ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dubban Mambobin Jam’iyyar APC Sun Sauya Sheka Zuwa Jam’iyyar PDP A Bauchi

A Bayyana Sunayen Wadanda Suka Fice Din - APC

by Khalid Idris Doya
4 years ago
PDP

Dan takarar shugaban matasa na jam’iyyar APC a Jihar Bauchi, Alhaji Adamu Dako tare da magoya bayansa sun ayyana ficewa daga jam’iyyar APC zuwa jam’iyyar PDP.

Da ya ke jawabi a lokacin yankan katin shiga PDP a ofishin jam’iyyar da ke karamar hukumar Bauchi a ranar Litinin, Dako ya bayyana cewar abubuwa ba su tafiya daidai a cikin APC don haka ne ya yanke shawarar ficewa.

  • Gwamnatin Legas Ta Rufe Wata Makaranta Saboda Mutuwar Dalibi
  • An Fitar Da Rahoton Nazari Game Da Yanayin Aiki Na Alummun Yankin Xinjiang

“Yau ni da magoya bayana sama da dubu bakwai (7,000) mun ayyana ficewa daga jam’iyyar APC zuwa PDP.

ADVERTISEMENT

“Na kasance a da baya jagora a cikin jam’iyyar APC, amma cikin ikon Allah na fice daga jam’iyyar sakamakon matsaloli da suke jibge a cikinta. Na yi nadamar bata shekara da shekaru a cikin jam’iyyar APC.”

Alhaji Dako ya ce, dukkanin alamun fadin jam’iyyar APC a jihar Bauchi ya tabbata, yana mai cewa, hatta zabin da jam’iyyar ta yi wa dan takarar gwamnan Sadik Baba Abubakar alamu ne da ke nuna ba za ta iya samun nasara a zaben gwamnan jihar ba.

LABARAI MASU NASABA

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

Rashin Mulki Ke Firgita Atiku – Kakakin APC Na Kaduna

“Wannan dan takara da jam’iyyar APC ta ayyana kalubale ne a gabanta a zaben 2023.”

“Duk wanda ya san yadda aka yi hadaka aka kafa APC, yanzu kowa ya san ba jam’iyya ake yi ba son zuciya kawai ake bi. APC ta mutu murus a jihar Bauchi. Na shigo jam’iyyar PDP da kyakkyawar manufa.”

Ya ce, sun shiga PDP ne lura da irin nasarorin da gwamnan jihar Bala Muhammad ya cimma na kyautata jihar.

Don haka ne ya nuna kwarin guiwarsa na cewa gwamna Bala zai sake samun nasara a karo na biyu tare da kiran al’umma da su mara wa gwamnan ba.

Da yake amsar wadanda suka sauya shekar, shugaban jam’iyyar PDP a karamar hukumar Bauchi, Alhaji Abdulkadir Alin Bababa, ya sanar da cewa, jam’iyyar ta karbi sabbin mambobin jam’iyyar APC da suka sauya sheka zuwa PDP su dubu bakwai.

Shugaban wanda ya samu wakilcin, mataimakinsa Sani Ahmad, tare da sauran shugabanin jam’iyyar a karamar hukumar, ya bai wa wanda suka dawo jam’iyyar tabbacin samun adalci daga wajensu tare da share musu hawayen matsalolin da suka zo da su, ya rokesu da su taimaka domin samun nasarar PDP a 2023.

Shi ma a jawabinsa na lale ga sabbin mambobin, babban mai bai wa gwamnan jihar Bauchi shawara kan harkokin siyasa, Hon. Abubakar Faggo, ya bayyana cewar yadda ake shigowa cikin jam’iyyar PDP alamu ne da ke nuna irin gamsuwa da salon mulkin gwamna Bala.

Ya ce, tabbas gwamna Bala Muhammad na gudanar da kyawawan ayyukan bunkasa jihar Bauchi, don haka ne ya nemi jama’ar jihar da su kara ba shi dama domin kyautata jihar, ya kuma nuna cewa tabbas wadanda suka dawo jam’iyyar za su samu goyon baya daga PDP.

Faggo, ya nuna cewa jam’iyyar APC bata kyauta wa mambobinta, don haka ne ma suke ta komawa cikin PDP.

“Mu a PDP akwai adalci, don haka kun zo lallai kuma za a muku adalci.”

Da ya ke maida martani kan wannan matakin, jami’in watsa labarai na jam’iyyar APC a jihar Bauchi, Alhaji Adamu Aliyu Jalla, ya ce suna da ja man cewa mutum 7,000 sun fice daga jam’iyyarsu.

Ya ce, kowa na da ‘yancin sauya sheka, amma ya ce da dandazon mutum kaza fita wannan kuma akwai bukatar tabbatarwar kafin amincewa.

“Farfagandar siyasa ce kawai. Mutum 7000 wasa ne. Mu ba mu da bayanin cewa wannan adadin sun fita a jam’iyyunmu. Don haka muna kalubala tarsa da ya bayyana sunayen mutum 7000 din.”

Ya ce babu gaskiya na cewa ana gudanar da mulki cikin jam’iyyar APC bisa rashin adalci, ya nuna cewa suna da karfin da za su iya cin zaben 2023 tare da goyon bayan al’ummar jihar.

PDP
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Yaro Ya Harbe Kansa Har Lahira Bayan Mafarauci Ya Yi Sakaci Da Bindigarsa A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    An Kama Mutane 5 Da Sassan Jikin Ɗan’Adam Za Su Yi Tsafi A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mai Neman Takarar Gwamnan Bauchi, Bala Jibrin, Ya Fice Daga APC Kan Zargin Ɗoki-ɗora

MASU ALAKA

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu
Manyan Labarai

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

September 9, 2026
Rashin Mulki Ke Firgita Atiku – Kakakin APC Na Kaduna
Siyasa

Rashin Mulki Ke Firgita Atiku – Kakakin APC Na Kaduna

September 9, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027
Siyasa

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Next Post
NCC Ta Bai Wa Kamfanonin Sadarwa Kwana 30 Don Warware Matsalolin Masu Amfani Da Layukansu

NCC Ta Bai Wa Kamfanonin Sadarwa Kwana 30 Don Warware Matsalolin Masu Amfani Da Layukansu

LABARAI MASU NASABA

Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

September 10, 2026
Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

September 10, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

September 10, 2026
’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

September 10, 2026
2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

September 10, 2026
Zabe: Gwamnatin Kano Ta Taƙaita Zirga-zirgar Mutane Da Ababen Hawa

Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu

September 10, 2026
Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026
Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.