ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [6]

by Nuhu Ubale Ibrahim
1 year ago
Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai

Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai

قَوْلُهُ عَلَيْهِ السَّلَامُ مُقَدَّمٌ عَلَى أَقْوَالِ النَّاسِ
Fassara:

“Maganar Manzon Allah (S.A.W) ita ake gabatarwa a kan magana mutane baki ɗaya “ Duba Kitãbu at-Tashīlu Li’ulūmi at-Tanzil [1/7].

Fashin Baƙi:

ADVERTISEMENT

Wannan magana ta babban malami Ibnu Juzai Allah Ya yi masa rahama ƙa’ida ce da tushenta yake da dalilai daga Alƙur’ani da Hadisi, kuma malamai da dama sun jaddada muhimmancinta da wajabcin aiki da ita a fili da ɓoye.

  • Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [4]
  • Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [5]

Allah Ta’ala Yana cewa:” Ya ku mummunai! Ku yu ɗa’a ga Allah, kuma ku yi ɗa’a ga Manzo da kuma majiɓinta lamarinku. Idan kun yi jayayya a kan wani abu, to ku mayar da shi zuwa ga Allah da Manzonsa in kun kasance kun yi imani da Allah da ranar ƙarshe. Wannan shi ne mafi alheri, kuma mafi kyawun makoma” Suratun Nisã’i aya ta 59.

LABARAI MASU NASABA

An Tantance Masu Neman Aikin Koyarwa 500 A Jigawa

JAMB Ta Ƙara Wa’adin Amincewar Guraben Karatu Zuwa 30 Satumba

Wannan aya tana nuna cewa idan aka sami saɓani, to dole ne a mayar da al’amari zuwa ga Allah da Manzonsa, wato Alƙur’ani da Sunna. Allah Ta’ala Ya ƙara cewa:” Kuma abin da Manzo ya ba ku sai ku karɓe shi, abin kuma da ya hana ku sai ku hanu. Ku kuma kiyaye dokokin Allah, Lalle Allah Mai tsananin uƙuba ne.” Suratul Hashri aya ta 7. Manzon Allah (S.A.W) ya ce: “Duk abin da na hane ku, to ku nisance shi; kuma abin da na umarce ku, to ku aikata shi gwargwadon iyawarku.” Bukhari ne ya ruwaito [#7288] da Muslim[#1337]. Wannan hadisi yana nuna cewa dole ne a bi umurnin Annabi (S.A.W) kuma a nisanci abin da ya hana.

Maganganun Malamai:

Banyan malaman Musulunci kuma jagorin shiriya sun bayyana maganar Manzon Rahama(S.A.W) ita ce ta fi cancanta abi a kan maganar mutane baki ɗaya. Ga maganar wasu daga cikinsu:

Imam Abu Hanifa Allah Ya yi masa rahama yana cewa:” Idan hadisi ya inganta, to shi ne Mazahabata” Duba Ibnu Abidin; al-Hãshiyatu [1/63]. Wannan yana nuna cewa Imam Abu Hanifa yana fifita hadisin Annabi (S.A.W) kan ra’ayinsa ko ijtihadinsa.

Imam Malik Allah Ya yi masa rahama shi kuma cewa ya yi:” Ni mutum ne, ina yin daidai kuma ina kuskure, ku duba ra’ayina, duk wanda ya dace da Alƙur’ani da Sunna, to ku riƙe shi, duk kuma wanda ya saɓa wa Alƙur’ani da Sunna, to ku bar shi.” Duba Ibnu Abdilbarri; Jãmi’u Bayãnil ilmi [2/32]. Imam Malik yana nuni da Alƙur’ani da Sunnar Annabi (S.A.W) su ne abin gabatarwa a bisa maganarsa.

Imam ash-Shafi’i Allah Ya yi masa rahama shi kuma cewa ya yi:”Idan hadisi ya inganta, to shi ne Mazahabata” Duba an-Nawawi; al-Majmū’u [1/63]. Wannan yana nuna cewa Imam ash- Shafi’i yana fifita hadisin Annabi a kan ra’ayinsa ko ijtihadinsa.

Imam Ahmad ɗan Hanbal Allah Ya yi masa rahama cewa ya yi:” Duk wanda ya ƙi karɓar Hadisin Manzon Allah Sallallahu alaihi wa alihi wa sallam, to yana gaɓar halaka” Duba Ibnul Jauzi; al-Manãƙibu [shafi na 182].
Wannan yana nuna cewa Imam Ahmad yana karɓar koyarwar Annabi (S.A.W) fiye da ra’ayoyin mutane, kuma ƙin karɓar hadisi halaka ne.

Maganar Ibn Juzai tana tabbatar da cewa maganar Annabi Muhammad (S.A.W) ita ce ake ba wa muhimmanci a kan maganar sauran mutane, kuma ita ce shiriya, saɓa mata kuma halaka ne da ɓata. Allah Ya datar da mu da bin Annabi (S.A.W) a fai da ɓoye. Amin.

Daga
Nuhu Ubale Ibrahim
+ postsBio
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    Layya Babbar Ibada A Musulunci Na 1
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    Karamar Sallah: Sallar Idi A Wajen Musulmi…
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    SAHUR [Falalarsa Da Fa’idojinsa] Na 23
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    SAHUR [Falalarsa Da Fa’idojinsa] Na 22

MASU ALAKA

Daga
Ilimi

An Tantance Masu Neman Aikin Koyarwa 500 A Jigawa

August 31, 2026
Daga
Ilimi

JAMB Ta Ƙara Wa’adin Amincewar Guraben Karatu Zuwa 30 Satumba

August 29, 2026
Zanga-Zanga: Gwamnatin Yobe Ta Bayar Da Umarnin Rufe Makarantun Jihar
Bakon Marubuci

Buni Ya Nuna Kwarewarsa Ta Diflomasiyya

August 28, 2026
Next Post
Ranar Mata Ta Duniya: Kalubalen Da Mata Ke Fuskanta A Siyasar Nijeriya

Ranar Mata Ta Duniya: Kalubalen Da Mata Ke Fuskanta A Siyasar Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.