• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dumamar Yanayi Ta Haddasa Ruwan Saman Ba-zata A Arewa – NiMet

by Bello Hamza and Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Labarai
0
Dumamar Yanayi Ta Haddasa Ruwan Saman Ba-zata A Arewa – NiMet
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

Hukumar Kula da Yanayi ta Nijeriya (NiMet) ta bayyana cewa sakamakon dumamar yanayi ne ta haddasa ruwan sama a wasu sassan arewacin Nijeriya a karshen makon da ya gabata zuwa farkon makon nan.

A cewarta, wannan na kara tabbatar da irin illar da gurbacewar sararin samaniya ke haifarwa, kuma ya zama dole a hada hannun wajen rage dumamar yanayi ta hanyar rage yadda iskar ‘carbon diodide’ ke gurbata muhalli.

  • Xi Ya Bukaci A Tsagaita Bude Wuta Tare Da Gudanar Da Tattaunawar Zaman Lafiya Kan Rikicin Falasdinu Da Isra’ila
  • Al’ummun Amurka Sun Yi Kira Ga Kyautata Dangantaka Tsakanin Sin Da Amurka

Hukumar ta bayyana hakan ne a wajen wani taron kara wa juna sani da ta shirya wa ‘yan jarida tare da hadin gwiwar Majalisar Dinkin Duniy na, wajen tunatar da ‘yan jarida kan dumamar yanayi ta yadda za su fadakar da al’ummar kasar nan.

Taron ya gudana ne a Otel din Rock Biew da ke Abuja, inda ta ce wannan wani sharar fage ne kan babban taron da aka fara a kasar Dubai daga ranar 30 ga Nuwamba zuwa 12 ga Disamba.

Hukumar NiMet ta yi nemi ‘yan jarida su kara kaimin fadakar da al’ummar Nijeriya kan illar dumamar yanayi a bangaren lafiya da tattalin arziki da kuma yadda za a magance matsalolin ta hanyar da ta dace.

A cewarta, ta dauki nauyin bayar da horo ga ‘yan jarida ne kan dumamar yanayi, saboda ayyukan ‘yan jarida ba zai iya misultuwa ba wajen fadakar da al’umma illarsa da kuma hanyoyin magance lamari.

Da yake jawabi a wurin taron, wakilin Majalisar Dinkin Duniya a Nijeriya Mattias Schmale, ya ce dukkan kasashen duniya na fama da matsalar dumamar yanayi, amma kasashen da suka ci gaba sun dauki matakin rage matsalolin wanda hakan ya sa suke kokarin bayar da tallafi ga kasashe masu tasowa irinsu Nijeriya, domin a gudu tare a tsira tare.

Ya ce kididdiga ta nuna cewa kasashen Nahiyar Afirka su suka fi fuskantar barazanar kamuwa da illolin dumamar yanayi, wanda hakan  ya sa Majalisar Dinkin Duniya ta mayar da hankali wajen taimaka musu.

Wakilin ya kara da cewa a 2023, an samu sauye-sauyen canjin yanayi ba ma a Nijeriya ba har da duniya baki daya, wanda akwai bukatar hada kannu da karfe wajen taimaka wa kasashe domin a tsira daga illar lamarin.

A tattaunawarsa da manema labarai, wakilin Kungiyar Masu Kula da Yanayi ta Duniya (WMO) a yankin yammaci da Afirika ta tsakiya, Mista Biyarnada Edward Gomez, ya bayyana cewa, an shirya taron ne don zaburar da ‘yan jarida da dukkan masu ruwa da tsaki wajen tattaunawa tare da bayar da rahotannin da suka shafi dumamar yanayi da yadda take addabar al’ummar sassan duniya da kuma irin gudunmwar da kowa zai bayar don rage irin matsalolin da ake fuskanta.

Ya ce, wannan yana da muhimmanci musamman da yake ana gudanar da babban taron ne da majalisar Dinkin Duniya ta shirya a kan dumamar yanayi a Hadaddiyar Daular Larabawa, taron shi ne na 28 tun da aka fara gabatarwa duk shekara.

“Muna zama ne a kan dumamar yanayi. Ana yin zaman saboda dumamar yanayi na addabar kowa a duniya. Kowa da kowa. Daga Nijeriya zuwa nahiyar Turai da Asiya da Amurka. Kuma babban abin da yake haddasa dumamar yanayi shi sinadarin CO2 din da suke fita wanda ni da kai duk muna taimakawa wajen gurbata muhalli. Idan kana tukin mota, motarka tana shan mai. Mai kuma yana fitar da sinadarin ‘Carbon Diodide’ cikin sararin samaniya idan kana amfani da ‘Air conditioner’ shi ma yana fitar da iskar. idan ka kunna wutar lantarki shi ma yana fitar da gurbatacciyar iska. Toh dukkanmu muna taimakawa wajen fitar da shi. Amma akwai kasashen da suka fi yi fiye da wasu, kasashen da suke da manyan kamfanoni, sun fi haifar da dumamar yanayi fiye da kananan kasashe”.

Mr Gomez ya kuma kara da cewa, “Dumamar yanayi na faruwa, me za mu yi a kai? Dole mu nemo hanyoyin da za mu saba. Misali, idan ana samun ruwa sosai da yake janyo ambaliya me za mu yi? Dole mu nemo hanyar da za mu saba. Ko kuma dalilin wannan zaman shi ne domin zaburar da ‘yan jarida domin su samu karfin gwiwa da ra’ayi a kan wadannan labarun, za su iya rubuta labarai a kan abubuwan da ke faruwa kuma su taimaka wajen sabawa da kuma shirya wa manyan dumamar yanayi, kuma muna kira gare ku ‘yan jarida ku sa ra’ayinku a kai, saboda wannan zai shafe ka kuma zai shafe shi kuma zai shafe ni, ya shafi dukkan al’umma.

Ya kara da cewa, “lallai mun yi sa’a, Nijeriya ba ma cikin manyan garuruwan da illolin dumamar yanayi yake shafa, idan ka samu kanka a garin da ake ambaliya sosai za ka iya rasa rayuwarka, zan iya rasa rayuwata. Saboda haka dukkanmu ya kamata mu maida hankali a kan abin da yake tafiya kuma mu fitar da labarun da za su tsawatar wa mutane don su dauki mataki a kan lokaci. Kuma a shirye muke mu ci gaba da ba ku wasu labarai da suka shafi dumamar yanayi don watsawa ga al’ummar yankunan karkara.”

Taron ya samu halartar masana daga cibiyoyin bincike, malaman jami’o’i da ‘yan jarida daga kafafen watsa labarai na jihohin Nijeriya da babban birnin tarayya Abuja.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Shari’ar Zaben Gwamnoni: Kallo Ya Koma Kotun Koli

Next Post

Allah Ya Girmama Annabi (SAW) Cikin Fadi Da Aikatawa

Related

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya
Manyan Labarai

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

3 hours ago
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC
Labarai

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

6 hours ago
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi
Labarai

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

6 hours ago
Daurarru
Labarai

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

16 hours ago
Wutar lantarki
Labarai

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

18 hours ago
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka
Labarai

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

19 hours ago
Next Post
Allah Ya Girmama Annabi (SAW) Cikin Fadi Da Aikatawa

Allah Ya Girmama Annabi (SAW) Cikin Fadi Da Aikatawa

LABARAI MASU NASABA

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.