ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, November 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [8]

by Nuhu Ubale Ibrahim
8 months ago
Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai

Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai

“التَّقْوَى مَصْدَرٌ مُشْتَقٌّ مِنَ الوِقَايَةِ، مَعْنَاهَا الخَوْفُ وَالِالْتِزَامُ بِطَاعَةِ اللهِ وَتَرْكُ مَعَاصِيهِ، فَهِيَ جَامِعَةٌ لِكُلِّ خَيْرٍ”

Fassara:

“Takawa kalma ce da aka samo daga ‘kariya’ Ma’anar taƙawa shi ne jin tsoron Allah, da lazimtar biyayya ga Allah da barin saɓa Masa. Taƙawa ta tattaro dukan alherai gaba ɗaya. “ Duba Kitãbu at-Tashīlu fi Ulūmi at-Tanzil [1/17]

ADVERTISEMENT
  • Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [6]
  • Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [7]

Fashin Baƙi:

Maganar babban malami Ibnu Juzai Allah Ya yi masa rahama, tana bayyana ma’anar taƙawa a harshen Larabci, da kuma harshe na na shari’a.

LABARAI MASU NASABA

NELFUND Ta Ce Dalibai Miliyan Daya Ne Suka Nemi Tallafin Kudin Karatu

Yaduwar Juyin Mulki A Afirka

Taƙawa a harshen Larabci: tana nufin ‘kariya’. Attaƙawa (التَّقْوَى) ta samo asali daga wiƙãya (وِقَايَة), wacce ke nufin katanga ko kariya. Wannan yana nuna cewa taƙawa tana nufin kare bawa daga azabar Allah ta hanyar bin umarninsa da guje wa saɓonsa.

Ma’anar Taƙawa a Shari’a: Ibnu Juzai al-Kalbi ya fassara taƙawa da jin tsoron Allah da lazimtar biyayya gare shi da barin saɓa masa. Wannan yana daidai da abin da malamai kamar Ibn Rajab da al-Gazzali suka bayyana, cewa taƙawa ba wai tsoro kaɗai ba ne, har da tsoron da ke haddasa aiki da biyayya.

Jin tsoron Allah: Wannan yana nufin mutum ya san Allah da girmansa, wanda hakan ke sa shi jin tsoron yin abin da zai jawo fushinsa.

Lazimtar biyayya: Wato mutum yana da nufin aikata duk abin da Allahda Manzonsa suka yi umurni da shi.

Barin saɓo: Wato mutum yana nisantar duk wani abu da zai jawo fushin Allah na magana ko aiki, na fili da na ɓoye.

Faidojin Taƙawa:

Taƙawa tana da fa’idoji masu yawa, da suka haɗa da: Samun ƙauna daga Allah da kankarar zunubai da girmama lada da mutum zai samu. Taƙawa sababi ce ta samun albarkatun Allah, da toshe kofofin sharri.

Taƙawa tana sanya mutum ya sami mafita a rayuwarsa duk rintsin da mutum zai shiga. Taƙawa tana sanya al’amuran bawa su zama masu sauƙi. Taƙawa tana sanya mutum ya sami rabauta da rahamar Allah, tana kuma sanya mutum ya sami tsira.

Taƙawa tana sanya mutum ya girmama Allah da kuma sanya mutum ya zama adali mai nagarta a cikin al’umma, sannan tana sanya mutum ya nisanci zalunci tare da lazimtar gaskiya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

NELFUND Ta Ce Dalibai Miliyan Daya Ne Suka Nemi Tallafin Kudin Karatu
Ilimi

NELFUND Ta Ce Dalibai Miliyan Daya Ne Suka Nemi Tallafin Kudin Karatu

November 8, 2025
Yaduwar Juyin Mulki A Afirka
Bakon Marubuci

Yaduwar Juyin Mulki A Afirka

November 7, 2025
gombe
Ilimi

Ɗaliban Jihar Gombe Sun Samu Ƙarin Kashi 100 Na Kuɗin Tallafin Karatu

October 18, 2025
Next Post
An Cafke Wadanda Ake Zargi Da Daba Wa Dan Wasan Nijeriya Mazaunin Kasar Ireland Wuka Har Lahira

An Cafke Wadanda Ake Zargi Da Daba Wa Dan Wasan Nijeriya Mazaunin Kasar Ireland Wuka Har Lahira

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Majalisa 60 Sun Yi Barazanar Ficewa Daga PDP

Kotu Ta Sake Hana PDP Gudanar Da Babban Taronta Na Ƙasa

November 11, 2025
‘Yansanda Sun Ƙaryata Rahoton Kashe Ɗan Wasan Barau FC A Katsina

‘Yansanda Sun Ƙaryata Rahoton Kashe Ɗan Wasan Barau FC A Katsina

November 11, 2025
Tinubu Ya Aika Wakilai Don Tattaunawa Da Birtaniya Kan Dawo Da Ekweremadu Nijeriya

Tinubu Ya Aika Wakilai Don Tattaunawa Da Birtaniya Kan Dawo Da Ekweremadu Nijeriya

November 11, 2025
HOTUNA: Yadda Gobara Ta Ƙone Shaguna 25 A Kasuwar Singa A Kano

HOTUNA: Yadda Gobara Ta Ƙone Shaguna 25 A Kasuwar Singa A Kano

November 11, 2025
‘Yan Bindiga Da ‘Yan Ta’adda Sun Fi Sojojin Nijeriya Yawan Makamai – Babachir

‘Yan Bindiga Da ‘Yan Ta’adda Sun Fi Sojojin Nijeriya Yawan Makamai – Babachir

November 11, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

Faɗa Ya Kaure Tsakanin Boko Haram Da ISWAP, An Kashe Mayaƙa Sama Da 170

November 11, 2025
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa

Trump Ya Yi Barazanar Maka BBC A Kotu Tare Da Neman Diyyar $1bn

November 11, 2025
Rashin Aiki Ga Matasa Babbar Barazana Ce Ga Nijeriya – Obasanjo 

Obasanjo Ya Buƙaci Matasa Su Karɓi Ragamar Shugabanci A Ƙasashen Afrika

November 11, 2025
Yadda Muka Zama Bayin ‘Yan Bindiga -Mazaunin Wani Kauye

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 A Ƙauyen Katsina

November 11, 2025
An Daddale Kulla Cinikin Sama Da Dala Biliyan 83 A Bikin CIIE Na Kasar Sin 

An Daddale Kulla Cinikin Sama Da Dala Biliyan 83 A Bikin CIIE Na Kasar Sin 

November 10, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.