• English
  • Business News
Monday, September 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [7]

by Nuhu Ubale Ibrahim
6 months ago
in Addini, Bakon Marubuci, Ilimi
0
Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai

Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai

Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

الشُّكْرُبِاللِّسَانِ: هُوَ الثَّنَاءُ عَلَى الْمُنْعِمِ، وَالتَّحَدُّثُ بِالنِّعَمِ. قَالَ رَسُولُ اللَّهِ صَلَّى اللَّهُ عَلَيْهِ وَسَلَّمَ: “التَّحَدُّثُ بِالنِّعَمِ شُكْرٌ”. وَالشُّكْرُ بِالْجَوَارِحِ: هُوَ الْعَمَلُ بِطَاعَةِ اللَّهِ، وَتَرْكُ مَعَاصِيهِ. وَالشُّكْرُ بِالْقَلْبِ: هُوَ مَعْرِفَةُ مِقْدَارِ النِّعْمَةِ، وَالْعِلْمُ بِأَنَّهَا مِنَ اللَّهِ وَحْدَهُ، وَالْعِلْمُ بِأَنَّهَا تَفَضُّلٌ، لَا بِاسْتِحْقَاقِ الْعَبْدِ.

Fassara:

“ Godiya ga Allah da harshe: Na nufin yabon Mai ni’ima da kuma bayyana ni’imomin da ya bayar. Manzon Allah (S.A.W) ya ce: “Bayyana ni’imomi yana daga cikin godiya.” Godiya da gaɓɓai kuma: Na nufin yin aiki da biyayya ga Allah da barin saɓa Masa. Godiya da zuciya kuma: Yana nufin sanin girman ni’ima da fahimtar cewa daga Allah take Shi kaɗai, kuma da sanin cewa yana bayar da ita ne a matsayin kyauta, ba don bawa ya cancanta ba.”

  • Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [3]
  • Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [5]

Fashin Baƙi:

Wannan magana ta Ibnu Juzai Allah Ya yi masa rahama, tana bayani ne a kan ma’anar godiya ga Allah (wato ash-Shukru) da sassanta uku da take da su:

Labarai Masu Nasaba

Ɗalibai 750 Sun Amfana Da Bashin Karatu Na Naira Milyan 32.14 A Jihar Gombe

Kwamitin JAMB Ya Bankaɗo Magudin Jarabawa A 2025 UTME

1. Godiya da harshe:
Wannan yana nufin yabon Allah da faɗar ni’imominsa da kuma ambatonsa a cikin kalmomi. Wannan yana da muhimmanci saboda yana nuni da cewa mutum ya gane cewa Allah ne mai bayar da ni’ima. Hadisin da aka kawo yana nuna cewa mutum idan ya bayyana ni’imomin Allah, to yana cikin masu godiya. Wannan na iya kasancewa ta hanyar zikirai, du’a’i, da yabonsa da albarkar da yake bayarwa, da cewa Allah Ya yi min ni’ima iri kaza da kaza.

2. Godiya da gaɓɓai:
Wannan yana nufin amfani da dukkan gabban jiki wajen yin biyayya ga Allah da nisantar saɓon Sa. Misali, idan mutum yana da lafiyar jiki, to ya yi amfani da lafiyar wajen aikata kyawawan ayyuka kamar sallah, azumi, sadaƙa, da taimakon jama’a. Idan kuma mutum yana da arziki, ya yi amfani da shi wajen tallafa wa marasa hali da hidimtawa addini. Wannan yana tabbatar da cewa godiya ga Allah ba kawai yana cikin harshe ba, har ma yana cikin aiki.

3. Godiya da zuciya:
Wannan yana da alaƙa da imani da ilimi. Yana nufin mutum ya gane cewa duk wata ni’ima daga Allah take, ba wai saboda ya cancanta a ba shi ba saboda wani abu da ya yi wa Allah, a a sai dai domin Allah yana da rahama da falala da jin ƙai. Wannan yana hana girman kai da alfahari, domin mutum zai fahimci cewa Allah Yana bayar da ni’ima a matsayin kyauta, ba lallai ne saboda ibadarsa ba. Wannan yana ƙarfafa tawali’u da jin haƙuri idan mutum bai samu abin da yake so ba.

A taƙaice, maganar Ibnu Juzai tana koyar da cewa godiya ba kawai fadar “Alhamdulillahi” ba ce kawai, a a, tana da sassa guda uku: da suka haɗa da harshe, da aiki, da kuma zuciya. Idan mutum yana godiya ta waɗannan hanyoyi, to zai zama cikakken mai godiya ga Allah. Wannan yana ƙarfafa imani, yana ƙara ni’ima, kuma yana kusantar da bawa ga Ubangijinsa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Abu Razina Nuhu Ubale PakiAl-qur'aniAlƙur’aniIbnu JuzaiRamadanTafsiriTafsirin Alƙur’aniTafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Ba Za Ta Taba Amincewa Da Ayyukan ’Yan Aware Ba 

Next Post

Na Cire Tallafin Mai Ne Domin Kare Makomar Matasan Nijeriya —Tinubu

Related

Ɗalibai 750 Sun Amfana Da Bashin Karatu Na Naira Milyan 32.14 A Jihar Gombe
Ilimi

Ɗalibai 750 Sun Amfana Da Bashin Karatu Na Naira Milyan 32.14 A Jihar Gombe

15 hours ago
Kwamitin JAMB Ya Bankaɗo Magudin Jarabawa A 2025 UTME
Ilimi

Kwamitin JAMB Ya Bankaɗo Magudin Jarabawa A 2025 UTME

7 days ago
ASUU
Ilimi

Malaman Jami’o’i Sun Zama Abin Tausayi —Kungiyar ASUU

1 week ago
Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai
Da ɗumi-ɗuminsa

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai

1 week ago
Ranar Hausa: Ba Ka Iyawa Duk Dagewarka Kuma Ba A Yaba Maka
Bakon Marubuci

Ranar Hausa: Ba Ka Iyawa Duk Dagewarka Kuma Ba A Yaba Maka

2 weeks ago
Lambar Yabo Ta CON: Buni Ya Zama Zinare Bashi Da Maboya
Ilimi

NTIC Ta Jinjina Wa Gwamna Buni Kan Taimako A Bangaren Ilimi

2 weeks ago
Next Post
Gwamnati Ta Dakatar Da Daraktocin Hukumar Sufurin Jiragen Sama 5 Sa’o’i Kadan Bayan Sauke Shugabanninsu

Na Cire Tallafin Mai Ne Domin Kare Makomar Matasan Nijeriya —Tinubu

LABARAI MASU NASABA

Tarihin Ƴan Majalisar Farko Kafin Da Kuma Zamanin Mulkin Mallaka (3)

Tarihin Ƴan Majalisar Farko Kafin Da Kuma Zamanin Mulkin Mallaka (3)

September 14, 2025
Sin Da Amurka Sun Fara Gudanar Da Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Madrid

Sin Da Amurka Sun Fara Gudanar Da Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Madrid

September 14, 2025
An Gano Gawar Yarinyar da Ruwan Sama Ya Tafi Da ita A Zariya

An Gano Gawar Yarinyar da Ruwan Sama Ya Tafi Da ita A Zariya

September 14, 2025
Kano Pillars Ta Samu Nasarar Farko A Gasar Firimiyar Nijeriya Ta Bana

Kano Pillars Ta Samu Nasarar Farko A Gasar Firimiyar Nijeriya Ta Bana

September 14, 2025
Za A Kaddamar Da Fim Mai Taken 731 A Sassan Duniya

Za A Kaddamar Da Fim Mai Taken 731 A Sassan Duniya

September 14, 2025
Lauyoyi Biyu Sun Janye Daga Kai Jaafar Jaafar Ƙara, Sun Ce An Sanya Sunayensu Ba Bisa Ƙa’ida Ba

Lauyoyi Biyu Sun Janye Daga Kai Jaafar Jaafar Ƙara, Sun Ce An Sanya Sunayensu Ba Bisa Ƙa’ida Ba

September 14, 2025
Kasar Sin Na Samarwa Duniya Damammaki A Fannin Hada-hadar Ba Da Hidima

Kasar Sin Na Samarwa Duniya Damammaki A Fannin Hada-hadar Ba Da Hidima

September 14, 2025
Duba Ga Kwaɗayi Da Son Duniya A Tsakanin Matan Wannan Zamanin

Duba Ga Kwaɗayi Da Son Duniya A Tsakanin Matan Wannan Zamanin

September 14, 2025
Jagororin Kamfanonin Ketare Sun Nuna Gamsuwa Dangane Da Zuba Jari A Kasar Sin

Jagororin Kamfanonin Ketare Sun Nuna Gamsuwa Dangane Da Zuba Jari A Kasar Sin

September 14, 2025
Bayan Fara Kamen Mabarata, An Samu Dalar Amurka, Wuƙa A Kwara

Bayan Fara Kamen Mabarata, An Samu Dalar Amurka, Wuƙa A Kwara

September 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.