• English
  • Business News
Wednesday, November 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Duniya Za Ta More Manyan Damammaki Uku Daga Kasar Sin Mai Bude Kofarta Ga Kasashen Waje

by CMG Hausa
3 years ago
Kasar Sin

A daren ranar Jumma’a 4 ga wata ne, shugaban kasar Sin Xi Jinping, ta kafar bidiyo, ya halarci bikin kaddamar da baje-kolin kayayyakin kasa da kasa da ake shigowa da su kasar Sin ko kuma CIIE karo na biyar wanda ake yi a birnin Shanghai, inda ya yi jawabin dake jaddada cewa, kasarsa za ta taimakawa kasa da kasa, more damammakin ci gaba tare.

Xi ya ce, “Ya dace mu kara bude kofarmu, don daidaita matsalolin ci gaba, da fadada hadin-gwiwa, da kara karfin yin kirkire-kirkire, da kuma samar da ci gaba tare, ta yadda za’a kara dunkule tattalin arzikin duniya baki daya, da samar da ci gaba ga kasa da kasa, don kara amfanar al’ummominsu cikin adalci”.

  • Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Samar Da Fa’ida A Zahiri Ga Jama’ar Afirka

A shekaru biyar da suka wuce, shugaba Xi ya sanar da gudanar da bikin CIIE, da zummar fadada bude kofar kasar Sin, ta yadda babbar kasuwar kasar za ta zama babban zarafi ga duk duniya baki daya.

Kididdigar ta nuna cewa, a wajen bukukuwan CIIE hudu da suka gabata, adadin kayayyakin da aka baje kolinsu, sun kai dubu 270, kuma jimillar darajar yarjeniyoyin da aka daddale ta zarce dala biliyan 270, inda aka bullo da sabbin hajoji, da fasahohi, da hidimomi da yawansu ya wuce 1500.

Bikin CIIE, tamkar dandali ne ga kasar Sin, na kafa sabon tsarin samar da ci gaba, da fadada bude kofarta ga kasashen ketare, inda sassan kasa da kasa za su ci gajiya tare.

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Kaddamar Da Kwas Din Horon Fasahar Gwaje-Gwaje A Cibiyar CDC Ta Afrika

‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Za Su Dawo Doron Kasa A Gobe Laraba

Baje kolin CIIE na bana, kasaitaccen bikin kasa da kasa ne na farko da kasar Sin ta gudanar, tun bayan da ta kira babban taron wakilan jam’iyyar kwaminis karo na 20, wanda ya samu halartar kasashe da yankuna, da kungiyoyin kasa da kasa 145, gami da kamfanoni 284 dake sahun gaba a duniya.

Rahoton babban taron wakilan jam’iyyar kwaminis karo na 20 ya jaddada cewa, kasar Sin za ta nace ga bin manufar bude kofarta ga kasashen waje, tare da cin moriya tare da kasashe daban-daban, ta yadda duniya za ta amfani sabon ci gaban kasar Sin.

A jawabin shugaba Xi, ya sake nanata cewa, kasarsa za ta taimakawa kasashe da bangarori daban-daban, ta yadda za su more damamakin da suka shafi babbar kasuwar kasar, da manufar bude kofa ga kasashen waje, da habaka hadin-gwiwa tsakanin kasa da kasa.

Manazarta na ganin cewa, damammakin uku, za su sanya babban kuzari ga tattalin arzikin duniya, wanda a yanzu haka yake murmurewa daga mawuyacin hali. (Murtala Zhang)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sin Ta Kaddamar Da Kwas Din Horon Fasahar Gwaje-Gwaje A Cibiyar CDC Ta Afrika
Daga Birnin Sin

Sin Ta Kaddamar Da Kwas Din Horon Fasahar Gwaje-Gwaje A Cibiyar CDC Ta Afrika

November 4, 2025
‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Za Su Dawo Doron Kasa A Gobe Laraba
Daga Birnin Sin

‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Za Su Dawo Doron Kasa A Gobe Laraba

November 4, 2025
Sin Na Goyon Bayan Najeriya Wajen Jagorantar Al’ummarta Zuwa Hawa Turbar Neman Ci Gaba Daidai Da Yanayin Kasar
Daga Birnin Sin

Sin Na Goyon Bayan Najeriya Wajen Jagorantar Al’ummarta Zuwa Hawa Turbar Neman Ci Gaba Daidai Da Yanayin Kasar

November 4, 2025
Next Post
Shugabannin Sin Da Madagascar Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafuwar Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Su

Shugabannin Sin Da Madagascar Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafuwar Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Su

LABARAI MASU NASABA

Sanata Barau Ya Tsaya Takarar Shugaban Majalisar Dattawa

Ba Na Jin Tsoron Trump – Martanin Sanata Barau Ga Akpabio

November 5, 2025
Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da BoS Ta Kaduna Sun Ƙulla Yarjejeniyar Samar Da Sahihan Bayanai Ga Al’umma

Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da BoS Ta Kaduna Sun Ƙulla Yarjejeniyar Samar Da Sahihan Bayanai Ga Al’umma

November 4, 2025
Sin Ta Kaddamar Da Kwas Din Horon Fasahar Gwaje-Gwaje A Cibiyar CDC Ta Afrika

Sin Ta Kaddamar Da Kwas Din Horon Fasahar Gwaje-Gwaje A Cibiyar CDC Ta Afrika

November 4, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

‘Yansanda Sun Ceto Mutane 3 Da Aka Sace A Kwara

November 4, 2025
‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Za Su Dawo Doron Kasa A Gobe Laraba

‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Za Su Dawo Doron Kasa A Gobe Laraba

November 4, 2025
tinubu

Tinubu Ya Umarci Ma’aikatar Ilimi Ta Kawo Ƙarshen Yajin Aikin ASUU

November 4, 2025
Sin Na Goyon Bayan Najeriya Wajen Jagorantar Al’ummarta Zuwa Hawa Turbar Neman Ci Gaba Daidai Da Yanayin Kasar

Sin Na Goyon Bayan Najeriya Wajen Jagorantar Al’ummarta Zuwa Hawa Turbar Neman Ci Gaba Daidai Da Yanayin Kasar

November 4, 2025
2027: Ko Kano Ta Zauna Lafiya Ko Ta Hautsine, Sai Mun Sauke Gwamna Abba — Shugaban APC

2027: Ko Kano Ta Zauna Lafiya Ko Ta Hautsine, Sai Mun Sauke Gwamna Abba — Shugaban APC

November 4, 2025
Li Qiang Ya Zanta Da Kakakin Majalisar Wakilan Najeriya

Li Qiang Ya Zanta Da Kakakin Majalisar Wakilan Najeriya

November 4, 2025
Karancin Abinci: Kofar Ofishin Tinubu A Rufe Take, Har Wasu Ministoci Ba Su Iya Ganinsa – Ndume 

Zargin Kisan Kiyashi Ga Kiristoci: Trump Bai San Ƙalubalen Tsaron Da Najeriya Ke Ciki Ba — Ndume

November 4, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.