• English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dole Ne A Tauna Tsakuwa Don Aya Ta Ji Tsoro

byCGTN Hausa and Sulaiman
12 months ago
Tsakuwa

Rundunar ‘yantar da jama’ar kasar Sin (PLA) ta yankin gabashin kasar ta shirya sojojinta na kasa, da na ruwa, da na sama da na harba makamai masu linzami, domin gudanar da atisaye mai taken “Joint Sword-2024B” a mashigin tekun Taiwan da arewa, da kudu da gabashin yankin tsibirin Taiwan.

 

Da farko dai, Taiwan wani yanki ne na kasar Sin da babban yankin ya sha nanata cewa ba zai iya ballewa ba, kuma dukkan wasu batutuwa da suka shafi tsibirin, batu ne na cikin gidan Sin. Amma wasu aikace aikace da bangarori masu adawa da dunkulewar baki dayan Sin wuri guda suke yi, wani yunkuri ne na takalar kasar Sin da keta cikakken ikon da take da shi kan yankunanta.

  • Ko Za A Kore Ni Daga APC Ba Zan Daina Fadar Gaskiya Ba – Ndume
  • Zaɓen Ƙananan Hukumomi: Mataimakiyar Gwamna Ta Yi Kira A Guji Tarzoma A Rungumi Zaman Lafiya

Babu wata kasa a duniya da za ta amince da irin takalar da ake yi wa kasar Sin don gane da batun Taiwan, don haka, matakan da Sin ke dauka sun zama wajibi domin bangarori masu ruwa da tsaki su farga, kuma su gane cewa Sin ba za ta nade hannu tana kallo ana keta cikakken ikon da ‘yanci da muradunta ba.

 

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Abin takaici ne yadda wasu ke nanata girmama manufar Sin daya tak, amma kuma suke nuna fuska biyu ta hanyar goyon bayan ‘yan awaren Taiwan, wanda kuma abu ne da Sin ba za ta lamunta ba.

 

‘Yancin Taiwan na nufin tashin hankali a Taiwan. Ya kamata mahukuntan yankin Taiwan da suke ganin suna samun goyon bayan wata babbar kasa, su nutsu, su yi nazarin yankuna irin nasu da aka yi ta ingizawa su nemi ‘yanci, shin yanzu a wani hali ko yanayi suke ciki? Duk wanda ke kaunar ci gaba da zaman lafiya da kwanciyar hankalin yankin, to ba zai goyi bayan ‘yancin Taiwan ba, sai dai idan yana da wata manufa da ta sabawa hakan.

 

Don haka, tilas ne Sin ta rika tauna tsakuwa don aya ta ji tsoro, kuma ‘yan awaren da masu ingizasu su san cewa, ba za ta yi kasa a gwiwa wajen daukan dukkan matakai domin kare cikakken ‘yanci da muradunta da burinta ba, wato ganin dunkulewar kasar wuri guda.(Fa’iza Mustapha)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci
Daga Birnin Sin

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?
Daga Birnin Sin

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
Next Post
An Yi Musayar Yawu Tsakanin Macron Da Netanyahu Kan Rikicin Gabas ta Tsakiya

An Yi Musayar Yawu Tsakanin Macron Da Netanyahu Kan Rikicin Gabas ta Tsakiya

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025
Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

October 7, 2025
Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

October 7, 2025
Tinubu

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Kan Karɓo Bashin Dala Biliyan $2.347 Da $500m Na Sukuk 

October 7, 2025
Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

October 7, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo

Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version