Hukumar tsaro ta farin kaya (DSS), ta kama wani matashi mai suna Innocent Chukwuma a Jihar Ribas, bisa zargin yin kira da a yi juyin mulki ta hanyar amfani da kafafen sada zumunta.
Masani kan harkokin tsaro, Zagazola Makama ne, ya bayyana hakan a shafinsa na X, inda ya ce DSS ta bi diddigin Chukwuma bayan ya wallafa saƙonnin da ya yi kira ga sojoji su kifar da gwamnatin Nijeriya.
- Ba Matakan Tinubu Ne Suka Karyar Da Farashin Kayan Abinci Ba – ADC
- Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba
Chukwuma ya wallafa cewa “ana buƙatar a yi juyin mulki a Nijeriya” tare da kira ga ‘yan ƙasa da su goyi bayan dakarun soji.
Makama, ya ce DSS ta kama matashin bayan ta bibiyi rubutunsa a Intanet.
Yanzu yana hannun jami’an tsaro kuma yana taimakawa wajen gudunar da bincike.
An rufe asusunsa na X saboda karya ƙa’idodin dandalin, kuma har yanzu DSS ba ta gurfanar da shi a kotu ba.














