• English
  • Business News
Friday, June 20, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [9]

by Nuhu Ubale Ibrahim
3 months ago
in Addini, Bakon Marubuci, Ilimi
0
Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai

Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai

Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

درجاتُ التَّقوى خمسٌ: أنْ يَتَّقِيَ العبدُ الكفرَ، وهو مقامُ الإسلامِ، وأنْ يَتَّقِيَ المعاصيَ والحرماتِ، وهو مقامُ التَّوبةِ، وأنْ يَتَّقِيَ الشُّبُهاتِ، وهو مقامُ الوَرَعِ، وأنْ يَتَّقِيَ المُباحاتِ، وهو مقامُ الزُّهدِ، وأنْ يَتَّقِيَ حضورَ غيرِ اللهِ على قلبِهِ، وهو مقامُ المُشاهدةِ.

Fassara:
“ Matakan taƙawa guda biyar ne: kare kai daga kafirci; Wannan shi ne matakin Musulunci. Kare kai daga aikata sɓon Allah da haram; Wannan shi ne matakin tuba. Kare kai daga shubuha; Wannan shi ne matakj na tsantseni. Kare kai daga abubuwan da aka halatta; Wannan shi ne matakin gudun duniya. Kare zuciya daga duk wani abu da ba Allah ba; Wannan shi ne matakin bautar Allah kamar kana ganin Sa.” Duba Kitãbu at-Tashīlu Li’ulūmi at-Tanzil [1/36]

  • Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [8]
  • Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [7]

Fashin Baƙi:
Wannan magana ta Ibn Juzai al-Kalbi tana bayani ne kan matakan da mutum zai bi domin kaiwa ga matakin taƙawa na ƙoli, daga mafi ƙasa zuwa mafi girma. Bari mu yi nazari da sharhi akan kowanne mataki daga cikinsu:

Mataki na Ɗaya: Kare kai daga kafirci; wato matakin Musulunci, wannan matakin yana nufin cewa musulunci shi ne matakin farko na taƙawa. Duk wanda zai zama mai taƙawa, dole ne ya fara da tabbatar da imani ga Allah, ya yarda da Manzonsa (SAW), kuma ya kauce wa duk wani nau’in kafirci. Wannan yana nufin mutum ya ƙudurce kalmar shahada tare da furta ta da kuma aiki da ita. Ya shaida shahada, wanda ita ce tushen addini. Idan babu wannan, to, duk wani ƙoƙari da mutum zai yi a kan taƙawa ba zai amfane shi ba.

Mataki na Biyu: Kare kai daga aikata saɓon Allah da aikata haram, wato matakin tuba; wannan matakin yana bayani ne akan wajabcin nisantar haram da kuma tuba daga zunubi. Idan mutum ya tabbatar da imani, mataki na gaba shi ne ya kiyaye dokokin Allah ta hanyar kauce wa haram. Duk wanda bai nisanci abin da Allah ya haramta ba, yana nuna gazawarsa a cikin taƙawa. Wannan matakin yana bayyana cewa taƙawa ba kawai a zuciya take ba, sai an aiwatar da ita a aikace.

Labarai Masu Nasaba

Wata Sabuwa: Malaman Jami’ar Tarayya A Kano Sun ƙi Amince Wa Da Zaɓen Sabon VC

Dabi’a: Yadda Ake Gini Da Rusa Ta 

Mataki na Uku: Kare kai daga shubuha; wato matakin tsantseni, shubuha na nufin abubuwan da ba a tabbatar da halacci ko haramcinsu ba. Akwai wani mataki da ya fi kauce wa haram, wato kauce wa abubuwan da ke da shakku. Annabi (SAW) ya ce:
” Lalle halal a bayyane take, kuma lalle haram a bayyane yake, amma akwai wasu abubuwa masu rikitarwa a tsakanin su waɗanda mutane da yawa ba su san su ba, wanda ya nisanci shubuha, to ya kare addininsa da mutuncinsa.” Bukhari da Muslim ne suka ruwaito. Saboda haka, matakin tsantseni yana nufin mutum ya kiyaye kansa daga duk wani abu da zai iya kai shi ga haram, koda kuwa ba a tabbatar da haramcinsa ba.

Mataki na Huɗu: Kare kai daga abubuwan da aka halatta; wato matakin gudun duniya. Wannan matakin ya fi zurfi domin yana nuni da zuhudu (wato yin watsi da son duniya). Duk da cewa akwai halal da aka ba wa mutum damar amfani da su, sai dai matakin mafi girman taƙawa shi ne rage kwaɗayin duniya domin kauce wa duk wani abu da zai shagaltar da mutum daga bautar Allah. Wannan ya dace da hadisin Annabi (SAW) da ya ce: “Ka kasance a duniya kamar baƙo, ko kuma kamar wani matafiyi.” Bukhari ne ya ruwaito. Don haka, matakin gudun duniya yana nuna cewa taƙawa ta gaskiya ba kawai da nisantar haram ba ce, har ma da rage dogaro da duniya don samun kyakkyawan sakamako a lahira.

Mataki na Biyar: Kare zuciya daga duk wani abu da ba Allah ba. Wato matakin bautar Allah kamar kana ganin Sa. Wannan shi ne matakin ihsani wanda Annabi (SAW) ya bayyana a hadisin Jibrilu da cewa:
“Ihsan shi ne ka bauta wa Allah kamar kana ganin Sa, idan ba ka ganin Sa, to Shi yana ganin ka.” Muslim ne ya ruwaito. Wannan matakin yana nuna tsarkake zuciya daga kowanne abu da zai shagaltar da mutum daga Allah. Ana son mai taƙawa ya kasance zuciyarsa a koyaushe a tare da Allah, yana ƙaunar Sa fiye da komai. Wannan matakin ne mafi girma a taƙawa, domin yana nuni da mutum ya kasance kullum yana jin tsoron Allah tare da ƙaunar Sa, ba wai kawai yana gudun azabarsa ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Abu Razina Nuhu Ubale PakiAl-qur'aniAlƙur’aniIbnu JuzaiRamadanTafsiriTafsirin Alƙur’aniTafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ba Don Tarbiyantar Da Mutane Nake Yin Fim Ba -Amina Shehu Lulu

Next Post

Ko Barcelona Ta Kama Hanyar Lashe Gasar Laliga Ta Bana?

Related

Wata Sabuwa: Malaman Jami’ar Tarayya A Kano Sun ƙi Amince Wa Da Zaɓen Sabon VC
Ilimi

Wata Sabuwa: Malaman Jami’ar Tarayya A Kano Sun ƙi Amince Wa Da Zaɓen Sabon VC

5 days ago
Dabi’a: Yadda Ake Gini Da Rusa Ta 
Bakon Marubuci

Dabi’a: Yadda Ake Gini Da Rusa Ta 

5 days ago
Hajjin Bana: Falalar Tsayuwar Arfa
Manyan Labarai

Hajjin Bana: Falalar Tsayuwar Arfa

2 weeks ago
Gwamnatin Kano Ta Ba Da Hutun Makaranta Domin Bukukuwan Sallah
Ilimi

Gwamnatin Kano Ta Ba Da Hutun Makaranta Domin Bukukuwan Sallah

3 weeks ago
SULEJA – An Ci Moriyar Ganga (3)
Bakon Marubuci

SULEJA – An Ci Moriyar Ganga (3)

3 weeks ago
Wasu ‘Yan Siyasa Da Jami’an Tsaro Na Taimaka Wa Boko Haram – Zulum
Ilimi

Zulum Ya Ba Da Tallafin Karatu Ga Mata ‘Yan Asalin Jihar Da Suka Samu Maki 250 A JAMB

3 weeks ago
Next Post
Ko Barcelona Ta Kama Hanyar Lashe Gasar Laliga Ta Bana?

Ko Barcelona Ta Kama Hanyar Lashe Gasar Laliga Ta Bana?

LABARAI MASU NASABA

Matsayin Sin Na Bude Kofar Tattalin Arzikinta Ga Duniya Ba Zai Canza Ba

Matsayin Sin Na Bude Kofar Tattalin Arzikinta Ga Duniya Ba Zai Canza Ba

June 20, 2025
Zamfara Ta Zama Jiha Ta Farko Da Ta Ƙaddamar da Tsarin Ilimin Fasahar Zamani

Zamfara Ta Zama Jiha Ta Farko Da Ta Ƙaddamar da Tsarin Ilimin Fasahar Zamani

June 20, 2025
An Kafa Fiye Da Kamfanonin Waje 24,000 A Sin Cikin Watanni 5 Na Farkon Bana

An Kafa Fiye Da Kamfanonin Waje 24,000 A Sin Cikin Watanni 5 Na Farkon Bana

June 20, 2025
Ba Tsoro Ne Yasa Muka Amince Da Sulhu Da Ƴan Bindiga Ba – Gwamnatin Sokoto

Ba Tsoro Ne Yasa Muka Amince Da Sulhu Da Ƴan Bindiga Ba – Gwamnatin Sokoto

June 20, 2025
Kin Biyan Bashi Daga Wasu Manoma Zai Kawo Cikas Ga Noman Shinkafa A Bana – Ɗan Madamin Samaru 

Kin Biyan Bashi Daga Wasu Manoma Zai Kawo Cikas Ga Noman Shinkafa A Bana – Ɗan Madamin Samaru 

June 20, 2025
Ambaliyar Ruwan Mokwa: Masana Sun Shawarci Gwamnati Kan Matakin Kariya A Nan Gaba

Ambaliyar Ruwan Mokwa: Masana Sun Shawarci Gwamnati Kan Matakin Kariya A Nan Gaba

June 20, 2025
Ɗan TikTok Tsulange Ya Shiga Hannu Bisa Wanka Da Rigar Mama A Titi

Ɗan TikTok Tsulange Ya Shiga Hannu Bisa Wanka Da Rigar Mama A Titi

June 20, 2025
GORON JUMA’A 16/05/2025

GORON JUMA’A 20-06-2025

June 20, 2025
Tinubu Zai Zaɓi Mataimakinsa Bayan Taron Jam’iyya – Fadar Shugaban Ƙasa 

Tinubu Zai Zaɓi Mataimakinsa Bayan Taron Jam’iyya – Fadar Shugaban Ƙasa 

June 20, 2025
Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Filato, Mutane 15 Sun Mutu A Bokkos Da Mangu

Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Filato, Mutane 15 Sun Mutu A Bokkos Da Mangu

June 20, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.