• English
  • Business News
Tuesday, July 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [8]

by Nuhu Ubale Ibrahim
4 months ago
in Addini, Bakon Marubuci, Ilimi
0
Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai

Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai

Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

“التَّقْوَى مَصْدَرٌ مُشْتَقٌّ مِنَ الوِقَايَةِ، مَعْنَاهَا الخَوْفُ وَالِالْتِزَامُ بِطَاعَةِ اللهِ وَتَرْكُ مَعَاصِيهِ، فَهِيَ جَامِعَةٌ لِكُلِّ خَيْرٍ”

Fassara:

“Takawa kalma ce da aka samo daga ‘kariya’ Ma’anar taƙawa shi ne jin tsoron Allah, da lazimtar biyayya ga Allah da barin saɓa Masa. Taƙawa ta tattaro dukan alherai gaba ɗaya. “ Duba Kitãbu at-Tashīlu fi Ulūmi at-Tanzil [1/17]

  • Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [6]
  • Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [7]

Fashin Baƙi:

Maganar babban malami Ibnu Juzai Allah Ya yi masa rahama, tana bayyana ma’anar taƙawa a harshen Larabci, da kuma harshe na na shari’a.

Labarai Masu Nasaba

Abinda Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (9)

Hadarin Da Ke Kunshe Da Jin Bangare Daya Na Labari

Taƙawa a harshen Larabci: tana nufin ‘kariya’. Attaƙawa (التَّقْوَى) ta samo asali daga wiƙãya (وِقَايَة), wacce ke nufin katanga ko kariya. Wannan yana nuna cewa taƙawa tana nufin kare bawa daga azabar Allah ta hanyar bin umarninsa da guje wa saɓonsa.

Ma’anar Taƙawa a Shari’a: Ibnu Juzai al-Kalbi ya fassara taƙawa da jin tsoron Allah da lazimtar biyayya gare shi da barin saɓa masa. Wannan yana daidai da abin da malamai kamar Ibn Rajab da al-Gazzali suka bayyana, cewa taƙawa ba wai tsoro kaɗai ba ne, har da tsoron da ke haddasa aiki da biyayya.

Jin tsoron Allah: Wannan yana nufin mutum ya san Allah da girmansa, wanda hakan ke sa shi jin tsoron yin abin da zai jawo fushinsa.

Lazimtar biyayya: Wato mutum yana da nufin aikata duk abin da Allahda Manzonsa suka yi umurni da shi.

Barin saɓo: Wato mutum yana nisantar duk wani abu da zai jawo fushin Allah na magana ko aiki, na fili da na ɓoye.

Faidojin Taƙawa:

Taƙawa tana da fa’idoji masu yawa, da suka haɗa da: Samun ƙauna daga Allah da kankarar zunubai da girmama lada da mutum zai samu. Taƙawa sababi ce ta samun albarkatun Allah, da toshe kofofin sharri.

Taƙawa tana sanya mutum ya sami mafita a rayuwarsa duk rintsin da mutum zai shiga. Taƙawa tana sanya al’amuran bawa su zama masu sauƙi. Taƙawa tana sanya mutum ya sami rabauta da rahamar Allah, tana kuma sanya mutum ya sami tsira.

Taƙawa tana sanya mutum ya girmama Allah da kuma sanya mutum ya zama adali mai nagarta a cikin al’umma, sannan tana sanya mutum ya nisanci zalunci tare da lazimtar gaskiya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Abu Razina Nuhu Ubale PakiAl-qur'aniAlƙur’aniIbnu JuzaiRamadanTafsiriTafsirin Alƙur’aniTafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai
ShareTweetSendShare
Previous Post

Nazarin CGTN: Kasar Sin Na Bayar Da Gudunmuwa Wajen Warware Batun Nukiliyar Iran

Next Post

An Cafke Wadanda Ake Zargi Da Daba Wa Dan Wasan Nijeriya Mazaunin Kasar Ireland Wuka Har Lahira

Related

Abinda Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (9)
Ilimi

Abinda Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (9)

3 days ago
Hadarin Da Ke Kunshe Da Jin Bangare Daya Na Labari
Bakon Marubuci

Hadarin Da Ke Kunshe Da Jin Bangare Daya Na Labari

4 days ago
AI Zai Maye Gurbin Ayyuka Miliyan 92 A Duniya – Farfesa Pate
Ilimi

AI Zai Maye Gurbin Ayyuka Miliyan 92 A Duniya – Farfesa Pate

1 week ago
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (8)
Ilimi

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (8)

1 week ago
Yawaitar Al’umma: Martanin Karl Marx Ga Rabaran Malthus
Bakon Marubuci

Yawaitar Al’umma: Martanin Karl Marx Ga Rabaran Malthus

2 weeks ago
Maraba Da Shekarar Hijirah Ta 1447: Manzon Allah (SAW) Zai Cika Shekara 1,500 Da Haihuwa A Shekarar (1)
Addini

Maraba Da Shekarar Hijirah Ta 1447: Manzon Allah (SAW) Zai Cika Shekara 1,500 Da Haihuwa A Shekarar (1)

2 weeks ago
Next Post
An Cafke Wadanda Ake Zargi Da Daba Wa Dan Wasan Nijeriya Mazaunin Kasar Ireland Wuka Har Lahira

An Cafke Wadanda Ake Zargi Da Daba Wa Dan Wasan Nijeriya Mazaunin Kasar Ireland Wuka Har Lahira

LABARAI MASU NASABA

HOTUNA: An Tsaurara Tsaro A Gidan Buhari Da Ke Daura

HOTUNA: An Tsaurara Tsaro A Gidan Buhari Da Ke Daura

July 15, 2025
Trump Ya Bai Wa Rasha Kwanaki 50 Ta Kawo Ƙarshen Yaƙinta Da Ukraine

Trump Ya Bai Wa Rasha Kwanaki 50 Ta Kawo Ƙarshen Yaƙinta Da Ukraine

July 15, 2025
Tinubu Zai Tarbi Gawar Buhari A Daura Don Yi Mata Jana’iza

Tinubu Zai Tarbi Gawar Buhari A Daura Don Yi Mata Jana’iza

July 15, 2025
Na Yafe Wa Buhari Duk Abin Da Ya Min – Buba Galadima

Na Yafe Wa Buhari Duk Abin Da Ya Min – Buba Galadima

July 15, 2025
Ministan Wajen Kasar Sin Ya Gana Da Takwaransa Na Rasha 

Ministan Wajen Kasar Sin Ya Gana Da Takwaransa Na Rasha 

July 14, 2025
Dangote Na Neman Izinin Gina Babbar Tashar Jiragen Ruwa Mafi Zurfi A Nijeriya

Dangote Na Neman Izinin Gina Babbar Tashar Jiragen Ruwa Mafi Zurfi A Nijeriya

July 14, 2025
Sin Da Amurka Na Kokarin Tabbatar Da Ci Gaban Da Aka Samu Na Yarjejeniyar London

Sin Da Amurka Na Kokarin Tabbatar Da Ci Gaban Da Aka Samu Na Yarjejeniyar London

July 14, 2025
Sarkin Maroko Ya Aike Da Ta’aziyya Ga Nijeriya Bisa Rasuwar Buhari

Sarkin Maroko Ya Aike Da Ta’aziyya Ga Nijeriya Bisa Rasuwar Buhari

July 14, 2025
Sin Na Maraba Da ’Yan Jaridar Duniya Da Su Halarci Bikin Cika Shekaru 80 Da Cimma Nasarar Yakin Kin Harin Japan Da Na Tafarkin Murdiya 

Sin Na Maraba Da ’Yan Jaridar Duniya Da Su Halarci Bikin Cika Shekaru 80 Da Cimma Nasarar Yakin Kin Harin Japan Da Na Tafarkin Murdiya 

July 14, 2025
Osimhen Na Dab Da Komawa Galatasaray Na Dindindin

Osimhen Na Dab Da Komawa Galatasaray Na Dindindin

July 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.