ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zaɓen Fidda Gwani Na APC: An Kashe Biliyan 2 Da Miliyan 750 Wajen Sayen Kuri’a A Katsina —NNPP

by El-Zaharadeen Umar
4 years ago
Zaɓen

Jam’iyyar NNPP a jihar Katsina ta yi zargin yin amfani da kuɗi na fitar hankali wajan sayen kuri’un Daliget a zaɓen fidda gwani na fitar da dan takarar gwamnan APC da ya gabata.

Shugaban Jam’iyyar NNPP reshe  Jihar Katsina, Hon. Sani Liti, ya bayyana haka a lokacin taron manema labarai da aka yi a Katsina.

  • Jam’iyyar Labour Party Ba Za Ta Lashe Zaben 2023 Ba – Kwankwaso
  • Ko Kwankwaso Zai Iya Kai Bantensa?

Hon. Sani Liti ya ƙara da cewa kimanin naira na gugar naira biliyan biyu da miliyan ɗari bakwai da hamsin aka yi amfani da su wajan sayen kuri’un Daliget 1,805 a cikin rana ɗaya kawai.

ADVERTISEMENT

“Idan har gwamnatin bata ɗauki mataki akan wannan al’amari ba, to ba’a san inda wannan ƙasa zata faɗa ba a sakamakon muzanta darajar naira da gwamnati ta taimaka aka yi a Nijeriya” in ji shi

Sannan ya ƙara da cewa suna da duk wani bayani na iri kuɗaɗen da aka kashe wajan zaɓen fidda gwani na jam’iyyar APC wanda mutum tara suka tsaya takara. Sai dai ya ce cikekken bayani na nan tafe nan gaba.

LABARAI MASU NASABA

PRP Ta Musanta Zargin Cewa Kwankwaso Ya Sayi Fom 69 Domin Kwace Jam’iyyar

Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP

Haka kuma jam’iyyar NNPP ta yi koken cewa gwamnan babban bankin Nijeriya, Mista Godwin Emefele, ya faɗa siyasa wanda hakan ya ci karo da dokar ƙasa, ya ce ya kamata ya sauka daga aikinsa tun kafin lokaci ya kure masa.

Hon. Sani Liti ya ce ta inda za a tabbatar da wannan ikirari nasu shi ne, yadda shugaban baban bankin Nijeriya ya yi amfani da kuɗi naira miliyan 100 wajan fom ɗin takarar shugaban ƙasa a kakar zaɓen da ake ciki.

Jam’iyyar NNPP ta ce baya ga sayen fom da shugaban baban bankin Nijeriya ya yi, ya kuma sayi motoci 100 da zai yi amfani da su wajan yakin neman zaɓe kafin ya janye takararsa.

Hon. Sani Liti ya ce kasancewar, Godwin Emefele, ɗan wata jam’iyyar kawai ya haramta masa ci gaba da zama gwamnan baban bankin Nijeriya, ya ce idan kuma hakan bata samu ba, shugaban ƙasa da kansa ya kamata ya nuna halin girma da mutunci wajan sauke shi daga kujerarsa.

Kazalika jam’iyyar NNPP ta yi zargin cewa, Godwin Emefele, yana da hannu dumu-dumu wajan faɗuwar darajar naira a Nijeriya wanda ke neman kassara kasar ta fuskar tattalin arziki.

Zaɓen
El-Zaharadeen Umar
+ postsBio
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Mutum 1,000 Daga Jam’iyyar ADC Sun Koma PDP A Jihar Katsina
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Tinubu Ya Amince Da Ɗaukar Ma’aikatan Gandun Daji 1,000 Domin Matsalolin Tsaro A Katsina
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Matsalar Tsaro:Yadda Sabbin Matakan Gwamnati Ke Shafar Walwalar Al’ummar Jihar Katsina
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

MASU ALAKA

2023: Gwarazan Jam’iyyu A Karon Battar Zaben Shugaban Kasa
Siyasa

PRP Ta Musanta Zargin Cewa Kwankwaso Ya Sayi Fom 69 Domin Kwace Jam’iyyar

June 22, 2026
Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP
Siyasa

Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP

June 22, 2026
ADC Ta Sake Tabbatar Da Ibrahim Khalil A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano Na 2027
Siyasa

ADC Ta Sake Tabbatar Da Ibrahim Khalil A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano Na 2027

June 21, 2026
Next Post
Atiku Ya Nada Dino Melaye Da Daniel Bwala A Matsayin Masu Magana da Yawunsa

Atiku Ya Nada Dino Melaye Da Daniel Bwala A Matsayin Masu Magana da Yawunsa

LABARAI MASU NASABA

Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.