ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Don Kare Hakkin Dan Adam Ana Bukatar Gudunmowa Maimakon Takunkumi

by CGTN Hausa
2 years ago
Dan Adam

Yau ranar hakkin dan Adam ce. Shekaru 75 da suka gabata ne, aka zartas da sanarwar kare hakkin dan Adam a duniya yayin babban taron MDD, lamarin da ya haifar da babban tasiri kan kokarin al’ummar duniya na kare da raya hakkin dan Adam. Sai dai, abin takaici shi ne, yadda a wannan zamanin da muke ciki, a kan fake da batun “hakkin dan Adam” don biyan bukatu na siyasa.

Misali, kwanaki 2 da suka wuce, ma’aikatar kudi ta kasar Amurka ta sanar da kakaba takunkumi kan wasu daidaikun mutane na kasashe 9, ciki har da Afirka ta tsakiya, da Kongo Kinshasa, da Sudan ta Kudu, bisa dalilin “keta hakkin dan Adam”. Kana a rana daya, kasar Amurka ita kadai ta kada kuri’ar kin amincewa a taron tattauna rikicin Isra’ila da Falasdinu na kwamitin sulhun MDD, inda ta sake hana ruwa gudu ga yunkurin kasashen duniya na neman tsagaita bude wuta a zirin Gaza. Wato kasar Amurka ta kakaba takunkumi na kashin kai kan wasu kasashe, da sunan “keta hakkin dan Adam”, yayin da a daya bangaren take goyon bayan kisan da ake yi wa fararen hular Falasdinu. Sannan kuma wai tana “taya al’ummar mutanen duniya murnar ranar kare hakkin dan Adam.

  • COP28: Sin Da Afirka Za Su Bunkasa Hadin Gwiwa A Fannin Raya Kananan Ayyukan Samar Da Makamashi Mai Tsafta
  • Sin: Ya Kamata Kwamitin Sulhu Ya Kara Daukar Matakai Kan Lokaci Don Inganta Tsagaita Bude Wuta Da Kawo Karshen Yaki A Dukkan Fannoni

Sai dai, kowa na da ‘yancin tabbatar da ra’ayinsa dangane da hakkin dan Adam. Lokacin da kasar Amurka da wasu kawayenta ke neman yin amfani da batun hakkin dan-Adam wajen dora wa wani laifi, da yanke hukunci, da sarrafa wasu kasasahe, da hana su samun ci gaba, za mu iya nuna akasin haka. Wato mu yi kokarin mai da hakkin dan Adam yadda ya kamata ya kasance, wanda ya kasance wani karfi dake haifar da ci gaba ga al’ummar dan Adam. A wannan fanni, wani rahoton da wasu kungiyoyin masana na kasar Sin suka fitar a kwanan baya, dangane da batun kare hakkin dan Adam, ya nuna wasu misalai.

ADVERTISEMENT

Cikin rahoton an ayyana ci gaban zaman rayuwar jama’ar kasashen Afirka da aka samu ta hanyar hadin gwiwa tsakanin kasashen Afirka da kasar Sin a kokarin aiwatar da shawarar “Ziri Daya da Hanya Daya” da kasar Sin ta gabatar. Misali, a lardin Bubanza na kasar Burundi, wani manomi mai suna Charles Ngendakumana, ya taba fama da talauci da yunwa. Sai dai daga bisani ya fara noman irin shinkafar zamani da aka tagwaita mai samar da yawan iri ko Hybrid, bisa taimakon da wani masanin ilimin aikin gona na kasar Sin ya samar. Bayan wasu shekaru 4, kudin shigar da ya samu ya ninka. Zuwa yanzu yana da yara 7, har ma ya gina wani sabon gida, gami da bude wani wurin sarrafa shinkafa. Wannan abu bai shafi kare hakkin dan Adam ba? Tabbas ya shafa. Wannan shi ne kare hakkin mutum na rayuwa.

Wani misali na daban da rahoton ya kunsa ya shafi tallafin da gwamnatin kasar Sin ta bayar da zummar taimakawa kauyuka dubu 10 dake nahiyar Afirka kama shirye-shiryen telabijin ta hanyar tauraron dan Adam. Zuwa karshen shekarar 2022, aikin ya amfani mutane kusan miliyan 10, na magidanta fiye da dubu 190, dake kauyuka 9512 na wasu kasashe 21 dake nahiyar Afirka. Wannan aiki ma ya shafi yunkurin kare hakkin dan Adam, inda ya samar da gudunmowa a fannin kare hakkin mutane na neman raya kansu.

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Cikin rahoton an yi amfani da dimbin misalai irin wadannan, wajen bayyana wani daidaitaccen ra’ayi game da hakkin dan Adam, wato hakkin dan Adam na tushe shi ne neman rayuwa, daga baya za a nemi raya kai. Don haka ya kamata kasashe daban daban su yi kokarin hadin gwiwa don inganta harkokin tattalin arziki da na zaman al’umma, daga baya za a iya tabbatar da ci gaban harkokin hakkin dan Adam. Maimakon a yi ta sanya ido kan maganar “keta hakkin dan Adam” da saka takunkumi kan sauran kasashe, zai fi kyau a samar da hakikanin gudunmowa ga yunkurin kare hakkin mutane na rayuwa da raya kansu. A wannan zamanin da ake fuskantar dimbin kalubaloli a fannonin tsaro, da tattalin arziki, da muhalli, da dai sauransu, duniyarmu tana bukatar samun karin gudunmowa ta fuskar kare hakkin dan Adam maimakon takunkumi da yanke hukunci na kashin kai da a karshe ka iya shafar rayuwar bil-Adama.. (Bello Wang)

Dan Adam
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

MASU ALAKA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
Daga Birnin Sin

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
Daga Birnin Sin

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos
Daga Birnin Sin

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Next Post
Yadda Ake Hada Miyar Hanta

Yadda Ake Hada Miyar Hanta

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.