• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Don Kare Hakkin Dan Adam Ana Bukatar Gudunmowa Maimakon Takunkumi

by CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Don Kare Hakkin Dan Adam Ana Bukatar Gudunmowa Maimakon Takunkumi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yau ranar hakkin dan Adam ce. Shekaru 75 da suka gabata ne, aka zartas da sanarwar kare hakkin dan Adam a duniya yayin babban taron MDD, lamarin da ya haifar da babban tasiri kan kokarin al’ummar duniya na kare da raya hakkin dan Adam. Sai dai, abin takaici shi ne, yadda a wannan zamanin da muke ciki, a kan fake da batun “hakkin dan Adam” don biyan bukatu na siyasa.

Misali, kwanaki 2 da suka wuce, ma’aikatar kudi ta kasar Amurka ta sanar da kakaba takunkumi kan wasu daidaikun mutane na kasashe 9, ciki har da Afirka ta tsakiya, da Kongo Kinshasa, da Sudan ta Kudu, bisa dalilin “keta hakkin dan Adam”. Kana a rana daya, kasar Amurka ita kadai ta kada kuri’ar kin amincewa a taron tattauna rikicin Isra’ila da Falasdinu na kwamitin sulhun MDD, inda ta sake hana ruwa gudu ga yunkurin kasashen duniya na neman tsagaita bude wuta a zirin Gaza. Wato kasar Amurka ta kakaba takunkumi na kashin kai kan wasu kasashe, da sunan “keta hakkin dan Adam”, yayin da a daya bangaren take goyon bayan kisan da ake yi wa fararen hular Falasdinu. Sannan kuma wai tana “taya al’ummar mutanen duniya murnar ranar kare hakkin dan Adam.

  • COP28: Sin Da Afirka Za Su Bunkasa Hadin Gwiwa A Fannin Raya Kananan Ayyukan Samar Da Makamashi Mai Tsafta
  • Sin: Ya Kamata Kwamitin Sulhu Ya Kara Daukar Matakai Kan Lokaci Don Inganta Tsagaita Bude Wuta Da Kawo Karshen Yaki A Dukkan Fannoni

Sai dai, kowa na da ‘yancin tabbatar da ra’ayinsa dangane da hakkin dan Adam. Lokacin da kasar Amurka da wasu kawayenta ke neman yin amfani da batun hakkin dan-Adam wajen dora wa wani laifi, da yanke hukunci, da sarrafa wasu kasasahe, da hana su samun ci gaba, za mu iya nuna akasin haka. Wato mu yi kokarin mai da hakkin dan Adam yadda ya kamata ya kasance, wanda ya kasance wani karfi dake haifar da ci gaba ga al’ummar dan Adam. A wannan fanni, wani rahoton da wasu kungiyoyin masana na kasar Sin suka fitar a kwanan baya, dangane da batun kare hakkin dan Adam, ya nuna wasu misalai.

Cikin rahoton an ayyana ci gaban zaman rayuwar jama’ar kasashen Afirka da aka samu ta hanyar hadin gwiwa tsakanin kasashen Afirka da kasar Sin a kokarin aiwatar da shawarar “Ziri Daya da Hanya Daya” da kasar Sin ta gabatar. Misali, a lardin Bubanza na kasar Burundi, wani manomi mai suna Charles Ngendakumana, ya taba fama da talauci da yunwa. Sai dai daga bisani ya fara noman irin shinkafar zamani da aka tagwaita mai samar da yawan iri ko Hybrid, bisa taimakon da wani masanin ilimin aikin gona na kasar Sin ya samar. Bayan wasu shekaru 4, kudin shigar da ya samu ya ninka. Zuwa yanzu yana da yara 7, har ma ya gina wani sabon gida, gami da bude wani wurin sarrafa shinkafa. Wannan abu bai shafi kare hakkin dan Adam ba? Tabbas ya shafa. Wannan shi ne kare hakkin mutum na rayuwa.

Wani misali na daban da rahoton ya kunsa ya shafi tallafin da gwamnatin kasar Sin ta bayar da zummar taimakawa kauyuka dubu 10 dake nahiyar Afirka kama shirye-shiryen telabijin ta hanyar tauraron dan Adam. Zuwa karshen shekarar 2022, aikin ya amfani mutane kusan miliyan 10, na magidanta fiye da dubu 190, dake kauyuka 9512 na wasu kasashe 21 dake nahiyar Afirka. Wannan aiki ma ya shafi yunkurin kare hakkin dan Adam, inda ya samar da gudunmowa a fannin kare hakkin mutane na neman raya kansu.

Labarai Masu Nasaba

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Cikin rahoton an yi amfani da dimbin misalai irin wadannan, wajen bayyana wani daidaitaccen ra’ayi game da hakkin dan Adam, wato hakkin dan Adam na tushe shi ne neman rayuwa, daga baya za a nemi raya kai. Don haka ya kamata kasashe daban daban su yi kokarin hadin gwiwa don inganta harkokin tattalin arziki da na zaman al’umma, daga baya za a iya tabbatar da ci gaban harkokin hakkin dan Adam. Maimakon a yi ta sanya ido kan maganar “keta hakkin dan Adam” da saka takunkumi kan sauran kasashe, zai fi kyau a samar da hakikanin gudunmowa ga yunkurin kare hakkin mutane na rayuwa da raya kansu. A wannan zamanin da ake fuskantar dimbin kalubaloli a fannonin tsaro, da tattalin arziki, da muhalli, da dai sauransu, duniyarmu tana bukatar samun karin gudunmowa ta fuskar kare hakkin dan Adam maimakon takunkumi da yanke hukunci na kashin kai da a karshe ka iya shafar rayuwar bil-Adama.. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Hakkin Dan AdamMDDSinawa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Hangzhou: An Gudanar Da Taron Dandalin Tattaunawar Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Larabawa Kan Shirye-shiryen Rediyo Da Telebijin Karo Na 6

Next Post

Yadda Ake Hada Miyar Hanta

Related

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

3 hours ago
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata
Daga Birnin Sin

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

4 hours ago
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

6 hours ago
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya
Daga Birnin Sin

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

7 hours ago
Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar
Daga Birnin Sin

Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

14 hours ago
Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin

16 hours ago
Next Post
Yadda Ake Hada Miyar Hanta

Yadda Ake Hada Miyar Hanta

LABARAI MASU NASABA

UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

May 14, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.