• English
  • Business News
Sunday, October 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [19]

by Nuhu Ubale Ibrahim
6 months ago
in Addini, Bakon Marubuci, Ilimi
0
Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai

Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai

Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Faidar Istigfari:

Ibnu Juzai a-Kalbi Allah Ya yi masa rahama yana cewa:

وَ أَمَّا ٱلٱسْتِغْفَارُ فَثَمَرَتُهُ ٱلٱسْتِقَامَةُ عَلَى ٱلتَّقْوَىٰ، وَ ٱلْمُحَافَظَةُ عَلَىٰ شُرُوطِ ٱلتَّوْبَةِ مَعَ إِنْكَارِ ٱلْقَلْبِ بِسَبَبِ ٱلذُّنُوبِ.

Fassara:

“ Ka ga yin istigfari, sakamakonsa shi ne tsayuwa kan taƙawa, da kiyaye sharuɗan tuba, tare da inkarin saɓo da zuciya za ta yi saboda zunuban da aka aikata” Duba Kitãbu at-Tashīlu Li’ulūmi at-Tanzil [1/65]

Labarai Masu Nasaba

Jami’ar Ibadan Ta Bude Sashen Karatu A Gida Ta Intanet

Raya Al’ada: Bikin Kalankuwa Na 2025 A Kano

  • Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [18]
  • Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [17]

Fashin Baƙi:

Wannan magana ta Ibnu Juzai al-Kalbi Allah Ya ji ƙan sa tana bayani ne a kan istigfari ( wato nema gafarar Allah) da sakamakonsa a rayuwar mutum. Domin fahimtar wannan tasa dalla-dalla, zan yi bayani a matakai uku:

Ma’anar Istigfari da Muhimmancinsa:

Istigfari na nufin neman gafarar Allah Ta’ala bisa zunubai da aka aikata. Ana yin hakan ta hanyar faɗin “Astaghfirullah” da sauran lafuzza masu kama da hakan. Allah Maɗaukakin Sarki ya yawaita umurni da a yi istigfari a cikin Alƙur’ani, kamar yadda ya ce:
” sai na ce: Ku nemi gafarar Ubangijinku, lalle Shi Ya kasance Mai ywana gafara ne” Suratu Nuh aya ta 10.

Manzon Allah (S.A.W) yana yawaita istigfari fiye da sau saba’in a rana, kamar yadda hadisi ya tabbatar da haka a cikin Sahihul Bukhari da Muslim..

Sakamakon Istigfari a Bisa Maganar Ibnu Juzai:

Ibnu Juzai yana bayani ne cewa istigfari yana da tasiri a rayuwar mai neman gafara, kuma sakamakonsa yana bayyana a cikin:

Tsayuwa Kan Taƙawa:
Taƙawa tana nufin kiyaye umarnin Allah da guje wa haninsa wato nisantar saɓa masa. Idan mutum yana neman gafarar Allah da gaske, hakan yana ƙarfafa tsoron Allah a zuciyarsa, wanda ke hana shi komawa ga zunubi. Allah Ta’ala Yana cewa:” Kuma ku tuba ga Allah gaba ɗayanku ya ku mummunai domin ku rabauta” Suratun Nur aya ta 31.

Kiyaye Sharuddan Tuba:
Tuba tana da sharuɗa guda uku, idan zunubin ba ya da alaƙa da wani bawa, to sharuɗan guda uku ne, idan kuma yana da alaƙa da wani, to sharuɗan hudu ne kamar haka:

1. Nadama bisa abin da aka aikata.
2. Barin zunubin nan take ba tare da jinkiri ba.
3. Ƙudirin kada a koma ga zunubin nan gaba.
4. Idan ya shafi wani mutum, sai a biya shi haƙƙinsa.

Idan mutum yana istigfari ba tare da kiyaye waɗannan sharuɗa ba, to istigfarinsa ba zai ba yi mass tasiri sosai ba.

Inkarin Saɓo da Zuciya:
Wannan yana nuna cewa zuciyar mai istigfari tana ƙin saɓo kuma tana jin haushin zunuban da aka aikata a baya. Wannan na nufin istigfari na gaskiya yan ƙarfafar bawa a kan aibata saɓo da jin nauyin aika shi. Hakan yana nufin istigfari yana gina halin mutumin da ya fahimci girman zunubi, kuma hakan yana hana shi sake aikata shi.

Muhimmancin Wannan Magana a Rayuwa:

Maganar Ibnu Juzai tana koyar da cewa:
• Istigfari ba kawai furuci ba ne, yana da tasiri ga zuciya da hali.
• Dole ne istigfari ya kasance tare da takawa da gujewa sabo.
• Kiyaye sharuɗan tuba yana tabbatar da cewa istigfarin mutum ya dace da shari’a.

A taƙaice, Ibnu Juzai a-Kalbi Allah Ya ji ƙan sa yana jaddada cewa istigfari na gaskiya yana haifar da tsayuwa a kan addini, da kiyaye dokokin Allah, da gujewa komawa ga zunubi. Wannan yana nufin cewa nema gafarar Allah ba wai magana ce ta fatar baki kawai ba, sai da aikin zuciya da na gaɓɓai.

Allah ya sa mu kasance cikin masu istigfari na gaskiya!


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Abu Razina Nuhu Ubale PakiAl-qur'aniAlƙur’aniIbnu JuzaiRamadanTafsiriTafsirin Alƙur’aniTafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Za Ta Dauki Matakai Don Kiyaye Hakki Da Muradun Kamfanoninta

Next Post

Sallah: Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Litinin Da Talata A Matsayin Hutu

Related

Jami’ar Ibadan Ta Bude Sashen Karatu A Gida Ta Intanet
Ilimi

Jami’ar Ibadan Ta Bude Sashen Karatu A Gida Ta Intanet

1 day ago
Raya Al’ada: Bikin Kalankuwa Na 2025 A Kano
Bakon Marubuci

Raya Al’ada: Bikin Kalankuwa Na 2025 A Kano

2 days ago
Ilimin Fasaha Shi Ne Tafarkin Cire Nijeriya Daga Kangin Fatara – NBTE
Ilimi

Ilimin Fasaha Shi Ne Tafarkin Cire Nijeriya Daga Kangin Fatara – NBTE

1 week ago
Me Ake Nufi Da Ado? 
Bakon Marubuci

Me Ake Nufi Da Ado? 

1 week ago
Makarantun Da Ba Ƙwararrun Malamai Za Su Rasa Zama Cibiyar Rubuta Jarrabawar NECO
Ilimi

Makarantun Da Ba Ƙwararrun Malamai Za Su Rasa Zama Cibiyar Rubuta Jarrabawar NECO

2 weeks ago
Ɗalibai 750 Sun Amfana Da Bashin Karatu Na Naira Milyan 32.14 A Jihar Gombe
Ilimi

Ɗalibai 750 Sun Amfana Da Bashin Karatu Na Naira Milyan 32.14 A Jihar Gombe

3 weeks ago
Next Post
Babu Wani Shiri Na Kwaso ‘Yan Nijeriya Daga Falasdin Ko Isra’ila –Gwamnatin Tarayya

Sallah: Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Litinin Da Talata A Matsayin Hutu

LABARAI MASU NASABA

Ko Kin San… Amfanin Sabaya Ga Mace?

Ko Kin San… Amfanin Sabaya Ga Mace?

October 5, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

Rundunar ‘Yansanda Ta Kama Wanda Ake Zargi Da Haɗa-baki Kan Sace Mai Anguwa A Kano

October 5, 2025
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto

Al’ummar Sokoto Sun Koka Kan Yadda Hare-haren Lakurawa Ke Kara Ta’azzara

October 5, 2025
Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

October 4, 2025
Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

October 4, 2025
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

October 4, 2025
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.