• English
  • Business News
Friday, November 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [10]

by Nuhu Ubale Ibrahim
8 months ago
Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai

Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai

إياك نستعينُ : أَي نطلبُ العَونَ مِنْكَ عَلَى الْعِبَادَةِ وَ عَلَى جَمِيْعِ أُمُوْرِنَا

Fassara:

“Kuma Kai kaɗai muke neman taimakonka:wato a wurinka kaɗai muke neman taimako a bisa bauta Maka Kai ɗai, kuma a wurinka kaɗai muke neman taimako a kan al’ummammu baki ɗaya” Duba Kitãbu at-Tashīlu Li’ulūmi at-Tanzil [1/33]

Fashin Baƙi:

Kalmar “nasta’īn” tana nufin neman taimako da dogaro da Allah. Wannan yana da nasaba da Tauhīdur-Rubūbiyya, da kuma Tauhidul-Uluhiyya, wato tauhidin da yake tabbatar da cewa Allah ne kaɗai ke gudanar da al’amuran duniya da halittunsa, da kuma tauhidin da yake nuna Allah kaɗai ne ya cancanta a bauta wa Shi kaɗai.

LABARAI MASU NASABA

Yaduwar Juyin Mulki A Afirka

Ɗaliban Jihar Gombe Sun Samu Ƙarin Kashi 100 Na Kuɗin Tallafin Karatu

  • Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [9]
  • Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [8]

Neman taimako daga Allah yana da nau’i biyu:

1. Taimako na Gaba ɗaya: Wannan yana nufin cewa dukkan halittu suna buƙatar Allah wajen gudanar da rayuwa, kamar samun arziki, da lafiya, da tsira da kulawa, da sauran su.

2. Taimako na Musamman: Wannan kuwa shi ne neman taimako daga Allah wajen yi Masa ibada da biyayya, da bin hanyoyin shiriya, da tabbatar da zuciya a bisa tafarkin daidai har lokacin mutuwa da sauran su.

A wurin Allah kaɗai ake neman taimako a cikin ibada. Wannan yana nuna cewa ibada ba za ta cika ba sai da taimakon Allah. Idan mutum yana son ya yi salla, ko azumi, ko wani aikin addini, to dole ne ya dogara ga Allah domin samun dacewa. Neman taimako daga wanin Allah a cikin lamuran da mutum ba zai iya yi ba sai Allah ya taimake shi, yana cikin shirka. Misali: idan mutum yana kiran matattu ko aljannu don su taimake shi, wannan yana cikin shirka. Amma ana iya neman taimako daga mutane a cikin abubuwan da suke iya yi. Misali, mutum yana iya tambayar wani mutum don ya koya masa ilimi ko ya ba shi kuɗi a matsayin aro, amma dole ne ya yarda cewa Allah ne yake sarrafa komai.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Yaduwar Juyin Mulki A Afirka
Bakon Marubuci

Yaduwar Juyin Mulki A Afirka

November 7, 2025
gombe
Ilimi

Ɗaliban Jihar Gombe Sun Samu Ƙarin Kashi 100 Na Kuɗin Tallafin Karatu

October 18, 2025
Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma
Ilimi

Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma

October 18, 2025
Next Post
Ganduje Ya Zargi ‘Yan Siyasa Da Hannu A Haddasa Rikice-rikicen Zabe

Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Kwamishinan Ganduje Kan Zargin Ɓatan N240m

LABARAI MASU NASABA

Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Halarci Taron COP30 A Brazil

Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Halarci Taron COP30 A Brazil

November 7, 2025
Jerin Gwarazan Taurarinmu!

Jerin Gwarazan Taurarinmu!

November 7, 2025
‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri 4, Sun Ƙwato Makamai A Filato

Zaben Kananan Hukumomi A Neja Ya Bar Baya Da Kura

November 7, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Ɗauki Malaman Makaranta 500 Aiki

Gwamnatin Zamfara Ta Ɗauki Malaman Makaranta 500 Aiki

November 7, 2025
GORON JUMA’A

GORON JUMA’A

November 7, 2025
Majalisar Wakilai Ta Yi Tir Da Harin Da Aka Kai Wa Tawagar Ɗan Majalisar Neja

Majalisar Wakilai Ta Yi Tir Da Harin Da Aka Kai Wa Tawagar Ɗan Majalisar Neja

November 7, 2025
Yadda Duniya Ta Fara Wayewa Tun Daga Zamanin Annabi Nuhu (AS) Har Manzon Allah (SAW) Ya Zo Ya Cika Komai (2)

Yadda Duniya Ta Fara Wayewa Tun Daga Zamanin Annabi Nuhu (AS) Har Manzon Allah (SAW) Ya Zo Ya Cika Komai (2)

November 7, 2025
Yaduwar Juyin Mulki A Afirka

Yaduwar Juyin Mulki A Afirka

November 7, 2025
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima

Hanyoyin Noma Na Gargajiya Ba Za Su Iya Wadata Abinci A Nijeriya Ba -Masanin Kimiyya

November 7, 2025
An Kaddamar Da Taron Kolin Wuzhen Na Ayyuka Masu Nasaba Da Yanar Gizo

An Kaddamar Da Taron Kolin Wuzhen Na Ayyuka Masu Nasaba Da Yanar Gizo

November 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.