• English
  • Business News
Tuesday, September 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Emefiele Ya Bayyana A Gaban Majalisa Kan Sauya Fasalin Kudi

Bankuna Za Su Cigaba Da Karbar Tsoffin Kudade Ko Bayan Karewar Wa'adin Daina Amfani Da Su 

by Khalid Idris Doya
3 years ago
in Manyan Labarai
0
Emefiele Ya Bayyana A Gaban Majalisa Kan Sauya Fasalin Kudi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Daga karshe dai Gwamnan Babban Bankin Nijeriya (CBN), Godwin Emefiele ya bayyana a gaban kwamitin Majalisar Wakilai da ke kula da harkokin babban bankin kasa da kuma bankuna dangane da sabon tsarin sauya fasalin kudade da daina amfani da tsofaffin takardun kudade.

Majalisar ta tura wa Emefiele sammaci kan rikita-rikitar ta biyo bayan sauya fasalin manyan takardun kudade da kuma sauya tsofaffin takardun kudi zuwa sabbi.

  • Ya Kamata Mutane Su Yi Amfani Da Kwanaki 10 Wajen Mayar Da Tsofaffin Kudinsu Banki – Sanusi 
  • Tsohon Shugaban Jam’iar Bayero Ta Kano, Farfesa Ibrahim Umar Ya Rasu

Emefiele ya gurfana a gaban Kwamitin wucin gadi da Majalisar ta kafa da aka daura wa alhalin bincikar rikicin da ke karkashin jagorancin shugaban masu rinjaye na Majalisar, Alhassan Ado-Doguwa a yau Talata.

Idan za a iya tunawa dai shugaban majalisar wakilai, Femi Gbajabiamila, a makon da ta gabata ya yi barazanar bada umarnin kama Emefiele muddin ya ki bayyana a gaban Majalisar zuwa ranar Talata.

Wannan matakin ya biyo bayan shure gayyata har kusan sau hudu da Majalisar ke aike wa Emefiele.

Labarai Masu Nasaba

‘Yan Bindiga Sun Yi Wa Hakimi Yankan Rago A Zamfara

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Mayar Wa Atiku Martani Kan Cewar ‘Yan Nijeriya Na Fama Da Yunwa

Da ya ke bayani a gaban kwamitin, Mista Godwin Emefiele, ya shaida wa duniya cewa, bankunan kasuwanci za su ci gaba da karbar tsofaffin kudade har bayan karewar wa’adin daina amfani da tsoffin takardun kudade da bankin CBN din ya umarta zuwa ranar 10 ga Fabrairun 2023.

Kodayake Godwin ya nuna takaicinsa kan yadda wasu ke kawo nakasu ga tsarin sauya fasalin kudin musammman a bankuna duk da umarnin da CBN ya baiwa bankunan. Ya na mai cewa, sun nemi taimakon hukumomin yaki da cin hanci da rashawa da sauran hukumomin tsaro domin dakile aniyar masu janyo zagon kasa.

Ya ce tsarin takaita kudade na da matukar tasiri wajen hana hauhauwar farashin kayayyaki da kuma bunkasa tattalin arzikin kasa.

Ya ce, alfanun sauya kudin nan na da yawa sosai domin hatta masu garkuwa da mutane za su rasa hanyoyin cin karensu babu babbaka.

Ya nemi ‘yan Nijeriya da su Kara hakuri kan wahalar da suke fuskanta musamman na wahalar samun takardun sabon kudin, ya ce nan gaba kadan komai zai daidai.

Ya kara da cewa CBN ya tura ma’aikatan na musamman guda 30,000 yankunan karkara da ka iya fuskantar wahalhalu game da sauya tsofaffin kudadensu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: CBNEmefieleNairaTsofaffin Kudi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ya Kamata Mutane Su Yi Amfani Da Kwanaki 10 Wajen Mayar Da Tsofaffin Kudinsu Banki – Sanusi 

Next Post

Cibiyar Binciken Sararin Samaniya Ta Kasar Sin Na Gayyatar Baki Masu Basira

Related

Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Yi Wa Hakimi Yankan Rago A Zamfara

2 hours ago
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe
Manyan Labarai

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Mayar Wa Atiku Martani Kan Cewar ‘Yan Nijeriya Na Fama Da Yunwa

5 hours ago
Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 
Manyan Labarai

Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

13 hours ago
Zamfara
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Kan Masallata Tare Da Garkuwa Da Mutane A Zamfara

19 hours ago
Ƴan Bindiga Sun Kashe Sarkin Shuwaka Na Kanam A Filato
Manyan Labarai

Ƴan Bindiga Sun Kashe Sarkin Shuwaka Na Kanam A Filato

22 hours ago
Likitoci Sun Tsunduma Yajin Aiki Na Dindindin A Abuja
Manyan Labarai

Likitoci Sun Tsunduma Yajin Aiki Na Dindindin A Abuja

23 hours ago
Next Post
Cibiyar Binciken Sararin Samaniya Ta Kasar Sin Na Gayyatar Baki Masu Basira

Cibiyar Binciken Sararin Samaniya Ta Kasar Sin Na Gayyatar Baki Masu Basira

LABARAI MASU NASABA

Dan Sanda Ya Kashe Abokin Aikinsa Da Almakashi Har Lahira A Kebbi

Wata Ta Kashe ’Yar Uwarta Kan Bashin Naira 800 A Ondo

September 16, 2025
Jigilar Mai: Me Ya Haddasa Rikicin Dangote Da Ƙungiyar NUPENG?

Jigilar Mai: Me Ya Haddasa Rikicin Dangote Da Ƙungiyar NUPENG?

September 16, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

‘Yan Bindiga Sun Yi Wa Hakimi Yankan Rago A Zamfara

September 16, 2025
Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan Dimokuraɗiyya A Ghana

Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan Dimokuraɗiyya A Ghana

September 16, 2025
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Mayar Wa Atiku Martani Kan Cewar ‘Yan Nijeriya Na Fama Da Yunwa

September 16, 2025
Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne

Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne

September 15, 2025
Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

September 15, 2025
Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu

Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu

September 15, 2025
Tinubu

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Yanke Hutu, Zai Dawo Abuja Gobe Talata

September 15, 2025
Sabunta Cinikin Ba Da Hidima, Masu Zuba Jari Na Waje Suna Ganin “Damar Da Kowa Ke Bukata A Kowane Lungu Na Sin”

Sabunta Cinikin Ba Da Hidima, Masu Zuba Jari Na Waje Suna Ganin “Damar Da Kowa Ke Bukata A Kowane Lungu Na Sin”

September 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.