ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Lawal Ya Rattaba Hannu Kan Kasafin Kudi Na Naira Biliyan 546 Na Shekarar 2025

by Sulaiman and Hussein Yero
2 years ago
Gwamna lawal

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal ya rattaba hannu kan ƙudirin kasafin kuɗin shekarar 2025 na Naira 546,014,575,000.00.

 

Kasafin kuɗin 2025 mai taken; “Kasafin Ceto 2.0”, kakakin majalisar dokokin jihar Zamfara ya gabatar wa gwamnan a ranar Alhamis a gidan gwamnatin jihar da ke Gusau.

ADVERTISEMENT
  • Dakarun MNJTF Sun Daƙile Harin Da Aka Kai Sansanin Su, Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 10 A Kamaru
  • Dubun Sojan Gona Ta Cika Bayan Damfarar Mutane A Jihar Yobe

A yayin rattaba hannu kan ƙudirin kasafin kuɗi na shekarar 2025, Gwamna Lawal ya ƙuduri aniyar kammala dukkan ayyukan da ake gudanarwa tare da inganta nasarorin da aka samu a cikin watanni 18 da gwamnatinsa ta yi.

 

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Gwamnan ya bayyana muhimmancin kasafin kuɗin shekarar 2025, inda ya ce ‘ba wai kawai mu kalli inda muke ko kuma inda muka dosa ba, amma inda muka kasance’.

 

“Abin ya tsananta a bara. Shekaru goma na rashin shugabanci nagari ya haifar da durƙushewar tattalin arziki, rashin biyan ma’aikatan gwamnati albashi, da kuma basussukan da ke kawo cikas ga ilimin yara. An lalata ababen more rayuwa, an yi watsi da asibitoci, kuma ayyukan jama’a sun ɗaiɗaita. Bugu da qari kuma, akwai rashin bin doka da oda, da batun kuɗin wutar lantarki da ake ci gaba da yi, da rashin isasshen ruwan sha, rashin tsaro, da ƙaruwar cututtuka masu yaɗuwa kamar kwalara, tare da raguwar kuɗaɗen shiga na cikin gida.

 

“Da ba mu yi gaggawar magance dukkan ƙalubalen ba, da jihar Zamfara ba za ta zama wurin da dukkan mu za mu iya rayuwa a yau ba.

 

“Ƙudirin Ceto na 2025 2.0 yana gudana ne ta hanyar jajircewarmu na ci gaba da ayyukan da muka fara wa mutanenmu, wanda ke nuna kyawawan manufofi na kishi. Wannan kasafin kuɗin kuma ya sanya aka ƙara wa ma’aikata ƙarin albashi mafi ƙaranci, inda ya tashi daga N30,000 zuwa N70,000.

 

Gwamna Lawal ya bayyana cewa lokaci ya yi da jihar Zamfara za ta shawo kan lalacewar ababen more rayuwa da kuma ƙoƙarin inganta gine-gine.

 

Kasafin kuɗin 2025 zai shafi gudanar da ayyukan filin jirgin sama na Gusau da kuma aikin gina hanyar Gusau-Magami zuwa Dansadau.

 

“Hakazalika, Kasafin 2025 zai shafi samar da kayan aikin tsaro ta hanyar ‘Asusun Tsaro’, gina makarantu ta hanyar shirin Agile, kafa cibiyar bincike ta zamani, gina birnin na zamani, samar da abinci a ƙarƙashin shirin Fadama III, sauƙin kasuwanci ta hanyar ‘Saber Program’, gyara Cibiyar Bafarawa Shinkafi, da gina Cibiyar Taro ta Duniya.

 

“Aikin gina titin Lalan zuwa Lalan, inganta asibitin ƙwararru na Yariman Bakura zuwa asibitin koyarwa, gina ƙarin gine-gine a manyan asibitocin Anka, Kauran namoda, Gummi, Shinkafi, Magami, Tsafe, Jangebe, da Bukkuyum, inganta wuraren kwanan ‘yan gudun hijira ta hanyar shirin Solid, haɓaka yawan amfani da dabbobi ta hanyar shirin L-Press, gina hanyar mai nisan kilomita 126 daga magami-dangulbi-dankurmi-bagega-anka.”

 

Sauran ayyukan da za a ƙaddamar a cikin kasafin kuɗin 2025 sun haɗa da shirin NG-Cares na ƙarfafa ci gaban al’umma, gina cibiyar wasanni ta Gusau, gina titin Mallamawa – Zarummai – Bukkuyyum, gina sabuwar makarantar koyon aikin jinya da ungozoma ta Zurmi, kammalawa Cibiyar Siyayya ta Gusau da ke tsohon wurin shaƙatawa, da kuma gina titin kilomita 94 a Yandoton Daji-Doka-Yanwaren-daji-Hayin alhaji-Bedi-Yankuzo-Tsafe.

Gwamna lawal
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Gwamna lawal
Hussein Yero
+ posts Bio
  • Hussein Yero
    https://hausa.leadership.ng/author/hussein-yero/
    Yaƙi Da Ta’addanci: Gwamnan Zamfara Ya Jinjina Wa Jami’an Tsaro Bisa Ƙwato Ɗarurruwan Shanu
  • Hussein Yero
    https://hausa.leadership.ng/author/hussein-yero/
    ’Yan Bindiga Sun Sace Dattawan Zamfara 50 Yayin Taron Sulhu A Cikin Daji
  • Hussein Yero
    https://hausa.leadership.ng/author/hussein-yero/
    Ɗan Takarar Sanata A Zamfara Ya Koka Kan Yi Wa Rayuwarsa Barazana
  • Hussein Yero
    https://hausa.leadership.ng/author/hussein-yero/
    Abdulaziz Yari Ya Bukaci Limamai Su Ƙara Addu’a Kan Yaƙi Da Ƴan Bindiga A Zamfara

MASU ALAKA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Next Post
Kasar Sin Na Adawa Da Danne Kamfanoninta Da Amurka Take Yi Bisa Fakewa Da Batun Tsaron Kasa

Kasar Sin Na Adawa Da Danne Kamfanoninta Da Amurka Take Yi Bisa Fakewa Da Batun Tsaron Kasa

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.