ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ana Zargin Wani Ɗansanda Da Kisan Wata Mata Kan Cin Hancin Naira 2,000 — Bincike

by Rabi'u Ali Indabawa
1 year ago
Dansanda

Wani korarren dansanda, Aremu Musiliu, wanda ake zargi da kashe wata mata mai shayarwa mai suna Comfort Udoh, ya bace bayan da ya karbi beli a asirce daga babbar kotun Jihar Legas, kamar yadda binciken jaridar PUNCH Metro ya gano.

Musiliu, tare da wasu ‘yansanda biyar, an yi zargin sun harbi babur mai kafa uku a unguwar Isheri a shekarar 2015, wanda mijin Comfort, Godwin Udoh ke tukawa.

  • Dansandan Da Ya Ki Karbar Cin Hancin Miliyan 150 Ya Samu Shatara Ta Arziki
  • Dokar Ta-ɓaci A Ribas: GwamnoninPDP Sun Ƙalubalanci Hukuncin Tinubu A Kotun Ƙoli

Rahotanni sun ce babur din na dauke Comfort ne da ‘ya’yanta hudu, ciki har da wani jariri dan watanni hudu a lokacin da suke dawowa gida daga wani shiri na coci.

ADVERTISEMENT

Duk da sun bayyana cewa su ba matafiya ba ne sun nufi gida ne kawai bayan kammala ibada, Musiliu ya dage kan sai an ba shi cin hancin Naira 2,000 kafin ya bar su su wuce.

A lokacin da daya daga cikin ‘yan sandan da ke shingen binciken ya umurci dangin su tafi, Musiliu ya ce ya harba makaminsa kan babur din.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Harbin dai ya samu Comfort ne a kai, inda nan take ta mutu, yayin da wasu harsasai suka samu mijinta a mukamuki da kafadarsa dama.

Yayin da ‘ya’yansu ke kururuwar firgici, rahotanni sun ce jami’an sun gudu daga wurin.

An kori Musiliu daga aikin ‘yansanda ne a ranar 17 ga watan Satumba, 2015, daga bisani kuma aka bayar da belinsa a shekarar 2017 ba tare da sanin dangin da ya kashewa ‘yan uwa ba.

Bayanan kotun sun nuna cewa mai shari’a O.A. Taiwo na Kotun 26, Babban Kotun Ikeja, ya bayar da belin Musiliu a kan Naira miliyan 1 tare da mutane biyu.

A hukuncin kotun, Mai shari’a Taiwo ya bayyana cewa, “Sashe na 115(1) na dokar shari’a ta shekarar 2011 ya bai wa kotu damar bayar da belin wanda ake tuhuma da laifin kisa.

“Don haka kotu na da hurumin bayar da belin wanda ake tuhuma da laifin kisa ko kuma a’a, hakkin mai nema ne ya nuna ta hanyar bayar da wasu bukatu na musamman wadanda za su bai wa kotu damar yin amfani da damar da ta ga ya dace ga mai bukata.”

Tun lokacin da aka bayar da belin Musiliu, jaridar PUNCH Metro ta gano cewa har yanzu ba a san inda Musiliu yake ba duk da zaman kotun da aka yi da kuma yunkurin kama wadanda za su tsaya masa.

Da yake zantawa da jaridar PUNCH, Godwin Udoh ya bayyana takaicinsa da irin wannan rashin imani.

“Na yi mamaki da ban gan shi (dan sandan) a kotu ba kafin daga baya na gano cewa an bayar da belinsa, babu wanda ya yi tsammanin za a bayar da belinsa.

“Duk lokacin da suka nemi gidan yarin da su gabatar da shi a gaban kotu, sai su ba da uzuri kamar rashin man da za su yi jigilarsa. A haka na fara binciken abin da ke faruwa,” in ji Udoh.

Udoh ya bayyana cewa binciken da ya yi ne ya sa ya gane cewa lallai an saki Musiliu.

“Kotun da ke tafiyar da shari’ar a yanzu tana babbar kotun TBS, amma ba su taba kawo shi wurin domin gurfanar da shi ba, lokacin da aka taba gurfanar da shi a gaban kotun majistare da ke Ebute Metta a shekarar 2015 da lamarin ya faru,” in ji shi.

“Alkalin mai shari’a, Hon. Justice Akintoye, har ma ya rubuta wa dukkan gidajen yarin Jihar Legas wasiku, amma sun ki gabatar da wannan mutum a kotu, har ma sun bayar da sammacin kama mutum biyun da za su tsaya masa.

Udoh ya koka da cewa, “Kotun gaba daya ba ta yarda an bayar da belinsa ba, sai da ni kaina na je na gano shi, a lokacin ne na tabbatar da cewa kotun Honarabul Taiwo da ke Ikeja ta bayar da belinsa, yanzu mutumin ya bace, ba mu sake jin komai a kansa ba.”

Har yanzu dai ana ci gaba da shari’ar, inda aka shirya zaman kotu na gaba a ranar 9 ga watan Afrilu, sai dai Udoh bai da tabbas ko za a yi adalci.

“Babu wanda ya tsaya masa a kotu a matsayin lauyansa, sai dai mai gabatar da kara daga ma’aikatar shari’a ta Jihar Legas ya ce in yi kokarin ganin su a Alausa domin su samu hanyar gurfanar da shi a gaban kotu,” in ji shi.

Udoh, yayin da yake tunani a kan rayuwarsa bayan wani mummunan lamari da ya faru a shekarar 2015, ya bayyana cewa an bar shi da ‘ya’yansa suna kokawa su kadai, duk da alkawuran da shugabannin ‘yansanda suka dauka na tallafa musu.

“Ciwon da nake ji daga wannan rauni har yanzu ba na iya jurewa,” in ji shi.

“Har yanzu akwai wani karfe a cikin mukamukina da ya kamata a cire, likitan ya ce suna bukatar fitar da shi a maye gurbinsa da kashi don in iya tauna da kyau. Amma yayin da nake magana da ku, karfen yana ci gaba da cutar da ni.

Udoh ya kuma tunatar da yadda ‘yansanda suka kasa taimakawa wajen binne matarsa marigayiya a shekarar 2016.

“Na gana da kwamishinan ‘yansandan Jihar Legas, amma ya ce min ‘yansanda ba sa binne kowa kuma in yi da kaina,” in ji shi.

Ya koka da cewa duk da tabbacin da ‘yansandan suka yi sun yi watsi da shi da iyalansa.

“Sun yi alkawari za su kula da ni, da biyan duk kudin da nake kashewa na jinya, da kuma tabbatar da cewa an yi mini tiyatar da ta dace, amma sun bar ni ina shan wahala.

“Kudin aikin cire wannan karfe daga mukamukina ya kai miliyoyin Naira, kuma ba ni da wannan kudin,” in ji shi.

Udoh ya ci gaba da bayyana cewa, rundunar ‘yansandan ta kuma yi alkawarin tallafa wa ‘ya’yansa na kudi, kula da lafiya, da bayar da tallafin karatu.

“Sun ce za su saka ni a cikin lissafin albashi don in sami akalla tallafin kudi a kowace shekara. Babu wani abu da ya faru,” in ji shi.

Hatta takardar shedar karatu da aka bai wa ‘ya’yansa daga baya an dawo da su.

“Sun ce kuskure ne kuma za su gyara su mayar da shi ga sufeto-janar domin ya amince min, har yau ban samu ba.”

Ta’asar da ‘yansanda ke yi wa fararen hular da ba su ji ba ba su gani ba ya zama ruwan dare duk da kokarin da ake na shawo kan jami’an da ke da ra’ayin aikata laifuka.

Rundunar ‘yansandan ta kori Sufeto Usman Dikko daga mukaminsa bisa rasuwar Baale na Lotu, Marigayi Cif Fatai Jubril, a shekarar 2023.

An kori wani jami’in da ya yi wa wata yarinya fyade da bindiga a cikin ofishin ‘yansanda a Legas.

Dansanda
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    NSCDC Ta Cafke Mutum 10 Da Ake Zargi Da Satar Kayan Gwamnati Da Kuma Fashi A Kano
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƴansanda Su Ƙi Karɓar Cin Hancin Naira Miliyan 500 Daga Hannun Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙasashen DR Congo Uganda Da Sudan Sun Haɗa Kai Domin Yaƙar Ibola
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Zafin Rana Ya Yi Ajalin Mutum 16 A Indiya

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
Labarai

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Next Post
Kogin Rima Zai Bunƙasa Noma Da Haɓaka Tattalin Arziƙi – Abubakar Malam

Kogin Rima Zai Bunƙasa Noma Da Haɓaka Tattalin Arziƙi - Abubakar Malam

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.