ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jega Ya Warware Zare Da Abawa Kan Hanyoyin Tsaftace Zaben Nijeriya

by Sadiq
3 years ago
Jega

Tsohon shugaban hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC), Farfesa Attahiru Jega ya bayyana wasu hanyoyin tsaftace zaben NMijeriya cikin sauki.

Jega ya bayyana hanyoyin ne a lokacin da yake gabatar da jawabi a wurin wani taron kwanaki biyu da ya gudana a Jihar Akwa Ibom.

  • Gwamnatin Tarayya Ta Kara Karbo Bashin Dala Biliyan 3.45 Daga Bankin Duniya
  • Shin Wasan Kwaikwayon Na Zaben Kakakin Majalisar Wakilan Amurka Ta Kawo Karshe Ne? 

Ya ce matukar ana bukatar a tsaftace zaben Nijeriya, to dole ne ya kasance ba shugaban kasa ba ne yake nada shugabannin hukumar INEC.

ADVERTISEMENT

Tsohon shugaban INEC ya yi kira da a yi wa dokar zabe na 2022 garanbawul.

A cewarsa, duk da cewa dokokin zaben Nijeriya na yanzu za a iya cewa su ne mafi kyau a tarihin kasar nan, amma ba su zama cikakku ba, akwai bukatar a kara yin wasu gyare-gyare domin kawar da rudani da fayyafe abubu yadda suke da kuma karfafa wasu bangarorin dokokin.

LABARAI MASU NASABA

2027: Rashin Hadin Kan Atiku Da Obi Da Kwankwaso Na Iya Taimaka Wa Tazarcen Tinubu

Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya Sun Shiga Rudani A Yayin Da Wa’adin Mika Sunayen Mambobi Ya Shude

Ya ce gyare-gyaren su kasance sun tilasta saka sakamakon zabe ta na’ura a zabe mai zuwa na 2027.

Game da shugabancin hukumar INEC, Jega ya jadda cewa kamata ya yi a cire hannun shugaban kasa wajen ikon nada shugaban INEC da kwamishinonin zabe, domin a ceto hukumar daga nuna bangaranci ko bambanci ko kuma taimaka wa wasu.

Ya kara da cewa ya kamata a sake duba dokokin zabe domin tabbatar da cewa an warware duk matsalolin da suka taso wajen gudanar da zabe da yanke hukunci kafin ranar rantsarwa.

Masu ruwa da tsaki da dama sun bayyana damuwarsu kan sashi na 64 na dokar zabe, wanda ya bayyana tsarin yadda za a bayyana sakamakon zabe, inda cikin sauki za a iya yin magudi da kuma kawo rudani.

Jega ya ce ya kamata a fayyace wannan sashe ta tilasta saka sakamakon zabe ta na’ura tun daga rumfunan zabe da har izuwa cibiyoyin tattara sakamakon zabe daban-daban a fadin kasar nan.

“INEC za ta sami isasshen lokacin da za ta shirya domin wannan lamari, idan an yi wa dokar kwaskwarima da wuri kafin zaben da ke tafe, in ji shi.

Haka kuma, Jega ya yi kira ko dai a bullo da wani tsari da zai bayar da damar fara yin zabe da wuri ga ma’aikatan INEC, masu sa ido da direbobinsu da ‘yan jarida, ko kuma wani tsari na musamman da zai ba su damar yin kada kuri’a a ranar zabe, musamman ma a lokacin zaben shugaban kasa.

Tsohon shugaban INEC ya bayar da shawarar barin ‘yan Nijeriya da ke kasashen waje su kada kuri’unsu a kalla zaben shugaban kasa, domin ba su damar yin zabe, musamman wadanda suke aiki a kasashen ketare.

Ya ce akwai bukatar bai wa mata damar tsayawa takara a kowacce jam’iyya na kashi 35, tun daga mukamin shugaban kasa, gwamnoni, ‘yan majalsa, shugaban kananan hukumomi da kansiloli.

haka zalika, ya ce ya kamata a bai wa INEC ikon gudanar da zaben cike gibi da zarar an samu hakan.

A halin da ake ciki kuma, Farfesa Attahiru Jega, ya musanta cewa an yi magudi a zaben 2023.

Wasu rahotanni sun bayyana cewa Jega ya ce an yi magudi a zaben 2023, a wani taro na kwanaki biyu da majalisar dattawa ta shirya a Ikot Ipene na Jihar Akwa Ibom.

“Mun ga a zabukan 2023, illar kawai yadda masu rike da madafun ikon ke samun damar nada makusantarsu a cikin hukumar zabe domin su taimaka musu wajen lashe zabe,” in ji shi.

Sai dai a wata sanarwa da ta fito daga hannun babban mataimakinsa, Princess Hamman-Obels, Jega ya ce rahotannin da suka bayyana cewa ya ce an tafka magudi a zaben 2023 ba daidai ba ne kuma ba su dace da matsayinsa ba.

Sanarwar ta kara da cewa, “Hankalin Farfesa Attahiru Jega ya karkata ne ga wani rahoto na yaudara da aka buga a jaridu da dama na intanet, inda ya ce an yi magudi a zaben 2023.

“Rahoton da aka yi ba daidai ba ne kuma ba dace da matsayin Farfesa Jega ba, lallai ya musanta yin wannan kalamai game da zaben 2023.”

MASU ALAKA

Jega
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Rashin Hadin Kan Atiku Da Obi Da Kwankwaso Na Iya Taimaka Wa Tazarcen Tinubu

May 16, 2026
Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya Sun Shiga Rudani A Yayin Da Wa’adin Mika Sunayen Mambobi Ya Shude

May 15, 2026
Abincin Da Ya Kamata Ku Ci Lokacin Al’ada
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Hadakar ‘Yan Adawa Ta Rushe Yayin Da Tikitin Takarar Shugaban Kasa Ya Raba Kan Shugabannin ADC

May 9, 2026
Next Post
Duk Da Narka Fiye Da Biliyan 200, Gwamnati Ta Yi Gum A Kan Kidaya

Duk Da Narka Fiye Da Biliyan 200, Gwamnati Ta Yi Gum A Kan Kidaya

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.