• English
  • Business News
Friday, June 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dora Laifi Kan Wasu Ba Zai Magance Matsalolin Da Amurka Ke Fama Da Su A Cikin Gida Ba

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Amurka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Har kullum, Amurka ta kasance mai kokarin dora alhakin muggan laifukan da ake aikatawa a kasar kan wasu, maimakon lalubo tushensu domin samar da mafita mai dorewa. 

A kokarin ci gaba da nuna kiyayya da yada jita-jita don bata sunan kasar Sin, a baya bayan nan, shugaban Amurka Joe Biden ya sanya kasar Sin cikin wasu jerin kasashe da ya bayyana a matsayin masu samarwa ko safarar miyagun kwayoyi.

  • Me Ya Sa Ake Yawan Samun Laifukan Fashi A Amurka?

Da farko dai, ba ni kadai da na shafe shekaru sama da 5 a kasar Sin ba, har da sauran baki da suka zauna ko ziyarci kasar, za su iya shaida cewa wannan zargi ya saba da ainihin yanayin da ake ciki a kasar. Kowa ya san cewa, safara ko amfani da miyagun kwayoyi a kasar Sin, babban laifi ne da zai fuskanci fushin doka.

Wani abu da kan burge ni da kasar Sin shi ne, yadda a ko da yaushe, ba ta kasa a gwiwa wajen daukar tsauraran matakan yaki da duk wani mugun abu ko muguwar tabi’a da za su iya lahanta moriyar al’ummarta, ciki kuwa har da tu’ammali da miyagun kwayoyi da safararsu.

Abun takaici ne yadda Amurka ta kasa gane cewa, rashin ingantattu matakai da suka kamata da rashin mayar da hankali kan al’ummarta ne tushen matsalolinta. Maimakon ta rika lalubo hanyoyin kyautatawa al’umma da kare su, sai ta bata lokaci wajen dora laifinta kan wata ko wasu kasashe. Lamarin da yake kara nuna rauninta na jagoranci da irin jan aikin dake gabanta.

Labarai Masu Nasaba

Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Yadda NATO Ta Yi Amfani Da Ita A Matsayin Dalilin Neman Fadada

Tinubu Ya Nemi Ƴan Nijeriya Su Taimaka A Yaƙi Shan Muggan Kwayoyi

A ganina, ko a wannan fanni ma, ya kamata Amurka ta yi koyi da dabarun kasar Sin kan yadda take yaki da miyagun kwayoyi da irin gudunmawar da ta bayar a wannan fanni a duniya.

Idan ba a manta ba, kasar Sin ce kasa ta farko a duniya da ta sanya kwayar fentanyl da ma abubuwan da suke da alaka da ita cikin jerin miyagun kwayoyi, lamarin da ya taka muhimmiyar rawa wajen hana samarwa da safara da ma shan kwayar, don haka, bai kamata Amurka ta rika alakanta kasar Sin da safarar ko samar da miyagun kwayoyi ba, wannan wani salo ne na cin zali. (Faeza Mustapha)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Ta'addanci
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ya Kamata Turai Ta Nuna Kwarin Gwiwa Wajen Tinkarar Takarar Kasuwa

Next Post

Babbar Tashar Samar Da Wutar Lantarki Ta Kasa Ta Sake Lalacewa

Related

Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Yadda NATO Ta Yi Amfani Da Ita A Matsayin Dalilin Neman Fadada
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Yadda NATO Ta Yi Amfani Da Ita A Matsayin Dalilin Neman Fadada

14 hours ago
Tinubu Ya Nemi Ƴan Nijeriya Su Taimaka A Yaƙi Shan Muggan Kwayoyi
Daga Birnin Sin

Tinubu Ya Nemi Ƴan Nijeriya Su Taimaka A Yaƙi Shan Muggan Kwayoyi

15 hours ago
An Yi Bikin Nune-Nunen Kayan Al’adu Na Murnar Cika Shekaru 55 Da Kulla Huldar Diflomasiyya Tsakanin Sin Da Italiya A Rome
Daga Birnin Sin

An Yi Bikin Nune-Nunen Kayan Al’adu Na Murnar Cika Shekaru 55 Da Kulla Huldar Diflomasiyya Tsakanin Sin Da Italiya A Rome

15 hours ago
Tattalin Arzikin Sin Na Ci Gaba Da Ba Da Gudunmuwa Ga Habakar Tattalin Arzikin Duniya
Daga Birnin Sin

Tattalin Arzikin Sin Na Ci Gaba Da Ba Da Gudunmuwa Ga Habakar Tattalin Arzikin Duniya

16 hours ago
Afirka CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwa Kan Kiwon Lafiya Da Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Afirka CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwa Kan Kiwon Lafiya Da Kasar Sin

18 hours ago
An Watsa Shirin Talabijin Mai Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” A Italiya
Daga Birnin Sin

An Watsa Shirin Talabijin Mai Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” A Italiya

21 hours ago
Next Post
Nijeriya Tana Bin Nijar, Togo Da Benin Bashin Kudin Wutar Lantarki Biliyan 132

Babbar Tashar Samar Da Wutar Lantarki Ta Kasa Ta Sake Lalacewa

LABARAI MASU NASABA

Ƴan Majalisa Na Binciken Cibiyoyin Ci Gaban Masana’antu 30 Da Aka Yi Watsi Da Su

Ƴan Majalisa Na Binciken Cibiyoyin Ci Gaban Masana’antu 30 Da Aka Yi Watsi Da Su

June 27, 2025
Tinubu Ya Sasanta Wike, Fubara, Da Ƴan Majalisar Ribas

Tinubu Ya Sasanta Wike, Fubara, Da Ƴan Majalisar Ribas

June 27, 2025
Gwamnan Kaduna Ya Yunkura Don Warware Matsalolin Rashin Aikin Yi Ga Matasa – Dan Isan

Gwamnan Kaduna Ya Yunkura Don Warware Matsalolin Rashin Aikin Yi Ga Matasa – Dan Isan

June 27, 2025
Sojojin Sama Sun Yi Lugudan Wuta Kan Ƴan Ta’adda A Jihar Neja

Sojojin Sama Sun Yi Lugudan Wuta Kan Ƴan Ta’adda A Jihar Neja

June 27, 2025
2027: An Samu Ruɗani Kan Buƙatar Yi Wa ADA Rajista Don Ta Zama Jam’iyya

2027: An Samu Ruɗani Kan Buƙatar Yi Wa ADA Rajista Don Ta Zama Jam’iyya

June 27, 2025
Sarkin Yarbawan Funtuwa Ya Nemi A Daƙile Aiyukan Masu Ba ‘Yan Ta’adda Bayanan  Sirri

Sarkin Yarbawan Funtuwa Ya Nemi A Daƙile Aiyukan Masu Ba ‘Yan Ta’adda Bayanan  Sirri

June 27, 2025
Rundunar Sojin Nijeriya Ta Tabbatar Da Kisan Jami’anta A Kaduna Da Neja

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Tabbatar Da Kisan Jami’anta A Kaduna Da Neja

June 27, 2025
Ziyarar Manzon Allah (SAW) A Madinah (3)

Ziyarar Manzon Allah (SAW) A Madinah (3)

June 27, 2025
Amince Wa Al’umma Mallakar Makamai Zai Ƙara Tsananta Rashin Tsaro — IGP

Amince Wa Al’umma Mallakar Makamai Zai Ƙara Tsananta Rashin Tsaro — IGP

June 27, 2025
Wata 6 Da Haramta Kauyawa Day A Kano: Badalar Na Ci Gaba Da Gudana 

Wata 6 Da Haramta Kauyawa Day A Kano: Badalar Na Ci Gaba Da Gudana 

June 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.