• English
  • Business News
Friday, July 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Duk Da Narka Fiye Da Biliyan 200, Gwamnati Ta Yi Gum A Kan Kidaya

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Labarai
0
Duk Da Narka Fiye Da Biliyan 200, Gwamnati Ta Yi Gum A Kan Kidaya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Duk da kashe sama da naira biliyan 200 wajen gudanar da shirye-shiryen kidayar jama’a da gidaje tun daga shekarar 2014, gwamnatin tarayya ta yi gum kan gudanar da kidayan da aka dage.

An fara gudanar da shirye-shiryen kidayar jama’a ne tun a farkon wannan shekara, wanda aka saka ranar 3 ga Mayun 2023, amma sai tsohuwar gwamnatin Muhammadu Buhari ta dage kidayar har sai wani lokaci.

  • Shin Wasan Kwaikwayon Na Zaben Kakakin Majalisar Wakilan Amurka Ta Kawo Karshe Ne? 
  • Gwamnati Ta Samo Jarin Fiye Da Dala Biliyan 2 A Bangaren Wutar Lantarki

A cewar hukumar kidaya ta kasa (NPC), babban makasudin daukar matakin dage aikin kidayar jama’a a shekarar 2023 shi ne, bayar da dama ga gwamnati mai zuwa.

Ta ce akwai bukatar sabuwar gwamnati ta kasance mai cikakken bayani kan tsarin da ake amfani da shi wajen tattara bayanan kidayar jama’a.

Amma, bayan watanni biyar da kafa sabuwar gwamnati, ba a ji komai ba game da gudanar da lamarin kidayar.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnan Zamfara Ya Raba Buhunan Taki 59,205 Ga Manoman Jihar

Matatun Man Fetur Na Nijeriya Ba Za Su Ci Gaba Da Aiki Yadda Ya Kamata Ba – Dangote

Nijeriya dai na daya daga cikin kasashen yammacin Afirka da ba a san hakikanin yawan mutanenta ba, sannan kuma ta dogara ne da alkaluman kididdigarta a kan hasashe.

An dai gudanar da kidayar jama’a da jidage ta karshe ne a shekarar 2006, kuma tun da ana gudanar da kidayan a duk bayan shekaru goma, ya kamata Nijeriya ta yi kidayar jama’arta na gaba a shekarar 2016, amma sakamakon siyasa da lamari da kudade hakan bai yuwu ba.

Lokacin da aka tuntubi daraktan hulda da jama’a na NPC, Dakta Isiaka Yahaya, ya ce har yanzu hukumar na jiran sanarwar Shugaba Kasa Ahmed Tinubu kan gudanar da kidayan.

“Mun gana da shugaban kasa tare da gabatar masa da tsayinmu, har yanzu muna jiran mu ji ta bakinsa,” in ji shi.

Ya ce jaddada cewa tabbas akwai yuwuwar gudanar da sahihin kidaya a Nijeriya.

Sakamakon rashin gudanar da kidaya ya sa an kasa samun cikakkun bayanai dalla-dalla kan yawan al’ummar kasar da rashin samun tanadin zamantakewa da na ci gaban tattalin arziki, wadanda ke kawo cikas wajen aiwatar da manufofi a Nijeriya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Jega Ya Warware Zare Da Abawa Kan Hanyoyin Tsaftace Zaben Nijeriya

Next Post

Ana Ci Gaba Da Alhinin Mutuwar Malam Adamu Fika

Related

Gwamnan Zamfara Ya Raba Buhunan Taki 59,205 Ga Manoman Jihar
Labarai

Gwamnan Zamfara Ya Raba Buhunan Taki 59,205 Ga Manoman Jihar

31 seconds ago
Matatun Man Fetur Na Nijeriya Ba Za Su Ci Gaba Da Aiki Yadda Ya Kamata Ba – Dangote
Manyan Labarai

Matatun Man Fetur Na Nijeriya Ba Za Su Ci Gaba Da Aiki Yadda Ya Kamata Ba – Dangote

18 minutes ago
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga Tare Da Kwato Makamai A Jihar Filato
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kai Wa ‘Yansanda Hari Tare Da Kashe Wani Mutum Da Raunata Wani A Nasarawa

1 hour ago
An Koka Kan Yadda Tsafi Da Jariran Da Aka Haifa Da Tsagaggen Lebe Ke Karuwa
Manyan Labarai

An Koka Kan Yadda Tsafi Da Jariran Da Aka Haifa Da Tsagaggen Lebe Ke Karuwa

2 hours ago
Bafarawa Ya Kaddamar Da Kungiyar Hada Kan Arewa Da Samar Da Zaman lafiya A Kaduna 
Labarai

Bafarawa Ya Kaddamar Da Kungiyar Hada Kan Arewa Da Samar Da Zaman lafiya A Kaduna 

2 hours ago
Shirin Sabunta Fata Na Tinubu Yana Samar da Damarmakin Cigaba — Minista
Labarai

Shirin Sabunta Fata Na Tinubu Yana Samar da Damarmakin Cigaba — Minista

4 hours ago
Next Post
Ana Ci Gaba Da Alhinin Mutuwar Malam Adamu Fika

Ana Ci Gaba Da Alhinin Mutuwar Malam Adamu Fika

LABARAI MASU NASABA

Gwamnan Zamfara Ya Raba Buhunan Taki 59,205 Ga Manoman Jihar

Gwamnan Zamfara Ya Raba Buhunan Taki 59,205 Ga Manoman Jihar

July 11, 2025
Matatun Man Fetur Na Nijeriya Ba Za Su Ci Gaba Da Aiki Yadda Ya Kamata Ba – Dangote

Matatun Man Fetur Na Nijeriya Ba Za Su Ci Gaba Da Aiki Yadda Ya Kamata Ba – Dangote

July 11, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga Tare Da Kwato Makamai A Jihar Filato

‘Yan Bindiga Sun Kai Wa ‘Yansanda Hari Tare Da Kashe Wani Mutum Da Raunata Wani A Nasarawa

July 11, 2025
Goron Sallah

GORON JUMA’A

July 11, 2025
An Koka Kan Yadda Tsafi Da Jariran Da Aka Haifa Da Tsagaggen Lebe Ke Karuwa

An Koka Kan Yadda Tsafi Da Jariran Da Aka Haifa Da Tsagaggen Lebe Ke Karuwa

July 11, 2025
Bafarawa Ya Kaddamar Da Kungiyar Hada Kan Arewa Da Samar Da Zaman lafiya A Kaduna 

Bafarawa Ya Kaddamar Da Kungiyar Hada Kan Arewa Da Samar Da Zaman lafiya A Kaduna 

July 11, 2025
Hadarin Da Ke Kunshe Da Jin Bangare Daya Na Labari

Hadarin Da Ke Kunshe Da Jin Bangare Daya Na Labari

July 11, 2025
NPA Ta Yi Wa Ma’aikatanta 1,500 Karin Girma

NPA Ta Yi Wa Ma’aikatanta 1,500 Karin Girma

July 11, 2025
Shirin Sabunta Fata Na Tinubu Yana Samar da Damarmakin Cigaba — Minista

Shirin Sabunta Fata Na Tinubu Yana Samar da Damarmakin Cigaba — Minista

July 11, 2025
NPA Ta Tarbi Babban Jirgin ‘Ruwa MB Ocean Dragon’ Don Bunkasa Ayyukanta

NPA Ta Tarbi Babban Jirgin ‘Ruwa MB Ocean Dragon’ Don Bunkasa Ayyukanta

July 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.