ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [17]

by Nuhu Ubale Ibrahim
1 year ago
Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai

Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai

Rabe-raben Hassa da

Ci gaba: Mataki na Biyu na Hassada:
Shi ne mutum ya so wata ni’ima ta gushe daga hannun wani saboda yana fatan ta koma wurinsa. Wannan nau’in hassada yana haɗe da kwaɗayi da son kai, domin mai irin wannan hali yana ganin cewa shi ne ya cancanci wannan ni’ima fiye da wanda yake da ita.

Misalin Irin Wannan Hassada:
Mutum yana so wani ya rasa matsayinsa ko shugabancinsa saboda yana fatan shi ya maye gurbinsa, ko wani ya riƙa fatan wani ya yi asarar dukiyarsa don shi ya gaji wannan dukiya, ko wani ya so wata mace ta rabu da mijinta saboda yana son ya aure ta, ko wani ɗalibi ya so a kore wani daga makaranta don shi ya karɓi gurbin sa.

ADVERTISEMENT
  • Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [15]
  • Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [14]

Wannan matakin hassada yana nuna babban matsayi na mugunta da rashin tausayi. Mai irin wannan hali ba kawai yana jin haushin ni’imar wani ba, har ma yana ƙoƙarin ganin ya mallake ta.

Alamomin Wannan Hassada:
Mutum mai irin wannan hassada yana da wasu alamu da ke bayyana shi:
• Jin tsananin kwaɗayi da kishi a kan wata ni’ima.
• Yana tunanin cewa shi ya fi cancanta da wannan alheri.
• Ƙoƙarin hana mai wannan ni’ima jin daɗin rayuwarsa.
• Idan wannan ni’ima ta gushe daga hannun wanda yake da ita, sai ya ji daɗi kuma ya natsu.
• Yana iya ɗaukar matakai na sharri don ganin ya mallaki abin da ba nasa ba.

LABARAI MASU NASABA

Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace

Hukumar Ilimin Bai-ɗaya Ta Jihar Yobe Ta Raba Kayan Karatu

Misalan Wannan Hassada:
1. Hassadar Fir’auna a Kan Annabi Musa (AS):
Fir’auna ba ya son aiken da Allah Ya yi wa Annabi Musa (AS) ba, domin yana tsoron cewa mulkinsa zai ƙare. Ya so cewa wannan matsayi na shugabanci da iko ya kasance a gare shi kawai.

Allah Ta’ala Ya ce:” Fir’auna kuma ya ce: ‘Ku bar ni in kashe Musa, kuma ya je ya kira Ubangijinsa! Lallai ni ina tsoron ya canza addininku, ko kuma ya bayyana ɓarna a cikin ƙasa.'” Suratu Gãfir aya ta 26.

Fir’auna bai so wani ya sami iko ko shugabanci sai shi, don haka ya so ya kashe annabi Musa (AS) domin mulkinsa ya dore.

2. Hassadar Ƙuraishawa ga Annabi Muhammad (SAW):
A lokacin da Manzon Allah (SAW) ya bayyana da’awarsa, manyan shugabannin Ƙuraishawa sun ji haushin hakan, domin suna son a ce su ne kawai suka mallaki wannan matsayi na shugabanci da daraja. Allah Ta’ala Yana cewa “ Yanzu su ne suke raba rahamar Ubangijinka (ta annabi)? Mu ne muka raba musu arziƙinsu a rayuwar duniya. Mu muka ɗaukaka darjojin sashinsu a kan sashi, don wani sashi ya riƙi wani sashi mai yi masa hidima. Rahamar Ubangijinka kuma ita ta fi abin da suke tarawa na duniya.” Suratuz-Zukhruf aya ta 32.

Illolin Wannan Hassada:
Rashin Yarda da Ƙaddarar Allah: Mutum mai irin wannan hassada yana ƙin yarda Allah Ya raba ni’imomi. Yana jin cewa shi ya fi cancanta da wata ni’ima fiye da wanda yake da ita. Wannan yana nuni da ƙarancin imani.

Haddasa Gaba da Rikici: Wannan nau’in hassada yana jawo matsaloli a cikin zamantakewa. Idan mutum yana da burin hana wasu cin gajiyar ni’imar da Allah Ya ba su, to hakan yana haifar da gaba, kishi, da yaƙe-yaƙe a cikin al’umma.

Rashin Albarka a Rayuwa: Allah Ba ya albarkantar da wanda yake da zuciyar hassada. Mutumin da yake son ya hana wani alheri don shi ya mallake shi, sau da yawa ba zai kai ga hakan ba, kuma ko da ya samu, ba zai sami albarka a ciki ba.

Ruɗewa da Rashin Hankali: Mai irin wannan hassadar baya samun kwanciyar hankali. Yana jin kishi da tsananin damuwa idan wani yana cikin ni’ima. Wannan yana iya haifar da ciwon zuciya, matsanancin damuwa, da rashin kwanciyar hankali da nutsuwa.

Daga
Nuhu Ubale Ibrahim
+ postsBio
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    Layya Babbar Ibada A Musulunci Na 1
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    Karamar Sallah: Sallar Idi A Wajen Musulmi…
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    SAHUR [Falalarsa Da Fa’idojinsa] Na 23
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    SAHUR [Falalarsa Da Fa’idojinsa] Na 22

MASU ALAKA

Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace
Ilimi

Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace

June 20, 2026
Hukumar Ilimin Bai-ɗaya Ta Jihar Yobe Ta Raba Kayan Karatu
Ilimi

Hukumar Ilimin Bai-ɗaya Ta Jihar Yobe Ta Raba Kayan Karatu

June 20, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund
Ilimi

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Next Post
Fursunoni 12 Sun Tsere Daga Gidan Yari A Jihar Kogi

Fursunoni 12 Sun Tsere Daga Gidan Yari A Jihar Kogi

LABARAI MASU NASABA

Ƙungiyar NPCF Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Ga Tinubu

Ƙungiyar NPCF Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Ga Tinubu

June 25, 2026
Firaministan Sin Ya Halarci Taron Tattaunawa Da Wakilan ‘Yan Kasuwa Mahalarta Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na DAVOS

Firaministan Sin Ya Halarci Taron Tattaunawa Da Wakilan ‘Yan Kasuwa Mahalarta Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na DAVOS

June 25, 2026
Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

June 25, 2026
Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

June 25, 2026
An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

June 25, 2026
APC Ta Dage Yakin Zaben Shugaban Kasarta A Kano

An Dakatar Da Shugaban APC Na Kebbi Da Kwamishina Kan Zaɓen Cike Gurbin Zuru

June 25, 2026
Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa — Atiku

June 25, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.