ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [3]

by Nuhu Ubale Ibrahim
1 year ago
Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai

Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai

Abubuwan da Suke Hana Mutum bin Allah:

“القَواطِعُ عَنِ اللهِ أَربَعَةٌ: الشَّيطانُ، وَالنَّفسُ، وَالدُّنيا، وَالخَلقُ. فَعِلاجُ الشَّيطانِ: الاِستِعاذَةُ وَالمُخالَفَةُ لَهُ، وَعِلاجُ النَّفسِ: بِالقَهرِ، وَعِلاجُ الدُّنيا: بِالزُّهدِ، وَعِلاجُ الخَلقِ: بِالاِنقِيادِ وَالعُزلَةِ.”

Fassara:

ADVERTISEMENT

“Abubuwa huɗu ne ke katange mutum daga bin Allah: Shaidan da son zuciya da duniya, da halittu (wato mutane). Maganin Shaiɗan shi ne: saɓa masa da kuma neman tsarin Allah a kansa, maganin son zuciya kuma shi ne: fin ƙarfin ta da taƙwara ta ta bi gaskiya. Maganin duniya kuma : shi ne guje wa ƙyaleƙyalenta da ruɗinta. Maganin mutane kuma: karkata ga Allah Shi kaɗai da nisanta kai yin biyayya da nisanta kai daga mutane (ɓatagari)” Kitãbu at-Tashīlu Li’ulūmi at-Tanzil [1/30].

  • Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [2]
  • Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [4]

Fashin Baƙi:

LABARAI MASU NASABA

An Tantance Masu Neman Aikin Koyarwa 500 A Jigawa

JAMB Ta Ƙara Wa’adin Amincewar Guraben Karatu Zuwa 30 Satumba

Wannan magana ta al-imam Ibnu Juzai tana bayani ne kan abubuwa huɗu da ke hana mutum bin Allah da kuma yadda za a magance kowanne daga cikinsu. Ga ƙarin haske akan haka:

1. Shaiɗan: Shaiɗan shi ne abokin gaban mutum na ƙoli tun daga haihuwarsa har mutuwarsa. A matsayinsa na maƙiyi, burinsa shi ne ya ɓatar da mutum daga bin Allah. Yana amfani da hanyoyi daban-daban kamar waswasi, da sanya shubuha, da ƙarya, da kawar da zuciya daga ibada, da sanya shakku a cikin imani, da sauran makirce-makircensa. Allah Ya umurce mu da kada mu bibiyi tafarkin shaiɗan a rayuwarmu.

Maganin Shaiɗan: Babban maganin Shaiɗan shi ne neman tsari da kariya a kansa a wurin Allah, da sɓa masa, Wato mutum ya yi ƙoƙarin yin akasin abin da Shaiɗan ke umarta. Idan Shaiɗan yana kiran mutum zuwa ga zunubi, ya yi ƙoƙarin kaucewa.

2. Son Zuciya: Zuciyar mutum tana da buƙatu da sha’awa, kuma tana iya karkatar da shi daga tafarkin gaskiya. Idan mutum bai kula ba, zuciyarsa za ta janyo masa son abin da bai dace ba, ko kuma nuna ƙyama ga abin da Allah ya shar’anta wanda hakan zai kai mutum da barin Allah da addinsa. Don haka; dole ne mutum ya kula da gyaran zuciyarsa.

Maganin Son Zuciya: Maganin son zuciya shi ne mutum ya fi ƙarfin ta, Wato mutum ya tilasta wa zuciyarsa bin gaskiya, ko da kuwa tana son akasin haka. Tanƙwara ta ta bi gaskiya, yana nufin horar da zuciya kan gaskiya da bin umurnin Allah. Hakan na faruwa ne ta hanyar tilasta wa kai yin biyayya, ta hanyar salla da azumi, da ambaton Allah, da kasancewa cikin kyawawan ayyuka tare da addu’a Allah Ya tsarkake ta.

3. Duniya: Duniya tana da ruɗi da ƙawanyar ƙyaleƙyale, tana janyo hankalin mutum zuwa ga jin daɗi kamar samun dukiya, ko matsayi, da sauran abubuwan da ke iya karkatar da shi daga bin Allah. Allah ya bayyana cewa duniya ruɗi a wurare daban-daban a cikin Alƙur’ani, hakanan Hadisai masu yawa sun yi bayani a kan ruɗin da duniya take yi wa mutane.

Maganin Duniya: Guje wa ƙyaleƙyalenta da ruɗinta, Wato mutum ya fahimci cewa duniya ba ta da daraja idan aka kwatanta da lahira, kuma bai kamata ya jefa kansa cikin ruɗinta ba, domin ba ta da tabbas. Mutum ya kasance mai tsoron Allah da ƙoƙarin bin dokokinsa a kowane hali.

4. Halittu (Mutane): Mutane na iya zama sanadin da zai hana mutum bin Allah, musamman idan yana koyi da su a kan abin da ba daidai ba. Akwai waɗanda za su janyo mutum cikin halayen banza ko su hana shi aikata alheri, ta yadda hakan zai lalata masa zuciya, domin zama da maɗaukin kanwa yana kawo farin kai.

Maganin Mutane: Karkata ga Allah Shi kaɗai, wato mutum ya yi ƙoƙarin maida hankalinsa ga Allah kaɗai, ba wai ya dogara da mutane ko kuma ya dinga yin abubuwa don faranta musu ba. Hakanan mutum ya nilisanci biyayya ga mutane idan a cikin abin da yake ɓata; Idan mutane suna jagorantar mutum zuwa ga ɓarna, ya kamata ya guje musu.

Zaɓar abokai nagari yana taimaka wa mutum wajen zama nagari. Ya zaɓi waɗanda za su taimaka masa wajen bin Allah, ba waɗanda za su janye shi zuwa ga halaka ba.

Daga
Nuhu Ubale Ibrahim
+ postsBio
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    Layya Babbar Ibada A Musulunci Na 1
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    Karamar Sallah: Sallar Idi A Wajen Musulmi…
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    SAHUR [Falalarsa Da Fa’idojinsa] Na 23
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    SAHUR [Falalarsa Da Fa’idojinsa] Na 22

MASU ALAKA

Daga
Ilimi

An Tantance Masu Neman Aikin Koyarwa 500 A Jigawa

August 31, 2026
Daga
Ilimi

JAMB Ta Ƙara Wa’adin Amincewar Guraben Karatu Zuwa 30 Satumba

August 29, 2026
Kosan Waka Ya Rasu, Gwamnan Kano Ya Jajanta Wa Iyalansa
Ta’aziyya

Kosan Waka Ya Rasu, Gwamnan Kano Ya Jajanta Wa Iyalansa

August 2, 2026
Next Post
NNPC Ya Samu Ribar Naira Tiriliyan 3 A 2023

NNPC Da Dangote Na Shirin Ƙulla Sabuwar Yarjejeniya Kan Sayen Ɗanyen Mai

LABARAI MASU NASABA

Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.