ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, November 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

EFCC Da NIS Za Su Yi Hadin Guiwa Kan Yaki Da Cin Hanci

by Khalid Idris Doya
3 years ago
efcc

Shugaban hukumar yaki da karya tattalin arzikin kasa da cin hanci da rashawa a Nijeriya (EFCC), Abdulrasheed Bawa ya yi kiran kara inganta alakar aiki a tsakanin hukumarsa da hukumar kula da shige da fice ta Nijeriya (NIS) wajen yaki da masu aikata lmzagon kasa ga tattalin arzikin kasa da dangogin laifukan rashawa a Nijeriya.

 

  • Zaɓen Fidda Gwani Na APC: An Kashe Biliyan 2 Da Miliyan 750 Wajen Sayen Kuri’a A Katsina —NNPP

Wannan bayanin na kunshe a cikin wata sanarwar da jami’in watsa labarai na hukumar lura da shige da fice, ACI Amos Okpu ya sanya wa hannu.

ADVERTISEMENT

Sanarwar ta nakalto cewa Shugaban hukumar EFCC ya yi wannan kiran ne a lokacin da suke ganawa da Kwanturola Janar nahukumar kula da shige da fice ta kasa Isah Jere a ranar Alhamis.

EFCC

LABARAI MASU NASABA

Farashin Kayan Abinci Na Cigaba Da Sauka A Jihohin Arewa Maso Gabas

Hauhawar Farashin Kayayyaki A Nijeriya Ta Ragu Zuwa Kashi 16.065%

A cewar sanarwar, Bawa “Ya zo shalkwatar hukumar ne domin neman karin goyon baya da hadin kai wajen yaki da dukkanin nau’ikan laifukan da suka shafi aikata rashawa da zagon kasa ga tattalin arzikin kasa a ciki da wajen kasar nan musamman ta kan iyakokin kasarmu”.

Ya ce, NIS tana sahun gaba a cikin hukumomin da suke yaki da harkallar rashawa don haka ne ya nemi hukumar da ta kara amfani da dabarun aikinta da amfani da na’urar zamani ta ICT wajen taimakon hukumarsa don kara bunkasa yaki da cin hanci da rashawa.

Abdulrasheed ya kuma sake yin kira na neman hadin kan hukumar a bangaren bibiya da kama wadanda ke kokarin ficewa da kudin da suka mallaka ta hanyar cin hanci da rashawa, sai ya nemi karin goyon baya kan hakan.

Da ya ke maida jawabi, Kwanturola Janar na hukumar kula da harkokin shige da fice (NIS), Isah Jere, ya ba da tabbacin hukumar na yin aikin hadin guiwa da dukkanin hukumomin da suka dace wajen kokarin kare tattalin arzikin kasar nan.

EFCC

Isah ya ce a matsayinsa na shugaban hukumar shige da fice, hukumar ta samar da na’urorin zamani da ke taimaka musu wajen tabbatar da cewa duk wani da ake zargi ko aka hana shi fita bai samu damar fita daga cikin kasar nan ta iyakokin kasar ba har sai an tantance tare da amincewa da fita ko shigarsa.

“Muna da na’urorin da kai tsaye cikin ‘yan dakika za su ba mu bayanan tarihi da motsin mutanen da ke son shiga ko fita a iyakokin kasarmu, don haka cikin sauki za mu hana mutumin da ke da wani tabon da ka iya hana shi fita ko shiga damar yin hakan”.

  • https://efcc-grills-venezuelan-4-nigerians-over-oil-theft/

 

Ya nemi a dauwamar da aikin hadin guiwa tsakanin NIS da EFCC domin samun nasarar da aka sanya a gaba a kowani lokaci.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Farashin Kayan Abinci Na Cigaba Da Sauka A Jihohin Arewa Maso Gabas
Labarai

Farashin Kayan Abinci Na Cigaba Da Sauka A Jihohin Arewa Maso Gabas

November 17, 2025
NBS
Labarai

Hauhawar Farashin Kayayyaki A Nijeriya Ta Ragu Zuwa Kashi 16.065%

November 17, 2025
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 
Labarai

‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

November 17, 2025
Next Post
Kotu Ta Umarci Wani Ma’aikacin Gwamanti Da Ya Dawo Da Albashinsa Na Shekara 11 A Filato

Kotu Ta Umarci Wani Ma'aikacin Gwamanti Da Ya Dawo Da Albashinsa Na Shekara 11 A Filato

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Sin Ba Ta Taba Bukatar Kamfanoni Su Tattara Ko Adana Bayanai Ba Bisa Ka’ida Ba Kuma Ba Za Ta Yi Hakan Ba 

Gwamnatin Sin Ba Ta Taba Bukatar Kamfanoni Su Tattara Ko Adana Bayanai Ba Bisa Ka’ida Ba Kuma Ba Za Ta Yi Hakan Ba 

November 17, 2025
Adadin Motocin Da Sin Ke Fitarwa Waje Ya Karu Da Kashi 15.7 Cikin Watanni 10 Na Farkon Bana

Adadin Motocin Da Sin Ke Fitarwa Waje Ya Karu Da Kashi 15.7 Cikin Watanni 10 Na Farkon Bana

November 17, 2025
Farashin Kayan Abinci Na Cigaba Da Sauka A Jihohin Arewa Maso Gabas

Farashin Kayan Abinci Na Cigaba Da Sauka A Jihohin Arewa Maso Gabas

November 17, 2025
An Bude Taron Tattaunawa Kan Wayewar Kai Tsakanin Sin Da Kasashen Larabawa Karo Na 11 A Beijing

An Bude Taron Tattaunawa Kan Wayewar Kai Tsakanin Sin Da Kasashen Larabawa Karo Na 11 A Beijing

November 17, 2025
NBS

Hauhawar Farashin Kayayyaki A Nijeriya Ta Ragu Zuwa Kashi 16.065%

November 17, 2025
Firaministan Sin Ya Isa Rasha Domin Halartar Taron SCO

Firaministan Sin Ya Isa Rasha Domin Halartar Taron SCO

November 17, 2025
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

November 17, 2025
Kudaden Kasafin Kudin Sin Sun Karu Da Kashi 0.8 Cikin Watanni 10 Na Farkon Bana

Kudaden Kasafin Kudin Sin Sun Karu Da Kashi 0.8 Cikin Watanni 10 Na Farkon Bana

November 17, 2025
Rashin Tsaro: Atiku Ya Yi Allah-wadai Da Harin Makarantar ‘Yan Mata Ta Kebbi

Rashin Tsaro: Atiku Ya Yi Allah-wadai Da Harin Makarantar ‘Yan Mata Ta Kebbi

November 17, 2025
An Sanya Hannu Kan Yarjejeniyoyin Cinikayya Na Biliyoyin Kudi Yayin Baje Kolin CHTF Na Kasar Sin

An Sanya Hannu Kan Yarjejeniyoyin Cinikayya Na Biliyoyin Kudi Yayin Baje Kolin CHTF Na Kasar Sin

November 17, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.