan Tsaro Da Tattalin Arziki, In ji Gwamnan Zamfara

by Sulaiman
2 hours ago
in Labarai
0
Dole Arewa Ta Yi Magana Da Murya Ɗaya Kan Tsaro Da Tattalin Arziki, In ji Gwamnan Zamfara
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal ya buƙaci jihohin Arewa 19 da su tsaya da ƙafarsu su jajirce su yi magana da murya ɗaya kan harkokin tsaro da tattalin arziki.

 

Gwamnan ya jagoranci taron ranar farko ta bangaren Zuba Jari da Bunƙasa Masana’antu ta Arewacin Nijeriya a ranar Litinin a otel ɗin Abuja Continental.

  • Ƙungiyar ASUU Ta Bai Wa Gwamnatin Tarayya Wa’adin Kwanaki 14 Ta Biya Buƙatunta 
  • FCT Ta Amince Da Naira Miliyan 8.2 Kan Kujerar Aikin Hajjin 2026

Wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar ta bayyana cewa Ƙungiyar Dattawan Arewa ƙarƙashin jagorancin Farfesa Ango Abdullahi ce ta shirya taron zuba jarin.

 

Labarai Masu Nasaba

Kotu Ta Dakatar Da PENGASSAN, NNPCL Kan Katse Wa Matatar Ɗangote Ɗanyen Mai Da Iskar Gas

FCT Ta Amince Da Naira Miliyan 8.2 Kan Kujerar Aikin Hajjin 2026

Sanarwar ta ƙara da cewa, taken taron shi ne “Buɗe Dabarun Damarmaki”, kuma ya tattaro duk masu ruwa da tsaki a sassan Arewacin Nijeriya.

 

A nasa jawabin, Gwamna Lawal ya yaba wa Ƙungiyar Dattawan Arewa bisa jajircewar da take yi wajen ci gaban yankin Arewa.

 

“Ta hanyar kiran wannan taro a ƙarƙashin taken ‘Buɗe Dabarun Damarmaki,’ kun sake nuna kyakkyawar manufar ku kan makomarmu baki ɗaya.

 

“Bangarori kamar – Ma’adinai, Noma, da Makamashi — ba bisa haɗari aka same su ba, ginshiƙai ne waɗanda dole ne a gina su don ci gaban Arewacin Nijeriya. A Zamfara muna sane da halin da muke ciki: ƙasa mai albarkar ma’adanai masu tarin yawa da ƙasar noma, amma duk da haka mutanenmu ba su ci cikakken ribar waɗannan abubuwan ba.

 

“Muhimmin tambaya a gare mu a matsayinmu na shugabanni ba shi ne yin abin da ya kamata ba, amma ta yaya za mu iya juya akalar abin da ake muke da shi zuwa ci gaban al’umma. Don jawo jarin da ake buƙata da kuma samar da masana’antu a yankinmu don amfanin al’umma, dole ne mu tsaya haiƙan, mu rungumi sabuwar hanyar haɗin gwiwa.”

 

Gwamna Lawal ya ci gaba da jaddada cewa, Arewa mai zaman lafiya, Arewa ce mai ƙarfin tattalin arziki, yanki ne da ya kamata shugabannin jihohinta 19 su zurfafa haɗin gwiwa fiye da siyasa.

 

“Dole ne mu haɗa ƙarfi da ƙarfe wajen kare mutane da saka hannun jari. Tsaro shi ne babban abin da ake buƙata na duk wani ci gaba mai ma’ana. Masu zuba jari, na cikin gida da na lasa da ƙasa, ba masu hannu da shuni ba ne; su masu gaskiya ne. Ba za su saka jari a inda babu tsaro ba. Dole ne mu haɗa ƙarfin tsaron mu, mu raba hankali a cikin haƙiƙanin lokaci, da kuma samar da manyan jami’an tsaro na al’umma don samar da ingantaccen tsaro.

 

“A Zamfara, ƙoƙarinmu a fili yake, mun ƙaura daga halin da ake ciki a da na rashin gaskiya da rashin bin doka da oda a fannin ma’adinai zuwa yanayin na gaskiya da amana. Mun farfaɗo da harkar noma ta hanyar inganta noman zamani, sarrafa kayan noma, da samun rance. Kuma muna samar da yanayi mai tsaro da kwanciyar hankali wanda shi ne ƙashin bayan komai.

 

“Kirana a yau shi ne Yarjejeniyar Tattalin Arziki na Arewacin Nijeriya — alaƙar mai ƙarfi tsakanin jihohi 19 da su yi magana da murya ɗaya kan harkokin tsaro da tattalin arziki. Samar da hanya guda ɗaya ga manyan masu zuba jari da ke neman yin kasuwanci a faɗin yankin. A hafa hannu a muhimman ababen more rayuwa kamar wutar lantarki da jirgin ƙasa, igiya mai ƙarfi da zara haɗe jihohin mu.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

CMG Ya Kaddamar Da Shirye-Shiryen Hadin Gwiwa Da Gwamnatin Yankin Hong Kong

Next Post

Sin Ta Cimma Nasarar Gina Tsarin Ban Ruwa Mafi Girma A Duniya

Related

Majalisa Ta Daƙile PENGASSAN Akan Shirin Daina Kai Wa Matatar Ɗangote Gas Da Ɗanyen Mai
Labarai

Kotu Ta Dakatar Da PENGASSAN, NNPCL Kan Katse Wa Matatar Ɗangote Ɗanyen Mai Da Iskar Gas

2 hours ago
Aikin Hajji: Za A Fara Jigilar Alhazan Jihar Kwara A Ranar 12 Ga Watan Mayu
Labarai

FCT Ta Amince Da Naira Miliyan 8.2 Kan Kujerar Aikin Hajjin 2026

3 hours ago
ASUU
Labarai

Ƙungiyar ASUU Ta Bai Wa Gwamnatin Tarayya Wa’adin Kwanaki 14 Ta Biya Buƙatunta 

5 hours ago
NAF Ta Kashe ‘Yan Bindiga Da Dama A Zamfara
Manyan Labarai

NAF Ta Fatattaki ‘Yan Ta’addan Da Suka Addabi Al’ummar Jihar Kwara

7 hours ago
Alfanun Harshen Mandarin A Kasashen Afirka
Ra'ayi Riga

Alfanun Harshen Mandarin A Kasashen Afirka

7 hours ago
Zulum Ya Rabawa Talakawan Dikwa  Tallafin Kuɗi Da Abinci
Labarai

Zulum Ya Rabawa Talakawan Dikwa  Tallafin Kuɗi Da Abinci

8 hours ago
Next Post
Sin Ta Cimma Nasarar Gina Tsarin Ban Ruwa Mafi Girma A Duniya

Sin Ta Cimma Nasarar Gina Tsarin Ban Ruwa Mafi Girma A Duniya

LABARAI MASU NASABA

Kofin Duniya: FIFA Ta Zabtarewa Afirka Ta Kudu Maki Uku

Kofin Duniya: FIFA Ta Zabtarewa Afirka Ta Kudu Maki Uku

September 29, 2025
Sin Ta Cimma Nasarar Gina Tsarin Ban Ruwa Mafi Girma A Duniya

Sin Ta Cimma Nasarar Gina Tsarin Ban Ruwa Mafi Girma A Duniya

September 29, 2025
Dole Arewa Ta Yi Magana Da Murya Ɗaya Kan Tsaro Da Tattalin Arziki, In ji Gwamnan Zamfara

Dole Arewa Ta Yi Magana Da Murya Ɗaya Kan Tsaro Da Tattalin Arziki, In ji Gwamnan Zamfara

September 29, 2025
CMG Ya Kaddamar Da Shirye-Shiryen Hadin Gwiwa Da Gwamnatin Yankin Hong Kong

CMG Ya Kaddamar Da Shirye-Shiryen Hadin Gwiwa Da Gwamnatin Yankin Hong Kong

September 29, 2025
Majalisa Ta Daƙile PENGASSAN Akan Shirin Daina Kai Wa Matatar Ɗangote Gas Da Ɗanyen Mai

Kotu Ta Dakatar Da PENGASSAN, NNPCL Kan Katse Wa Matatar Ɗangote Ɗanyen Mai Da Iskar Gas

September 29, 2025
Sin Da AU Sun Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Fahimtar Juna A Fannin Hadin Gwiwar Raya Kimiyya Da Fasaha

Sin Da AU Sun Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Fahimtar Juna A Fannin Hadin Gwiwar Raya Kimiyya Da Fasaha

September 29, 2025
Aikin Hajji: Za A Fara Jigilar Alhazan Jihar Kwara A Ranar 12 Ga Watan Mayu

FCT Ta Amince Da Naira Miliyan 8.2 Kan Kujerar Aikin Hajjin 2026

September 29, 2025
Masana’antar Raya Al’adu Ta Sin Ta Samu Ci Gaba Bisa Daidaito Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar Karo Na 14

Masana’antar Raya Al’adu Ta Sin Ta Samu Ci Gaba Bisa Daidaito Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar Karo Na 14

September 29, 2025
ASUU

Ƙungiyar ASUU Ta Bai Wa Gwamnatin Tarayya Wa’adin Kwanaki 14 Ta Biya Buƙatunta 

September 29, 2025
Xi: Ya Kamata A Sa Kaimi Ga Dunkulewar Addinan Sin Da Kyawawan Al’adun Gargajiya Na Kasar

Xi: Ya Kamata A Sa Kaimi Ga Dunkulewar Addinan Sin Da Kyawawan Al’adun Gargajiya Na Kasar

September 29, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.