• English
  • Business News
Saturday, July 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Duk Da Matsin Tattalin Arziki, Bukukuwan Sallar Bana Ta Yi Armashi

by Rabi'at Sidi Bala
3 months ago
in Labarai
0
Duk Da Matsin Tattalin Arziki, Bukukuwan Sallar Bana Ta Yi Armashi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shafin TASKIRA shafi ne daya saba zakulo muku batutuwa daban-daban wadanda suka shafi al’umma, cikin sun hadar da; zamantakewar aure, rayuwar yau da kullum, rayuwar matasa, soyayya, da dai sauransu.

Tsokacin mu na yau zai yi duba ne game da shagulgulan bikin sallar da ta gabata, inda muka ji ta bakin wasu daga cikin mabiya shafin game da wannan batu; “Ya bikin sallah ya kasance a garinku/unguwarku?, wadanne wurare aka kai ziyara dan zumunci ko kuma nishadi?, ko me za a ce game da wannan salar da ta gabata?” Ga dai bayanan nasu kamar haka:

  • Ana Zargin Wani Ɗansanda Da Kisan Wata Mata Kan Cin Hancin Naira 2,000 — Bincike
  • Matasa 4 Sun Yi Garkuwa Da Yaro, Sun Kashe Shi A Bauchi

Sunana Zahra’u Abubakar Kasuwar Takari Gama-D:

Tattali

Mun yi bikin sallah lafiya Lau Alhamdulillah an gudanar da sallar idi wasu wuraren 8:05 wasu 8:30 wasu 9am. Na ziyarci kanwar mahaifiya ta. To babu abin da zance sai godiya ga Allah Alhamdulillah Allah ya maimaita mana Allah ya amshi ibadun mu ya sa mu ga na badin badada muna masu rai da lafiya a cikin aminci.

Labarai Masu Nasaba

“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

Sunana Lawan Isma’il (Lisary) Jihar Kano Rano LGA:

Tattali

Alhamdulillah mun yi bikin sallah lafiya kalau a garin Rano kamar yadda muka saba duk shekara kowa yana uzurinsa kamar yadda aka saba lafiya. Alhamdulillah an yi ziyarce-ziyarce lafiya gidajen ‘yan’uwa da surukai da abokan arziki da kuma haduwa da tsofaffin dalibai. Gaskiya sai godiya duba da yadda ake cikin tsadar rayuwa da wani irin hali na kuncin rayuwa a wannan a kasa ta mu sai dai mu a yankinmu na karamar hukumar Rano muna cikin alhinin kisan gillar da aka yi wa ‘yan’uwanmu a yankin kudu a jihar Edo ba zamu tava manta wannan aika-aika da aka yi mana ba Allah ya isar mana, Allah ya sa mudace Allah yasa mun yi ibadu karvabbu Allah ya maimaita mana masu amfani.

Sunana Zainab Zeey Ilyas Jihar Kaduna:

Tattali

Bikin sallah ya kayatar da mu sosai sai dai wasu ba kamar yadda suka saba duk shekara ba, musamman yadda sallar ta zo ba tare da wasu sun kammala shiri ba. Na ziyarci ‘yan’uwa na na kusa da na nesa kamar Babbar Yayata, Kawu na, Aunty na, dan har garin Kano mun ziyarta, sai wuraren shakatawa, gidajen tarihi, da kuma gidan Sarki. Sallar bana za a ce da ita ma sha Allah Alhamdulillahi, an yi ta cikin zaman lafiyya da kwanciyyar hakali, mun yi kallon hawa.

Sunana Aminu Adamu, Malam Maduri A Jihar Jigawa:

Tattali

Alhamdullilah Ma sha Allah, hakika mun gudanar da bikin sallar idi da shagulgulan bikin sallah cikin nutsuwa da kwanciyar hankali, al’umma sun yi hidimar sallah daidai gwargwado duk da halin da ake ciki na matsin tattalin arzikin da tsadar rayuwa, fatan mu Allah ya karvi ibadar mu bakidaya. To maganar zuwa ziyara hakika mun ziyarci gidajen ‘yan’uwa da abokan arziki an gaisa an yi zumunci sosai kai har ma mun samu damar zuwa garuruwan ‘yan’uwa dake nesa domin sada zumunci. To batun sallah sai mu ce Alhamdullilah Ma sha Allah tunda mun samu damar gudanar da sallah cikin nutsuwa da kwanciyar hankali domin koda ba a samu damar yin hidima mai yawa ba tunda aka samu damar gudanarwa cikin lumana dole mu godewa Allah daya ba mu wannan dama, daga karshe nake kara addu’ar Allah ya karvi ibadar mu ya yafe mana kura-kuran mu don darajar fiyayyen halitta manzon Allah (S.A.W).

Sunana Hafsat Yusuf Karamar Hukumar Isa A Jihar Sokoto:

Hidimar wannan sallar ta zamo mai kayatarwa a garin mu duk da matsalar tsaron da ake fama da ita a yankin, mun kai ziyara ga ‘yan’uwa kuma mun hadu da wadanda muka dade ba mu hadu da su ba, abun akwai burgewa. Daga karshe ba abun da zan ce sai Alhamdulillah Allah ya maimaita mana.

Sunana Yasar Saleh Zareku Miga A Jihar Jigawa:

Tattali

Yadda bikin sallah yake kasancewa a garin mu sai mu ce Alhamdullilah Ma sha Allah. Da zarar gari ya waye kowa da kowa zai fita filin idi dan gabatar da sallah da an sakko za ai ta kai ziyara zuwa gidan ‘yan’uwa da abokan arziki; yayye, kanne da ‘yan’uwa da abokan arziki. To sai godiyar Allah amma kam ta zo wa mutane da yanayi na tsadar rayuwa da matsin tattalin arzikin da muke fama da shi amma duk da haka Alhamdullilah tun da mun samu damar gudanar da bikin cikin nutsuwa da kwanciyar hankali.

Sunana Fatima Ibrahim Jihar Katsina:

Tattali

Bikin sallah dai a unguwar da nake ya kasance abu ne mai ban sha’awa, mun je gurare da dama kamar gidan zoo, gurin wasa, gidan ‘yan’uwa da abokan arziki da gidan makama. A gaskiya dai wannan sallar za a iya cewa ta zo kwatsan dan wadansu basu tanadi dinkin sallah ba da kuma lalle da sauransu, ni dai na samu nayi da wuri komai kalau a wajena.

Sunana Fatima Nura Kila, A jihar Jigawa:

Alhamdulillah mun yi sallah lafiya inda kowa yake cikin farin ciki a wannnan rana ta sallah duk da yanayin da ake ciki, amma mutane sun yi ado daidai wadaitar kowa, fatanmu Allah ya nuna mana wata sallar. Alhamdulillah mun yi ziyarar ‘yan’uwa da abokan arziki mutanan da aka dade ba a hadu ba mun kai musu ziyara Yayin da kowa yake farin ciki da ziyarar juna. Wannnan sallar sai dai mu ce Alhamdulillah domin an samu zaman lafiya mun yi ta cikin nutsuwa,walwa da kaunar juna, Ubangiji ya karvi ibadunmu ya kai mu wata shekarar mai albarka ya sa muna raye.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ArzikiSallah
ShareTweetSendShare
Previous Post

Wajibcin Gina Al’ummar Duniya Mai Kyakkyawar Makomar Bai Daya

Next Post

Kofin Duniya 2026: Kasashen Da Suka Samu Tikitin Shiga Gasar Zuwa Yanzu

Related

“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai
Ra'ayi Riga

“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

6 hours ago
2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a
Rahotonni

2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

7 hours ago
Illar Kakaba Wa Majalisa Ta 10 Shugabanni Ga Gwamnatin Tinubu – Dattawan Arewa
Labarai

Majalisar Tarayya Ta Karrama NPA Da Kyautar Gaskiya Da Riƙon Amana Ta 2025

9 hours ago
Sojoji Sun Sake Ceto ‘Yan Matan Makarantar Chibok 2
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kama Mutum 2 Da AK-47 A Taraba

9 hours ago
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa
Labarai

Amurka Ta Rage Wa’adin Bizar ‘Yan Nijeriya Zuwa Wata Uku

11 hours ago
Fadar Shugaban Ƙasa Ta Ƙaryata Alaƙanta Shettima Da Kwatanta Jonathan Da Tinubu Kan Batun Tsige Gwamna
Labarai

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Ƙaryata Alaƙanta Shettima Da Kwatanta Jonathan Da Tinubu Kan Batun Tsige Gwamna

11 hours ago
Next Post
Kofin Duniya 2026: Kasashen Da Suka Samu Tikitin Shiga Gasar Zuwa Yanzu

Kofin Duniya 2026: Kasashen Da Suka Samu Tikitin Shiga Gasar Zuwa Yanzu

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

July 11, 2025
Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

July 11, 2025
Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 

Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 

July 11, 2025
Nijeriya Na Fuskantar Siyasa Mara Tabbas —  Peter Obi

2027: Takarar Shugaban Kasa Zan Yi Ba Mataimaki Ba – Peter Obi

July 11, 2025
“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

July 11, 2025
2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

July 11, 2025
Wang Yi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka

Wang Yi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka

July 11, 2025
Fahimtar Kyawun Bambance-Bambance Kyakkawar Hanya Ce Ta Wanzar Da Zaman Jituwa A Duniya

Fahimtar Kyawun Bambance-Bambance Kyakkawar Hanya Ce Ta Wanzar Da Zaman Jituwa A Duniya

July 11, 2025
Illar Kakaba Wa Majalisa Ta 10 Shugabanni Ga Gwamnatin Tinubu – Dattawan Arewa

Majalisar Tarayya Ta Karrama NPA Da Kyautar Gaskiya Da Riƙon Amana Ta 2025

July 11, 2025
FRCN Ya Kaddamar Da Shirin Koyar Da Sinanci Mai Taken “Hello China”

FRCN Ya Kaddamar Da Shirin Koyar Da Sinanci Mai Taken “Hello China”

July 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.