• English
  • Business News
Sunday, June 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Emefiele Ya Bayyana A Gaban Majalisa Kan Sauya Fasalin Kudi

Bankuna Za Su Cigaba Da Karbar Tsoffin Kudade Ko Bayan Karewar Wa'adin Daina Amfani Da Su 

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Emefiele Ya Bayyana A Gaban Majalisa Kan Sauya Fasalin Kudi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Daga karshe dai Gwamnan Babban Bankin Nijeriya (CBN), Godwin Emefiele ya bayyana a gaban kwamitin Majalisar Wakilai da ke kula da harkokin babban bankin kasa da kuma bankuna dangane da sabon tsarin sauya fasalin kudade da daina amfani da tsofaffin takardun kudade.

Majalisar ta tura wa Emefiele sammaci kan rikita-rikitar ta biyo bayan sauya fasalin manyan takardun kudade da kuma sauya tsofaffin takardun kudi zuwa sabbi.

  • Ya Kamata Mutane Su Yi Amfani Da Kwanaki 10 Wajen Mayar Da Tsofaffin Kudinsu Banki – Sanusi 
  • Tsohon Shugaban Jam’iar Bayero Ta Kano, Farfesa Ibrahim Umar Ya Rasu

Emefiele ya gurfana a gaban Kwamitin wucin gadi da Majalisar ta kafa da aka daura wa alhalin bincikar rikicin da ke karkashin jagorancin shugaban masu rinjaye na Majalisar, Alhassan Ado-Doguwa a yau Talata.

Idan za a iya tunawa dai shugaban majalisar wakilai, Femi Gbajabiamila, a makon da ta gabata ya yi barazanar bada umarnin kama Emefiele muddin ya ki bayyana a gaban Majalisar zuwa ranar Talata.

Wannan matakin ya biyo bayan shure gayyata har kusan sau hudu da Majalisar ke aike wa Emefiele.

Labarai Masu Nasaba

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Da ya ke bayani a gaban kwamitin, Mista Godwin Emefiele, ya shaida wa duniya cewa, bankunan kasuwanci za su ci gaba da karbar tsofaffin kudade har bayan karewar wa’adin daina amfani da tsoffin takardun kudade da bankin CBN din ya umarta zuwa ranar 10 ga Fabrairun 2023.

Kodayake Godwin ya nuna takaicinsa kan yadda wasu ke kawo nakasu ga tsarin sauya fasalin kudin musammman a bankuna duk da umarnin da CBN ya baiwa bankunan. Ya na mai cewa, sun nemi taimakon hukumomin yaki da cin hanci da rashawa da sauran hukumomin tsaro domin dakile aniyar masu janyo zagon kasa.

Ya ce tsarin takaita kudade na da matukar tasiri wajen hana hauhauwar farashin kayayyaki da kuma bunkasa tattalin arzikin kasa.

Ya ce, alfanun sauya kudin nan na da yawa sosai domin hatta masu garkuwa da mutane za su rasa hanyoyin cin karensu babu babbaka.

Ya nemi ‘yan Nijeriya da su Kara hakuri kan wahalar da suke fuskanta musamman na wahalar samun takardun sabon kudin, ya ce nan gaba kadan komai zai daidai.

Ya kara da cewa CBN ya tura ma’aikatan na musamman guda 30,000 yankunan karkara da ka iya fuskantar wahalhalu game da sauya tsofaffin kudadensu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: CBNEmefieleNairaTsofaffin Kudi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ya Kamata Mutane Su Yi Amfani Da Kwanaki 10 Wajen Mayar Da Tsofaffin Kudinsu Banki – Sanusi 

Next Post

Cibiyar Binciken Sararin Samaniya Ta Kasar Sin Na Gayyatar Baki Masu Basira

Related

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki
Manyan Labarai

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

4 hours ago
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa
Manyan Labarai

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

19 hours ago
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe
Manyan Labarai

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

20 hours ago
Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu
Manyan Labarai

Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

22 hours ago
Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe
Manyan Labarai

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

24 hours ago
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa
Manyan Labarai

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

1 day ago
Next Post
Cibiyar Binciken Sararin Samaniya Ta Kasar Sin Na Gayyatar Baki Masu Basira

Cibiyar Binciken Sararin Samaniya Ta Kasar Sin Na Gayyatar Baki Masu Basira

LABARAI MASU NASABA

Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar

Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar

June 29, 2025
Babu Irin Arziƙin Da Babu A Masana’antar Kannywood – Bashir Maishadda

Babu Irin Arziƙin Da Babu A Masana’antar Kannywood – Bashir Maishadda

June 29, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

June 29, 2025
Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

June 29, 2025
Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

June 28, 2025
An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

June 28, 2025
Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

June 28, 2025
Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

June 28, 2025
Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

June 28, 2025
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.