• English
  • Business News
Saturday, August 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

EFCC Ta Sanya Tukwici Ga Masu Fallasa Waɗanda Ke Wulaƙanta Naira

by Khalid Idris Doya
1 year ago
in Labarai
0
EFCC Ta Sanya Tukwici Ga Masu Fallasa  Waɗanda Ke Wulaƙanta Naira
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A wani yunƙurin daƙile wulaƙanta Naira a wajen bukukuwa, hukumar yaƙi da masu yi wa tattalin arzikin ƙasa zagon ƙasa (EFCC) ta sanar da sanya tukwuicin kaso 5 cikin 100 ga duk wanda ya kawo mata labarin masu muzanta Naira har aka kai ga gurfanar da su.

Jami’in watsa labarai na EFCC, Dakta Dele Oyewale, shi ne ya shaida hakan a lokacin da yake ganawa da manema labarai a Abuja cikin makon nan.Oyewale ya jaddada aniyar hukumar na tabbatar da doka da kare martabar tattalin arziki daga masu cin zarafin Naira.

  • Tsohon Shugaban Hukumar EFCC, Ibrahim Lamorde Ya Rasu
  • Wata Sabuwa: EFCC Ta Buɗe Littafin Kwankwaso

Ya ce, kaso 5 na tukwuici an ware shi ne domin ƙarfafa gwiwar mutane da suke tona sirin masu cin zarafin Naira k6uma hakan zai taimaka wajen bayar da bayanai da za su kai ga cafkewa da gurfanar da masu cin zarafin Naira.

“Akwai tukwuici ga duk ani da ya kawo rahoton masu watsa Naira. Duk wanda ya tono asirin cin zarafin Naira zai samu kyautar kaso 5 cikin 100 na kuɗin da aka yi amfani da su wajen tafka ta’asar, amma muhimman bayanan da za su kai har a gurfanar da masu laifin ba wai bayanai na shaci faɗi ko ƙage ba,” Oyewale ya shelanta.

Ya ƙara da cewa EFCC ta gabatar da kusan mutum 50 a faɗin ƙasar nan tun lokacin da aka kafa sashin kar-ta kwana kan masu cin zarafin naira da dala.

Labarai Masu Nasaba

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

Kakakin na EFCC ya kuma tabbatar da cewa ƙin amincewa da naira a matsayin wata doka babban laifi ne, kuma duk wanda aka kama da laifin hakan zai fuskanci hukunci mai tsauri. Ya ce, hukumar tana yin ƙoƙarinta wajen ganin ta samar wa Naira kima a idon sauran ƙasashen waje domin kyautata tattalin arziki.

Oyewale ya ce, “Laifi ne ƙin amsar naira, watakila ko don ya yi datti ko don ba sabbi ba ne, laifi ne hakan babba. “Naira ne alamin tattalin arzikinmu. Ƙasarmu tana dai Cikakken ƴancinta kuma dole harkokin cinikayyarmu su tafi da Naira a Nijeriya, don haka ƙin amincewa da Naira laifi ne.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ₦CBNEFCCMoneyNaira
ShareTweetSendShare
Previous Post

A Tsame Masarautunmu Daga Siyasa

Next Post

Falalar Goman Farko Na Watan Fahimtar Sayyidina Umar (RA) Da Sayyidina Aliyu (RA) Kan Ramakon Ramadan A Goman Zulhajji

Related

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya
Labarai

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

7 hours ago
Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi
Labarai

Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

8 hours ago
JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa
Labarai

JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

8 hours ago
Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba
Labarai

Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

9 hours ago
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Jagororin ‘Yan Bindiga A Abuja, Sun Ƙwato Makamai Da ₦7.4m

11 hours ago
Likitoci Sun Gano Wuka Da Aka Burma A Kirjin Wani Mutum Tsawon Shekara 8 
Labarai

Likitoci Sun Gano Wuka Da Aka Burma A Kirjin Wani Mutum Tsawon Shekara 8 

12 hours ago
Next Post
Falalar Goman Farko Na Watan Fahimtar Sayyidina Umar (RA) Da Sayyidina Aliyu (RA) Kan Ramakon Ramadan A Goman Zulhajji

Falalar Goman Farko Na Watan Fahimtar Sayyidina Umar (RA) Da Sayyidina Aliyu (RA) Kan Ramakon Ramadan A Goman Zulhajji

LABARAI MASU NASABA

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

August 22, 2025
UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

August 22, 2025
Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

August 22, 2025
Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

August 22, 2025
JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

August 22, 2025
Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

August 22, 2025
Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

August 22, 2025
Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

August 22, 2025
Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025

Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025

August 22, 2025
Ruben Dias Ya Rattaba Hannu Kan Sabon Kwantiragi A Manchester City

Ruben Dias Ya Rattaba Hannu Kan Sabon Kwantiragi A Manchester City

August 22, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.