ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [6]

by Nuhu Ubale Ibrahim
1 year ago
Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai

Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai

قَوْلُهُ عَلَيْهِ السَّلَامُ مُقَدَّمٌ عَلَى أَقْوَالِ النَّاسِ
Fassara:

“Maganar Manzon Allah (S.A.W) ita ake gabatarwa a kan magana mutane baki ɗaya “ Duba Kitãbu at-Tashīlu Li’ulūmi at-Tanzil [1/7].

Fashin Baƙi:

ADVERTISEMENT

Wannan magana ta babban malami Ibnu Juzai Allah Ya yi masa rahama ƙa’ida ce da tushenta yake da dalilai daga Alƙur’ani da Hadisi, kuma malamai da dama sun jaddada muhimmancinta da wajabcin aiki da ita a fili da ɓoye.

  • Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [4]
  • Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [5]

Allah Ta’ala Yana cewa:” Ya ku mummunai! Ku yu ɗa’a ga Allah, kuma ku yi ɗa’a ga Manzo da kuma majiɓinta lamarinku. Idan kun yi jayayya a kan wani abu, to ku mayar da shi zuwa ga Allah da Manzonsa in kun kasance kun yi imani da Allah da ranar ƙarshe. Wannan shi ne mafi alheri, kuma mafi kyawun makoma” Suratun Nisã’i aya ta 59.

LABARAI MASU NASABA

Hukumar NCCE Ta Yi Tsare-tsaren Bunƙasa Horar Da Malamai

Abubuwan Da Ya Kamata Magidanci Ya Sani Bayan Matarsa Ta Haihu

Wannan aya tana nuna cewa idan aka sami saɓani, to dole ne a mayar da al’amari zuwa ga Allah da Manzonsa, wato Alƙur’ani da Sunna. Allah Ta’ala Ya ƙara cewa:” Kuma abin da Manzo ya ba ku sai ku karɓe shi, abin kuma da ya hana ku sai ku hanu. Ku kuma kiyaye dokokin Allah, Lalle Allah Mai tsananin uƙuba ne.” Suratul Hashri aya ta 7. Manzon Allah (S.A.W) ya ce: “Duk abin da na hane ku, to ku nisance shi; kuma abin da na umarce ku, to ku aikata shi gwargwadon iyawarku.” Bukhari ne ya ruwaito [#7288] da Muslim[#1337]. Wannan hadisi yana nuna cewa dole ne a bi umurnin Annabi (S.A.W) kuma a nisanci abin da ya hana.

Maganganun Malamai:

Banyan malaman Musulunci kuma jagorin shiriya sun bayyana maganar Manzon Rahama(S.A.W) ita ce ta fi cancanta abi a kan maganar mutane baki ɗaya. Ga maganar wasu daga cikinsu:

Imam Abu Hanifa Allah Ya yi masa rahama yana cewa:” Idan hadisi ya inganta, to shi ne Mazahabata” Duba Ibnu Abidin; al-Hãshiyatu [1/63]. Wannan yana nuna cewa Imam Abu Hanifa yana fifita hadisin Annabi (S.A.W) kan ra’ayinsa ko ijtihadinsa.

Imam Malik Allah Ya yi masa rahama shi kuma cewa ya yi:” Ni mutum ne, ina yin daidai kuma ina kuskure, ku duba ra’ayina, duk wanda ya dace da Alƙur’ani da Sunna, to ku riƙe shi, duk kuma wanda ya saɓa wa Alƙur’ani da Sunna, to ku bar shi.” Duba Ibnu Abdilbarri; Jãmi’u Bayãnil ilmi [2/32]. Imam Malik yana nuni da Alƙur’ani da Sunnar Annabi (S.A.W) su ne abin gabatarwa a bisa maganarsa.

Imam ash-Shafi’i Allah Ya yi masa rahama shi kuma cewa ya yi:”Idan hadisi ya inganta, to shi ne Mazahabata” Duba an-Nawawi; al-Majmū’u [1/63]. Wannan yana nuna cewa Imam ash- Shafi’i yana fifita hadisin Annabi a kan ra’ayinsa ko ijtihadinsa.

Imam Ahmad ɗan Hanbal Allah Ya yi masa rahama cewa ya yi:” Duk wanda ya ƙi karɓar Hadisin Manzon Allah Sallallahu alaihi wa alihi wa sallam, to yana gaɓar halaka” Duba Ibnul Jauzi; al-Manãƙibu [shafi na 182].
Wannan yana nuna cewa Imam Ahmad yana karɓar koyarwar Annabi (S.A.W) fiye da ra’ayoyin mutane, kuma ƙin karɓar hadisi halaka ne.

Maganar Ibn Juzai tana tabbatar da cewa maganar Annabi Muhammad (S.A.W) ita ce ake ba wa muhimmanci a kan maganar sauran mutane, kuma ita ce shiriya, saɓa mata kuma halaka ne da ɓata. Allah Ya datar da mu da bin Annabi (S.A.W) a fai da ɓoye. Amin.

Daga
Nuhu Ubale Ibrahim
+ postsBio
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    Layya Babbar Ibada A Musulunci Na 1
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    Karamar Sallah: Sallar Idi A Wajen Musulmi…
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    SAHUR [Falalarsa Da Fa’idojinsa] Na 23
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    SAHUR [Falalarsa Da Fa’idojinsa] Na 22

MASU ALAKA

Hukumar NCCE Ta Yi Tsare-tsaren Bunƙasa Horar Da Malamai
Ilimi

Hukumar NCCE Ta Yi Tsare-tsaren Bunƙasa Horar Da Malamai

May 31, 2026
Abubuwan Da Ya Kamata Magidanci Ya Sani Bayan Matarsa Ta Haihu
Ilimi

Abubuwan Da Ya Kamata Magidanci Ya Sani Bayan Matarsa Ta Haihu

May 30, 2026
Layya Babbar Ibada A Musulunci Na 1
Bakon Marubuci

Layya Babbar Ibada A Musulunci Na 1

May 27, 2026
Next Post
Ranar Mata Ta Duniya: Kalubalen Da Mata Ke Fuskanta A Siyasar Nijeriya

Ranar Mata Ta Duniya: Kalubalen Da Mata Ke Fuskanta A Siyasar Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.