ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [6]

by Nuhu Ubale Ibrahim
1 year ago
Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai

Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai

قَوْلُهُ عَلَيْهِ السَّلَامُ مُقَدَّمٌ عَلَى أَقْوَالِ النَّاسِ
Fassara:

“Maganar Manzon Allah (S.A.W) ita ake gabatarwa a kan magana mutane baki ɗaya “ Duba Kitãbu at-Tashīlu Li’ulūmi at-Tanzil [1/7].

Fashin Baƙi:

ADVERTISEMENT

Wannan magana ta babban malami Ibnu Juzai Allah Ya yi masa rahama ƙa’ida ce da tushenta yake da dalilai daga Alƙur’ani da Hadisi, kuma malamai da dama sun jaddada muhimmancinta da wajabcin aiki da ita a fili da ɓoye.

  • Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [4]
  • Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [5]

Allah Ta’ala Yana cewa:” Ya ku mummunai! Ku yu ɗa’a ga Allah, kuma ku yi ɗa’a ga Manzo da kuma majiɓinta lamarinku. Idan kun yi jayayya a kan wani abu, to ku mayar da shi zuwa ga Allah da Manzonsa in kun kasance kun yi imani da Allah da ranar ƙarshe. Wannan shi ne mafi alheri, kuma mafi kyawun makoma” Suratun Nisã’i aya ta 59.

LABARAI MASU NASABA

Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace

Hukumar Ilimin Bai-ɗaya Ta Jihar Yobe Ta Raba Kayan Karatu

Wannan aya tana nuna cewa idan aka sami saɓani, to dole ne a mayar da al’amari zuwa ga Allah da Manzonsa, wato Alƙur’ani da Sunna. Allah Ta’ala Ya ƙara cewa:” Kuma abin da Manzo ya ba ku sai ku karɓe shi, abin kuma da ya hana ku sai ku hanu. Ku kuma kiyaye dokokin Allah, Lalle Allah Mai tsananin uƙuba ne.” Suratul Hashri aya ta 7. Manzon Allah (S.A.W) ya ce: “Duk abin da na hane ku, to ku nisance shi; kuma abin da na umarce ku, to ku aikata shi gwargwadon iyawarku.” Bukhari ne ya ruwaito [#7288] da Muslim[#1337]. Wannan hadisi yana nuna cewa dole ne a bi umurnin Annabi (S.A.W) kuma a nisanci abin da ya hana.

Maganganun Malamai:

Banyan malaman Musulunci kuma jagorin shiriya sun bayyana maganar Manzon Rahama(S.A.W) ita ce ta fi cancanta abi a kan maganar mutane baki ɗaya. Ga maganar wasu daga cikinsu:

Imam Abu Hanifa Allah Ya yi masa rahama yana cewa:” Idan hadisi ya inganta, to shi ne Mazahabata” Duba Ibnu Abidin; al-Hãshiyatu [1/63]. Wannan yana nuna cewa Imam Abu Hanifa yana fifita hadisin Annabi (S.A.W) kan ra’ayinsa ko ijtihadinsa.

Imam Malik Allah Ya yi masa rahama shi kuma cewa ya yi:” Ni mutum ne, ina yin daidai kuma ina kuskure, ku duba ra’ayina, duk wanda ya dace da Alƙur’ani da Sunna, to ku riƙe shi, duk kuma wanda ya saɓa wa Alƙur’ani da Sunna, to ku bar shi.” Duba Ibnu Abdilbarri; Jãmi’u Bayãnil ilmi [2/32]. Imam Malik yana nuni da Alƙur’ani da Sunnar Annabi (S.A.W) su ne abin gabatarwa a bisa maganarsa.

Imam ash-Shafi’i Allah Ya yi masa rahama shi kuma cewa ya yi:”Idan hadisi ya inganta, to shi ne Mazahabata” Duba an-Nawawi; al-Majmū’u [1/63]. Wannan yana nuna cewa Imam ash- Shafi’i yana fifita hadisin Annabi a kan ra’ayinsa ko ijtihadinsa.

Imam Ahmad ɗan Hanbal Allah Ya yi masa rahama cewa ya yi:” Duk wanda ya ƙi karɓar Hadisin Manzon Allah Sallallahu alaihi wa alihi wa sallam, to yana gaɓar halaka” Duba Ibnul Jauzi; al-Manãƙibu [shafi na 182].
Wannan yana nuna cewa Imam Ahmad yana karɓar koyarwar Annabi (S.A.W) fiye da ra’ayoyin mutane, kuma ƙin karɓar hadisi halaka ne.

Maganar Ibn Juzai tana tabbatar da cewa maganar Annabi Muhammad (S.A.W) ita ce ake ba wa muhimmanci a kan maganar sauran mutane, kuma ita ce shiriya, saɓa mata kuma halaka ne da ɓata. Allah Ya datar da mu da bin Annabi (S.A.W) a fai da ɓoye. Amin.

Daga
Nuhu Ubale Ibrahim
+ postsBio
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    Layya Babbar Ibada A Musulunci Na 1
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    Karamar Sallah: Sallar Idi A Wajen Musulmi…
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    SAHUR [Falalarsa Da Fa’idojinsa] Na 23
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    SAHUR [Falalarsa Da Fa’idojinsa] Na 22

MASU ALAKA

Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace
Ilimi

Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace

June 20, 2026
Hukumar Ilimin Bai-ɗaya Ta Jihar Yobe Ta Raba Kayan Karatu
Ilimi

Hukumar Ilimin Bai-ɗaya Ta Jihar Yobe Ta Raba Kayan Karatu

June 20, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund
Ilimi

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Next Post
Ranar Mata Ta Duniya: Kalubalen Da Mata Ke Fuskanta A Siyasar Nijeriya

Ranar Mata Ta Duniya: Kalubalen Da Mata Ke Fuskanta A Siyasar Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Safarar Kuɗi Dala Miliyan 2.53

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Safarar Kuɗi Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.