• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

EFCC, ICPC Sun Kwato Naira Biliyan 277.69 Da Dala Miliyan 106 A Shekara Guda

byKhalid Idris Doya and Sulaiman
10 months ago
EFCC

Hukumomi biyu da suke yaki da cin hanci da rashawa da dangoginsu wato EFCC da ICPC, sun samu nasarar kwato naira biliyan 277.685 da kuma kudin da yawansa ya kai dala miliyan 105,966 a cikin shekara daya.

Yayin da EFCC ta kwato rukunin gidaje 753, ita kuma ICPC ta bi diddingin ayyuka 1,500 a fadin kasar nan.

  • Gwamna Lawal Ya Rattaba Hannu Kan Kasafin Kudi Na Naira Biliyan 546 Na Shekarar 2025
  • Yadda Minista Ya Kaddamar Da Ginin Radio House Da Aka Yi Wa Kwaskwarima A Abuja

Kazalika, ICPC ta samu nasarar dakile ma’aikatu da sashi-sashi daga taba naira biliyan 10.8 na kudaden da ba a yi amfani da su ba.

Hukumomi biyun sun samu nasarar gurfanar da mutane 3,468 da laifuka daban-daban a cikin shekara guda.

Daraktan sashin shari’a na ofishin mashawarcin shugaban kasa kan harkokin tsaro (ONSA), Zakari Mijinyawa, shi ne ya shaida hakan a hirarsa da ‘yan jarida a Abuja jiya.

LABARAI MASU NASABA

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

Mijinyawa ya ce a halin yanzu tsofaffin gwamnoni hudu da tsofaffin ministoci uku su na kan fuskar shari’a a kotuna daban-daban. Sai dai bai bayyana sunayen su ba.

Ya misalta nasarorin hukumomin biyu a matsayin wata gagarumar ci gaba da kokarin gwamnati na yaki da cin hanci da rashawa a fadin kasar nan.

“A karkashin jagorancin babban shugaba, Ola Olukoyede, EFCC ta aiwatar da sauye-sauye masu gayar ma’ana, da suka hada da kafa sabuwar sashi-sashi na yaki da ‘yan damfara, farfado da ofisoshin shiyyoyi, da kuma kafa gidan rediyon EFCC 97.3FM domin wayar da kan jama’a.

‘’Hukumar ta amshi bakwancin babban taro kan laifukan yanar gizo da masu ruwa da tsaki ciki har da Shugaba Bola Ahmed Tinubu suka halarta.

“Hukumar ta sashin tawagar musamman dinta ta samu nasarar gurfanar da masu laifukan 35 da suka ci zarafin Naira.

‘’A duniyance, EFCC ta samu inganta hadaka da FBI da Canadian Royal Mounted Police, da kwato kadarorin da aka boye a kasashen waje.”

Ya ce gurfanar da tsofaffin gwamnoni da ministoci ciki har da tsohon gwamnan Babban Bankin Nijeriya (CBN), Godwin Emefiele, kan sama da fadi da duniyar al’umma da sauran laifuka ya nuna kokarin hukumar wajen wanzar da gaskiya da adalci.

Ya ce, “Nasarorin da ICPC ya cimma a 2024 abun alfahari ne. Hukumar ta kwato tsabar kudi na naira biliyan 29.685 da dala 966,900.83, da kuma kari kan dakile ma’aikatu da sashi-sashi daga taba naira biliyan 10.8 na kudaden da ba a yi amfani da su ba.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace
Labarai

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Tinubu
Manyan Labarai

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa
Labarai

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Next Post
Ganduje Ya Zargi Gwamna Yusuf Da Ɗaukar Nauyin Zanga-zanga A Kano

2027: ‘Yan Majalisan Adawa 18 Suka Sauya Sheka Zuwa Jam’iyyar APC

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version