• English
  • Business News
Saturday, June 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Duk Da Matsin Tattalin Arziki, Bukukuwan Sallar Bana Ta Yi Armashi

by Rabi'at Sidi Bala
2 months ago
in Labarai
0
Duk Da Matsin Tattalin Arziki, Bukukuwan Sallar Bana Ta Yi Armashi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shafin TASKIRA shafi ne daya saba zakulo muku batutuwa daban-daban wadanda suka shafi al’umma, cikin sun hadar da; zamantakewar aure, rayuwar yau da kullum, rayuwar matasa, soyayya, da dai sauransu.

Tsokacin mu na yau zai yi duba ne game da shagulgulan bikin sallar da ta gabata, inda muka ji ta bakin wasu daga cikin mabiya shafin game da wannan batu; “Ya bikin sallah ya kasance a garinku/unguwarku?, wadanne wurare aka kai ziyara dan zumunci ko kuma nishadi?, ko me za a ce game da wannan salar da ta gabata?” Ga dai bayanan nasu kamar haka:

  • Ana Zargin Wani ÆŠansanda Da Kisan Wata Mata Kan Cin Hancin Naira 2,000 — Bincike
  • Matasa 4 Sun Yi Garkuwa Da Yaro, Sun Kashe Shi A Bauchi

Sunana Zahra’u Abubakar Kasuwar Takari Gama-D:

Tattali

Mun yi bikin sallah lafiya Lau Alhamdulillah an gudanar da sallar idi wasu wuraren 8:05 wasu 8:30 wasu 9am. Na ziyarci kanwar mahaifiya ta. To babu abin da zance sai godiya ga Allah Alhamdulillah Allah ya maimaita mana Allah ya amshi ibadun mu ya sa mu ga na badin badada muna masu rai da lafiya a cikin aminci.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Addu’ar Kwana 3 Don Samun Isasshen Abinci

Sarkakiyar Da Ke Tattare Da Zaben 2027 Da Yadda Za Ta Kaya

Sunana Lawan Isma’il (Lisary) Jihar Kano Rano LGA:

Tattali

Alhamdulillah mun yi bikin sallah lafiya kalau a garin Rano kamar yadda muka saba duk shekara kowa yana uzurinsa kamar yadda aka saba lafiya. Alhamdulillah an yi ziyarce-ziyarce lafiya gidajen ‘yan’uwa da surukai da abokan arziki da kuma haduwa da tsofaffin dalibai. Gaskiya sai godiya duba da yadda ake cikin tsadar rayuwa da wani irin hali na kuncin rayuwa a wannan a kasa ta mu sai dai mu a yankinmu na karamar hukumar Rano muna cikin alhinin kisan gillar da aka yi wa ‘yan’uwanmu a yankin kudu a jihar Edo ba zamu tava manta wannan aika-aika da aka yi mana ba Allah ya isar mana, Allah ya sa mudace Allah yasa mun yi ibadu karvabbu Allah ya maimaita mana masu amfani.

Sunana Zainab Zeey Ilyas Jihar Kaduna:

Tattali

Bikin sallah ya kayatar da mu sosai sai dai wasu ba kamar yadda suka saba duk shekara ba, musamman yadda sallar ta zo ba tare da wasu sun kammala shiri ba. Na ziyarci ‘yan’uwa na na kusa da na nesa kamar Babbar Yayata, Kawu na, Aunty na, dan har garin Kano mun ziyarta, sai wuraren shakatawa, gidajen tarihi, da kuma gidan Sarki. Sallar bana za a ce da ita ma sha Allah Alhamdulillahi, an yi ta cikin zaman lafiyya da kwanciyyar hakali, mun yi kallon hawa.

Sunana Aminu Adamu, Malam Maduri A Jihar Jigawa:

Tattali

Alhamdullilah Ma sha Allah, hakika mun gudanar da bikin sallar idi da shagulgulan bikin sallah cikin nutsuwa da kwanciyar hankali, al’umma sun yi hidimar sallah daidai gwargwado duk da halin da ake ciki na matsin tattalin arzikin da tsadar rayuwa, fatan mu Allah ya karvi ibadar mu bakidaya. To maganar zuwa ziyara hakika mun ziyarci gidajen ‘yan’uwa da abokan arziki an gaisa an yi zumunci sosai kai har ma mun samu damar zuwa garuruwan ‘yan’uwa dake nesa domin sada zumunci. To batun sallah sai mu ce Alhamdullilah Ma sha Allah tunda mun samu damar gudanar da sallah cikin nutsuwa da kwanciyar hankali domin koda ba a samu damar yin hidima mai yawa ba tunda aka samu damar gudanarwa cikin lumana dole mu godewa Allah daya ba mu wannan dama, daga karshe nake kara addu’ar Allah ya karvi ibadar mu ya yafe mana kura-kuran mu don darajar fiyayyen halitta manzon Allah (S.A.W).

Sunana Hafsat Yusuf Karamar Hukumar Isa A Jihar Sokoto:

Hidimar wannan sallar ta zamo mai kayatarwa a garin mu duk da matsalar tsaron da ake fama da ita a yankin, mun kai ziyara ga ‘yan’uwa kuma mun hadu da wadanda muka dade ba mu hadu da su ba, abun akwai burgewa. Daga karshe ba abun da zan ce sai Alhamdulillah Allah ya maimaita mana.

Sunana Yasar Saleh Zareku Miga A Jihar Jigawa:

Tattali

Yadda bikin sallah yake kasancewa a garin mu sai mu ce Alhamdullilah Ma sha Allah. Da zarar gari ya waye kowa da kowa zai fita filin idi dan gabatar da sallah da an sakko za ai ta kai ziyara zuwa gidan ‘yan’uwa da abokan arziki; yayye, kanne da ‘yan’uwa da abokan arziki. To sai godiyar Allah amma kam ta zo wa mutane da yanayi na tsadar rayuwa da matsin tattalin arzikin da muke fama da shi amma duk da haka Alhamdullilah tun da mun samu damar gudanar da bikin cikin nutsuwa da kwanciyar hankali.

Sunana Fatima Ibrahim Jihar Katsina:

Tattali

Bikin sallah dai a unguwar da nake ya kasance abu ne mai ban sha’awa, mun je gurare da dama kamar gidan zoo, gurin wasa, gidan ‘yan’uwa da abokan arziki da gidan makama. A gaskiya dai wannan sallar za a iya cewa ta zo kwatsan dan wadansu basu tanadi dinkin sallah ba da kuma lalle da sauransu, ni dai na samu nayi da wuri komai kalau a wajena.

Sunana Fatima Nura Kila, A jihar Jigawa:

Alhamdulillah mun yi sallah lafiya inda kowa yake cikin farin ciki a wannnan rana ta sallah duk da yanayin da ake ciki, amma mutane sun yi ado daidai wadaitar kowa, fatanmu Allah ya nuna mana wata sallar. Alhamdulillah mun yi ziyarar ‘yan’uwa da abokan arziki mutanan da aka dade ba a hadu ba mun kai musu ziyara Yayin da kowa yake farin ciki da ziyarar juna. Wannnan sallar sai dai mu ce Alhamdulillah domin an samu zaman lafiya mun yi ta cikin nutsuwa,walwa da kaunar juna, Ubangiji ya karvi ibadunmu ya kai mu wata shekarar mai albarka ya sa muna raye.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ArzikiSallah
ShareTweetSendShare
Previous Post

Wajibcin Gina Al’ummar Duniya Mai Kyakkyawar Makomar Bai Daya

Next Post

Kofin Duniya 2026: Kasashen Da Suka Samu Tikitin Shiga Gasar Zuwa Yanzu

Related

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Addu’ar Kwana 3 Don Samun Isasshen Abinci
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Addu’ar Kwana 3 Don Samun Isasshen Abinci

25 minutes ago
jam'iyyu
Rahotonni

Sarkakiyar Da Ke Tattare Da Zaben 2027 Da Yadda Za Ta Kaya

13 hours ago
Nijeriya Na Kan Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arziki Da Dawo Da Martabar Ƙasa — Ministan Yaɗa Labarai
Labarai

Nijeriya Na Kan Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arziki Da Dawo Da Martabar Ƙasa — Ministan Yaɗa Labarai

14 hours ago
Nijeriya Da Morocco Za Su Sanya Hannu Kan Kulla Yarjejeniyar Aikin Bututun Iskar Gas
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Himmatu Wajen Inganta Karfin Sashen Fetur Da Gas Na Cikin Gida

15 hours ago
Gwamnati Ta Yi Karin Haske Kan Biyan Tallafin Rage Radadi Da Mafi Karancin Albashi
Labarai

Gwamnati Ta Yi Karin Haske Kan Biyan Tallafin Rage Radadi Da Mafi Karancin Albashi

17 hours ago
Dawanau
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Dukufa Wajen Karya Farashin Kayan Abinci – Minista

19 hours ago
Next Post
Kofin Duniya 2026: Kasashen Da Suka Samu Tikitin Shiga Gasar Zuwa Yanzu

Kofin Duniya 2026: Kasashen Da Suka Samu Tikitin Shiga Gasar Zuwa Yanzu

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Addu’ar Kwana 3 Don Samun Isasshen Abinci

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Addu’ar Kwana 3 Don Samun Isasshen Abinci

June 14, 2025
Kudaden Da Ake Karba A Kogin Hadejia Jama’are Daga Hannun Manoma, Ba Haraji Ba Ne – HJRBDA

Kudaden Da Ake Karba A Kogin Hadejia Jama’are Daga Hannun Manoma, Ba Haraji Ba Ne – HJRBDA

June 14, 2025
Wani Gidan Gona A Jihar Ogun Zai Fitar Da Tarwada Ta Kimanin Naira Biliyan Shida A 2025

Wani Gidan Gona A Jihar Ogun Zai Fitar Da Tarwada Ta Kimanin Naira Biliyan Shida A 2025

June 14, 2025
Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai

June 14, 2025
APC

Sauya Sheka Ya Sa APC Ta Samu Gagarumin Rinjaye A Majalisun Tarayya

June 14, 2025
Taron Koli Na Sin Da Kasashen Yankin Tsakiyar Asiya Karo Na Biyu Zai Ingiza Manufar Kara Dunkulewar Sassan Yankin

Taron Koli Na Sin Da Kasashen Yankin Tsakiyar Asiya Karo Na Biyu Zai Ingiza Manufar Kara Dunkulewar Sassan Yankin

June 13, 2025
jam'iyyu

Sarkakiyar Da Ke Tattare Da Zaben 2027 Da Yadda Za Ta Kaya

June 13, 2025
Nijeriya Na Kan Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arziki Da Dawo Da Martabar Ƙasa — Ministan Yaɗa Labarai

Nijeriya Na Kan Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arziki Da Dawo Da Martabar Ƙasa — Ministan Yaɗa Labarai

June 13, 2025
Babban Jami’in Diflomasiyyar Kasar Sin Ya Yi Kiran Karfafa Alaka Da Afirka

Babban Jami’in Diflomasiyyar Kasar Sin Ya Yi Kiran Karfafa Alaka Da Afirka

June 13, 2025
Xi Ya Yi Kira Da A Kara Azamar Gina Kasa A Gabar Da Ake Bikin Cika Shekaru 120 Da Haihuwar Dan Mazan Jiya Chen Yun

Xi Ya Yi Kira Da A Kara Azamar Gina Kasa A Gabar Da Ake Bikin Cika Shekaru 120 Da Haihuwar Dan Mazan Jiya Chen Yun

June 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.