Daya daga cikin wadanda ake zargi da sayan kuri’un sun boye Atamfofi a wurin ajiye kaya na mota kira Peugeot 406.
Jami’an Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati, (EFCC), karkashin jagorancin Kwamandan EFCC, Aliyu Yusuf, a ranar 25 ga Fabrairu, 2023, sun kama wasu mutane biyu da ake zargi da sayan kuri’u a Gusau, Jihar Zamfara.
- Yadda Jami’an EFCC Suka Yi Dirar Mikiya A Rumfunan Zabe A Zamfara
- EFCC Ta Kama Wasu Masu Sayen Katin Zabe A Kano, Kaduna Da Abuja
Inda aka kama Mustapha Abubaka da kudi N107,000 (Naira Dubu Dari da Bakwai) da tikitin da aka kera na musamman domin masu kada kuri’a a matsayin shaida na zaben jam’iyyarsa, kafin karbar kudaden, an kama Isa Abdullahi da laifin sayan kuri’u tare da boye su a cikin boot da kujerar baya na Peugeot 406.
Wadanda ake zargin da kayayyakin da aka kwato suna hannun hukumar yayin da ake ci gaba da bincike.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp