ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, November 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dole Arewa Ta Yi Magana Da Murya Ɗaya Kan Tsaro Da Tattalin Arziki, In ji Gwamnan Zamfara

by Sulaiman
1 month ago
Zamfara

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal ya buƙaci jihohin Arewa 19 da su tsaya da ƙafarsu su jajirce su yi magana da murya ɗaya kan harkokin tsaro da tattalin arziki.

 

Gwamnan ya jagoranci taron ranar farko ta bangaren Zuba Jari da Bunƙasa Masana’antu ta Arewacin Nijeriya a ranar Litinin a otel ɗin Abuja Continental.

ADVERTISEMENT
  • Ƙungiyar ASUU Ta Bai Wa Gwamnatin Tarayya Wa’adin Kwanaki 14 Ta Biya Buƙatunta 
  • FCT Ta Amince Da Naira Miliyan 8.2 Kan Kujerar Aikin Hajjin 2026

Wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar ta bayyana cewa Ƙungiyar Dattawan Arewa ƙarƙashin jagorancin Farfesa Ango Abdullahi ce ta shirya taron zuba jarin.

 

LABARAI MASU NASABA

Babu Wani Abu Kuskure Ga Sojan Da Ya Yi Sa-in-sa Da Ministan FCT – Matawalle

Majalisar Tarayya Za Ta Binciki Masaƙa Ta Kaduna Da Sauran Gine-ginen Gwamnati 11,000 Da Aka Yi Watsi Da Su

Sanarwar ta ƙara da cewa, taken taron shi ne “Buɗe Dabarun Damarmaki”, kuma ya tattaro duk masu ruwa da tsaki a sassan Arewacin Nijeriya.

 

A nasa jawabin, Gwamna Lawal ya yaba wa Ƙungiyar Dattawan Arewa bisa jajircewar da take yi wajen ci gaban yankin Arewa.

 

“Ta hanyar kiran wannan taro a ƙarƙashin taken ‘Buɗe Dabarun Damarmaki,’ kun sake nuna kyakkyawar manufar ku kan makomarmu baki ɗaya.

 

“Bangarori kamar – Ma’adinai, Noma, da Makamashi — ba bisa haɗari aka same su ba, ginshiƙai ne waɗanda dole ne a gina su don ci gaban Arewacin Nijeriya. A Zamfara muna sane da halin da muke ciki: ƙasa mai albarkar ma’adanai masu tarin yawa da ƙasar noma, amma duk da haka mutanenmu ba su ci cikakken ribar waɗannan abubuwan ba.

 

“Muhimmin tambaya a gare mu a matsayinmu na shugabanni ba shi ne yin abin da ya kamata ba, amma ta yaya za mu iya juya akalar abin da ake muke da shi zuwa ci gaban al’umma. Don jawo jarin da ake buƙata da kuma samar da masana’antu a yankinmu don amfanin al’umma, dole ne mu tsaya haiƙan, mu rungumi sabuwar hanyar haɗin gwiwa.”

 

Gwamna Lawal ya ci gaba da jaddada cewa, Arewa mai zaman lafiya, Arewa ce mai ƙarfin tattalin arziki, yanki ne da ya kamata shugabannin jihohinta 19 su zurfafa haɗin gwiwa fiye da siyasa.

 

“Dole ne mu haɗa ƙarfi da ƙarfe wajen kare mutane da saka hannun jari. Tsaro shi ne babban abin da ake buƙata na duk wani ci gaba mai ma’ana. Masu zuba jari, na cikin gida da na lasa da ƙasa, ba masu hannu da shuni ba ne; su masu gaskiya ne. Ba za su saka jari a inda babu tsaro ba. Dole ne mu haɗa ƙarfin tsaron mu, mu raba hankali a cikin haƙiƙanin lokaci, da kuma samar da manyan jami’an tsaro na al’umma don samar da ingantaccen tsaro.

 

“A Zamfara, ƙoƙarinmu a fili yake, mun ƙaura daga halin da ake ciki a da na rashin gaskiya da rashin bin doka da oda a fannin ma’adinai zuwa yanayin na gaskiya da amana. Mun farfaɗo da harkar noma ta hanyar inganta noman zamani, sarrafa kayan noma, da samun rance. Kuma muna samar da yanayi mai tsaro da kwanciyar hankali wanda shi ne ƙashin bayan komai.

 

“Kirana a yau shi ne Yarjejeniyar Tattalin Arziki na Arewacin Nijeriya — alaƙar mai ƙarfi tsakanin jihohi 19 da su yi magana da murya ɗaya kan harkokin tsaro da tattalin arziki. Samar da hanya guda ɗaya ga manyan masu zuba jari da ke neman yin kasuwanci a faɗin yankin. A hafa hannu a muhimman ababen more rayuwa kamar wutar lantarki da jirgin ƙasa, igiya mai ƙarfi da zara haɗe jihohin mu.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Babu Wani Abu Kuskure Ga Sojan Da Ya Yi Sa-in-sa Da Ministan FCT – Matawalle
Labarai

Babu Wani Abu Kuskure Ga Sojan Da Ya Yi Sa-in-sa Da Ministan FCT – Matawalle

November 13, 2025
Majalisar Tarayya Za Ta Binciki Masaƙa Ta Kaduna Da Sauran Gine-ginen Gwamnati 11,000 Da Aka Yi Watsi Da Su
Manyan Labarai

Majalisar Tarayya Za Ta Binciki Masaƙa Ta Kaduna Da Sauran Gine-ginen Gwamnati 11,000 Da Aka Yi Watsi Da Su

November 13, 2025
Lambar Yabo Da LEADERSHIP Ta Ba Mu, Ta Ƙara Zaburar Da Mu – Gwamna Sule
Manyan Labarai

Lambar Yabo Da LEADERSHIP Ta Ba Mu, Ta Ƙara Zaburar Da Mu – Gwamna Sule

November 13, 2025
Next Post
Sin Ta Cimma Nasarar Gina Tsarin Ban Ruwa Mafi Girma A Duniya

Sin Ta Cimma Nasarar Gina Tsarin Ban Ruwa Mafi Girma A Duniya

LABARAI MASU NASABA

Babu Wani Abu Kuskure Ga Sojan Da Ya Yi Sa-in-sa Da Ministan FCT – Matawalle

Babu Wani Abu Kuskure Ga Sojan Da Ya Yi Sa-in-sa Da Ministan FCT – Matawalle

November 13, 2025
Majalisar Tarayya Za Ta Binciki Masaƙa Ta Kaduna Da Sauran Gine-ginen Gwamnati 11,000 Da Aka Yi Watsi Da Su

Majalisar Tarayya Za Ta Binciki Masaƙa Ta Kaduna Da Sauran Gine-ginen Gwamnati 11,000 Da Aka Yi Watsi Da Su

November 13, 2025
Lambar Yabo Da LEADERSHIP Ta Ba Mu, Ta Ƙara Zaburar Da Mu – Gwamna Sule

Lambar Yabo Da LEADERSHIP Ta Ba Mu, Ta Ƙara Zaburar Da Mu – Gwamna Sule

November 13, 2025
Zaɓen 2027: Jam’iyyar ADC ta Ƙaddamar Da Kwamitin Sake Fasalinta A Kaduna

Zaɓen 2027: Jam’iyyar ADC ta Ƙaddamar Da Kwamitin Sake Fasalinta A Kaduna

November 12, 2025
Sin Ta Bukaci Japan Ta Daina Yi Wa Masu Fafutukar “‘Yancin Kan Taiwan” Ingiza Mai Kantu Ruwa

Sin Ta Bukaci Japan Ta Daina Yi Wa Masu Fafutukar “‘Yancin Kan Taiwan” Ingiza Mai Kantu Ruwa

November 12, 2025
Gwamnati Ta Janye Buƙatar Amfani Da Harshen Gida Wurin Koyarwa A Makarantu 

Gwamnati Ta Janye Buƙatar Amfani Da Harshen Gida Wurin Koyarwa A Makarantu 

November 12, 2025
Peng Liyuan Da Sarauniya Letizia Ta Spain Sun Ziyarci Cibiyar Kula Da Nakasassu A Beijing

Peng Liyuan Da Sarauniya Letizia Ta Spain Sun Ziyarci Cibiyar Kula Da Nakasassu A Beijing

November 12, 2025
Madalla Da Sabon Binciken Jami’ar Nankai Ta Kasar Sin Kan Mata Marasa Haihuwa

Madalla Da Sabon Binciken Jami’ar Nankai Ta Kasar Sin Kan Mata Marasa Haihuwa

November 12, 2025
'yansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutane 4 Kan Zargin Fashi Da Makami A Bauchi

November 12, 2025
Ana Ci Gaba Da Raya Kasar Sin Daga Matakin Kasa Mai Sauri Zuwa Kasa Mai Inganci

Ana Ci Gaba Da Raya Kasar Sin Daga Matakin Kasa Mai Sauri Zuwa Kasa Mai Inganci

November 12, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.