ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yansanda Sun Cafke Wani Matashi Ɗan Shekara 15 Da Ake Zargi Da Yin Fashi Da Makami A Gombe

by Sulaiman
9 months ago
Gombe

Rundunar ‘yansandan jihar Gombe a ranar Laraba ta cafke wani yaro dan shekara 15 mai suna Abubakar Aliyu da ke unguwar Tudun Wada Shamaki, bisa zarginsa da aikata laifukan fashi da makami da kuma sata a unguwar Federal Low-Cost da ke cikin birnin Gombe.

 

Wanda ake zargin, a cewar rundunar ‘yansanda, an kama shi ne biyo bayan wani binciken gaggawa da aka gudanar bayan wani korafin fashi da aka kai a ranar 15 ga Oktoba, 2025.

ADVERTISEMENT
  • Gwamna Uba Sani Ya Rantsar Da Sabon Kwamishinan Yada Labarai Ahmed Maiyaki 
  • Kasar Sin Ta Sake Farfado Da Muhimman Koguna Da Tafkuna 88 A Kokarin Inganta Muhalli

Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yansandan jihar, DSP Buhari Abdullahi, wanda ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar, ya ce kamen ya kai ga kwato wasu muhimman kayayyaki da suka hada da iPhone 13 Pro Max, kwamfuta Laptop ta (Apple MacBook), agogo na (Apple), ‘power bank na Oraimo’, da jakar makaranta.

 

LABARAI MASU NASABA

Kungiya Ta Nemi Mambobinta Su Rungumi Hanyoyin Kasuwanci Na Zamani

Sojoji Sun Kamata Ƴan Bindiga 5 Da Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane A Yobe

A cewar sanarwar, “A ranar 15 ga Oktoba, 2025, da misalin karfe 11:00 na rana, wata mata da ke zaune a unguwar Federal Low-Cost, Gombe, ta bayyana cewa a daidai wannan ranar da misalin karfe 2:30 na dare, wani wanda ba ta san ko wanene ba, dauke da wuka ya kai mata hari, inda ya sace mata kayanta.

 

“Abubuwan da aka sace, sun haɗa da iphone 13 Pro Max, an kimanta kudinta akan ₦800,000, kwamfutar ‘Apple MacBook’ da darajarta ta kai ₦250,000, da agogon ‘Apple’ da darajarsa ta kai ₦35,000, ‘power bank’ na Oraimo wanda darajarsa ta kai ₦30,000, da jakar makaranta akan darajar ₦25,000.”

 

Abdullahi ya ce, nan take jami’an ‘yansanda na shiyyar suka dauki matakin kama wanda ake zargin tare da kwato dukkan kayayyakin da aka sace.

Gombe
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Kungiya Ta Nemi Mambobinta Su Rungumi Hanyoyin Kasuwanci Na Zamani
  • Sulaiman
    An Karrama Masana Ilimin Lissafi Na Kasar Sin Da Lambobin Yabo Na Fields Medal
  • Sulaiman
    Ta Da Zaune Tsaye Da Philippines Ta Yi A Teku Ba Zai Lalata Dangantakar Hadin Gwiwar Sin Da ASEAN Ba
  • Sulaiman
    An Zartas Da Sanarwar Chengdu A Taron Ministocin Kungiyar APEC Kan Harkar Raya Fasahohin Dijital Da AI

MASU ALAKA

Kungiya Ta Nemi Mambobinta Su Rungumi Hanyoyin Kasuwanci Na Zamani
Labarai

Kungiya Ta Nemi Mambobinta Su Rungumi Hanyoyin Kasuwanci Na Zamani

July 25, 2026
Gombe
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kamata Ƴan Bindiga 5 Da Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane A Yobe

July 25, 2026
Gombe
Labarai

Ku Buɗe Wuta Kan Duk Wanda Kuka Gani Ɗauke Da Bindiga – IGP

July 25, 2026
Next Post
Yawan Hada-hadar Kudaden Kasashen Waje Na Kasar Sin A Farkon Rabu’i Na Uku Na Bana Ya Zarce Dala Triliyan 11

Yawan Hada-hadar Kudaden Kasashen Waje Na Kasar Sin A Farkon Rabu’i Na Uku Na Bana Ya Zarce Dala Triliyan 11

LABARAI MASU NASABA

Kalolin Kitso Na Zamani: Yadda Ake Yin Fulani Style

Muhimmancin Kula Da Gashi Domin Lafiyarsa Da Kyawunsa

July 25, 2026
Kungiya Ta Nemi Mambobinta Su Rungumi Hanyoyin Kasuwanci Na Zamani

Kungiya Ta Nemi Mambobinta Su Rungumi Hanyoyin Kasuwanci Na Zamani

July 25, 2026
Amfanin Ganyen Magarya Ga Lafiya Dan Adam

Amfanin Ganyen Magarya Ga Lafiya Dan Adam

July 25, 2026
Wane Ne Khalil Al-Hayya, Sabon Shugaban Kungiyar Hamas?

Wane Ne Khalil Al-Hayya, Sabon Shugaban Kungiyar Hamas?

July 25, 2026
Tsakanin Digiri Da Sana’a Wanne Ya Fi Muhimmanci A Wannan Lokacin?

Tsakanin Digiri Da Sana’a Wanne Ya Fi Muhimmanci A Wannan Lokacin?

July 25, 2026
Gombe

Sojoji Sun Kamata Ƴan Bindiga 5 Da Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane A Yobe

July 25, 2026
Gwamnatin Jihar Kano Za Ta Fara Aiwatar Da Shirin Inshorar Lafiya Ga Jaruman Kannywood

Gwamnatin Jihar Kano Za Ta Fara Aiwatar Da Shirin Inshorar Lafiya Ga Jaruman Kannywood

July 25, 2026
Gombe

Ku Buɗe Wuta Kan Duk Wanda Kuka Gani Ɗauke Da Bindiga – IGP

July 25, 2026
Idan Aka Cire Bangaren Man Fetur Kannywood Ce Ta Fi Samar Da Aikin Yi Ga Matasa —Hamisu Iyantama

Idan Aka Cire Bangaren Man Fetur Kannywood Ce Ta Fi Samar Da Aikin Yi Ga Matasa —Hamisu Iyantama

July 25, 2026
Kogin Kumadugu Ya Yi Ambaliya Karon Farko Cikin Shekara 100 A Yobe

Jihohi 28 Da Abuja Na Fuskantar Hadarin Ambaliyar Ruwa —Rahoto

July 25, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.