ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Emefiele Ya Bayyana A Gaban Majalisa Kan Sauya Fasalin Kudi

Bankuna Za Su Cigaba Da Karbar Tsoffin Kudade Ko Bayan Karewar Wa'adin Daina Amfani Da Su 

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Emefiele

Daga karshe dai Gwamnan Babban Bankin Nijeriya (CBN), Godwin Emefiele ya bayyana a gaban kwamitin Majalisar Wakilai da ke kula da harkokin babban bankin kasa da kuma bankuna dangane da sabon tsarin sauya fasalin kudade da daina amfani da tsofaffin takardun kudade.

Majalisar ta tura wa Emefiele sammaci kan rikita-rikitar ta biyo bayan sauya fasalin manyan takardun kudade da kuma sauya tsofaffin takardun kudi zuwa sabbi.

  • Ya Kamata Mutane Su Yi Amfani Da Kwanaki 10 Wajen Mayar Da Tsofaffin Kudinsu Banki – Sanusi 
  • Tsohon Shugaban Jam’iar Bayero Ta Kano, Farfesa Ibrahim Umar Ya Rasu

Emefiele ya gurfana a gaban Kwamitin wucin gadi da Majalisar ta kafa da aka daura wa alhalin bincikar rikicin da ke karkashin jagorancin shugaban masu rinjaye na Majalisar, Alhassan Ado-Doguwa a yau Talata.

ADVERTISEMENT

Idan za a iya tunawa dai shugaban majalisar wakilai, Femi Gbajabiamila, a makon da ta gabata ya yi barazanar bada umarnin kama Emefiele muddin ya ki bayyana a gaban Majalisar zuwa ranar Talata.

Wannan matakin ya biyo bayan shure gayyata har kusan sau hudu da Majalisar ke aike wa Emefiele.

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Da ya ke bayani a gaban kwamitin, Mista Godwin Emefiele, ya shaida wa duniya cewa, bankunan kasuwanci za su ci gaba da karbar tsofaffin kudade har bayan karewar wa’adin daina amfani da tsoffin takardun kudade da bankin CBN din ya umarta zuwa ranar 10 ga Fabrairun 2023.

Kodayake Godwin ya nuna takaicinsa kan yadda wasu ke kawo nakasu ga tsarin sauya fasalin kudin musammman a bankuna duk da umarnin da CBN ya baiwa bankunan. Ya na mai cewa, sun nemi taimakon hukumomin yaki da cin hanci da rashawa da sauran hukumomin tsaro domin dakile aniyar masu janyo zagon kasa.

Ya ce tsarin takaita kudade na da matukar tasiri wajen hana hauhauwar farashin kayayyaki da kuma bunkasa tattalin arzikin kasa.

Ya ce, alfanun sauya kudin nan na da yawa sosai domin hatta masu garkuwa da mutane za su rasa hanyoyin cin karensu babu babbaka.

Ya nemi ‘yan Nijeriya da su Kara hakuri kan wahalar da suke fuskanta musamman na wahalar samun takardun sabon kudin, ya ce nan gaba kadan komai zai daidai.

Ya kara da cewa CBN ya tura ma’aikatan na musamman guda 30,000 yankunan karkara da ka iya fuskantar wahalhalu game da sauya tsofaffin kudadensu.

Emefiele
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Zaɓen Fidda Gwani Na Gwamna: Ba Za Mu Lamunci Kaƙaba Mana Ɗan Takara A Bauchi Ba – Mambobin APC
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Sanata Buba Ya Janye Daga Takarar Fidda Gwani Ta Gwamnan APC A Bauchi, Ya Zargi Cewa ‘Ɗauki Ɗaura Ake Yi Ba Zaɓe Ba”
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Shugaban Kwamitin Yaɗa Labarai Na Aikin Hajjin Bana Na Bauchi Ya Rasu A Saudiyya
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Na Bar Harƙoƙin Siyasa Gaba Ɗaya – Ɗan Takarar Gwamnan Bauchi, Air Marshal Saddique Baba

MASU ALAKA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Next Post
Cibiyar Binciken Sararin Samaniya Ta Kasar Sin Na Gayyatar Baki Masu Basira

Cibiyar Binciken Sararin Samaniya Ta Kasar Sin Na Gayyatar Baki Masu Basira

LABARAI MASU NASABA

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.