• English
  • Business News
Monday, October 20, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [8]

by Nuhu Ubale Ibrahim
7 months ago
Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai

Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai

“التَّقْوَى مَصْدَرٌ مُشْتَقٌّ مِنَ الوِقَايَةِ، مَعْنَاهَا الخَوْفُ وَالِالْتِزَامُ بِطَاعَةِ اللهِ وَتَرْكُ مَعَاصِيهِ، فَهِيَ جَامِعَةٌ لِكُلِّ خَيْرٍ”

Fassara:

“Takawa kalma ce da aka samo daga ‘kariya’ Ma’anar taƙawa shi ne jin tsoron Allah, da lazimtar biyayya ga Allah da barin saɓa Masa. Taƙawa ta tattaro dukan alherai gaba ɗaya. “ Duba Kitãbu at-Tashīlu fi Ulūmi at-Tanzil [1/17]

  • Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [6]
  • Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [7]

Fashin Baƙi:

Maganar babban malami Ibnu Juzai Allah Ya yi masa rahama, tana bayyana ma’anar taƙawa a harshen Larabci, da kuma harshe na na shari’a.

LABARAI MASU NASABA

Ɗaliban Jihar Gombe Sun Samu Ƙarin Kashi 100 Na Kuɗin Tallafin Karatu

Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma

Taƙawa a harshen Larabci: tana nufin ‘kariya’. Attaƙawa (التَّقْوَى) ta samo asali daga wiƙãya (وِقَايَة), wacce ke nufin katanga ko kariya. Wannan yana nuna cewa taƙawa tana nufin kare bawa daga azabar Allah ta hanyar bin umarninsa da guje wa saɓonsa.

Ma’anar Taƙawa a Shari’a: Ibnu Juzai al-Kalbi ya fassara taƙawa da jin tsoron Allah da lazimtar biyayya gare shi da barin saɓa masa. Wannan yana daidai da abin da malamai kamar Ibn Rajab da al-Gazzali suka bayyana, cewa taƙawa ba wai tsoro kaɗai ba ne, har da tsoron da ke haddasa aiki da biyayya.

Jin tsoron Allah: Wannan yana nufin mutum ya san Allah da girmansa, wanda hakan ke sa shi jin tsoron yin abin da zai jawo fushinsa.

Lazimtar biyayya: Wato mutum yana da nufin aikata duk abin da Allahda Manzonsa suka yi umurni da shi.

Barin saɓo: Wato mutum yana nisantar duk wani abu da zai jawo fushin Allah na magana ko aiki, na fili da na ɓoye.

Faidojin Taƙawa:

Taƙawa tana da fa’idoji masu yawa, da suka haɗa da: Samun ƙauna daga Allah da kankarar zunubai da girmama lada da mutum zai samu. Taƙawa sababi ce ta samun albarkatun Allah, da toshe kofofin sharri.

Taƙawa tana sanya mutum ya sami mafita a rayuwarsa duk rintsin da mutum zai shiga. Taƙawa tana sanya al’amuran bawa su zama masu sauƙi. Taƙawa tana sanya mutum ya sami rabauta da rahamar Allah, tana kuma sanya mutum ya sami tsira.

Taƙawa tana sanya mutum ya girmama Allah da kuma sanya mutum ya zama adali mai nagarta a cikin al’umma, sannan tana sanya mutum ya nisanci zalunci tare da lazimtar gaskiya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

gombe
Ilimi

Ɗaliban Jihar Gombe Sun Samu Ƙarin Kashi 100 Na Kuɗin Tallafin Karatu

October 18, 2025
Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma
Ilimi

Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma

October 18, 2025
ASUU
Ilimi

Cikin Wata 9 Farfesoshi 309 Sun Bar Aiki A Jami’o’in Gwamnati, In Ji ASUU

October 18, 2025
Next Post
An Cafke Wadanda Ake Zargi Da Daba Wa Dan Wasan Nijeriya Mazaunin Kasar Ireland Wuka Har Lahira

An Cafke Wadanda Ake Zargi Da Daba Wa Dan Wasan Nijeriya Mazaunin Kasar Ireland Wuka Har Lahira

LABARAI MASU NASABA

Kano Derby: Barau FC Ta Doke Kano Pillars A Karon Farko A Tarihin Gamuwarsu

Kano Derby: Barau FC Ta Doke Kano Pillars A Karon Farko A Tarihin Gamuwarsu

October 19, 2025
Binciken CGTN: An Fitar Da Sakamakon Jin Ra’ayin Jama’a Dangane Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Kolin JKS Na 20

Binciken CGTN: An Fitar Da Sakamakon Jin Ra’ayin Jama’a Dangane Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Kolin JKS Na 20

October 19, 2025
Arewa Ta Samu Kashi 56% Na Muƙaman Gwamnatin Tinubu — Shugaban FCC

Arewa Ta Samu Kashi 56% Na Muƙaman Gwamnatin Tinubu — Shugaban FCC

October 19, 2025
Xi Jinping Ya Mika Sakon Taya Cheng Li-wun Murnar Zama Shugabar Jam’iyyar KMT Ta Kasar Sin

Xi Jinping Ya Mika Sakon Taya Cheng Li-wun Murnar Zama Shugabar Jam’iyyar KMT Ta Kasar Sin

October 19, 2025
Ɗan Jarida Ibrahim Ɗan’uwa Rano Ya Shaƙi Iskar Ƴanci Bayan Tsare Shi

Ɗan Jarida Ibrahim Ɗan’uwa Rano Ya Shaƙi Iskar Ƴanci Bayan Tsare Shi

October 19, 2025
Tie Ning Ta Halarci Bikin Bude Taron Karawa Juna Sani Na ‘Yan Majalisun Dokokin Kasashen Afirka

Tie Ning Ta Halarci Bikin Bude Taron Karawa Juna Sani Na ‘Yan Majalisun Dokokin Kasashen Afirka

October 19, 2025
Ƴansanda Sun Kama Ɗan Jarida A Kano Bisa Zargin Ɓata Suna

Ƴansanda Sun Kama Ɗan Jarida A Kano Bisa Zargin Ɓata Suna

October 19, 2025
Amfanin Yawan Shan Ruwa Da Kuma Illolin Rashin Yawan Sha

Amfanin Yawan Shan Ruwa Da Kuma Illolin Rashin Yawan Sha

October 19, 2025
Xinjiang Ta Janyo Karin Jari A Rubu’i Uku Na Farkon Shekarar Nan

Xinjiang Ta Janyo Karin Jari A Rubu’i Uku Na Farkon Shekarar Nan

October 19, 2025
Yadda Shagwaɓa Kananan Yara Da Kudi Ke Shafar Tarbiyyarsu

Yadda Shagwaɓa Kananan Yara Da Kudi Ke Shafar Tarbiyyarsu

October 19, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.