ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, July 27, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wakilai Daga Jihohi 19 Sun Isa Ibadan Don Taron PDP Na Ƙasa

by Abubakar Sulaiman
8 months ago
PDP

Wakilai daga jihohi 19 sun isa Ibadan, babban birnin jihar Oyo, a ranar Juma’a, domin halartar taron ƙasa na jam’iyyar PDP wanda za a gudanar a ranar Asabar 15 ga Nuwamba da Lahadi 16 ga Nuwamba. Jihohin da suka halarta sun haɗa da Adamawa, da Akwa Ibom, da Anambra, da Bauchi, da Bayelsa, da Benue, da Borno, da Cross River, da Delta, da Edo, da Ebonyi, da Enugu, da FCT, da Imo, da Kaduna, da Jigawa, da Kano, da Katsina, da kuma Ekiti.

Taron na zuwa ne yayin da jam’iyyar ke fuskantar rikice-rikice na cikin gida da kuma shari’a a kotu. Kwamitin aiki na ƙasa (NWC), ƙarƙashin jagorancin Shugaban jam’iyyar na ƙasa, Umar Damagum, ya dakatar da Sakatare na ƙasa, Sanata Samuel Anyanwu; Sakatare mai Shirya taro, Umar Bature; da Lauyan jam’iyyar na ƙasa, Kamaldeen Ajibade, bisa zargin aikata abubuwan da suka saɓawa jam’iyya. Wannan mataki ya biyo bayan hukuncin kotun tarayya wanda ya dakatar da taron na ɗan lokaci saboda rashin bin ƙa’idojin gudanarwa, ciki har da gazawar isar da sanarwar taron ga INEC.

  • Rikicin PDP: Fiye Da Wakilai 3,000 Ne Za Su Raba Gardama A Babban Taron Jam’iyyar
  • Atiku Ya Fice Daga PDP Saboda Na Ƙi Bari Ya Lalata Mana Jam’iyya – Wike

Sai dai umarnin Alƙali Akintola ya baiwa jam’iyyar dama ta ci gaba da taron. An kammala shirye-shiryen wajen taron a Filin Wasanni na Lekan Salami, inda aka ƙawata shi da launukan jam’iyyar. Ana sa ran wakilai sama da 3,000 daga jihohin tarayya 36 da FCT, tare da shugabanni, masu ruwa da tsaki, da kuma masu sanya ido daga ƙasashen waje zasu halarci taron.

ADVERTISEMENT

Za a gudanar da zaɓen manyan muƙamai na kasa a wannan taro, ciki har da zaɓen Shugaban jam’iyyar na ƙasa, Sakatare, da sauran manyan jami’an NWC da mataimakansu. A wajen taron, aiyuka na tafiya a ƙarshe, inda aka ɗora tallace-tallace da hotunan yaƙin neman zabe a wurare masu muhimmanci a ciki da wajen filin wasa.

An yi hasashen wannan taro a matsayin ɗaya daga cikin masu jawo cece-kuce mafi girma a tarihin PDP, musamman ma ganin cewa wani ɓangare na jam’iyyar ya janye daga halarta, wanda hakan ya ƙara tsananta yanayin siyasar zaɓen.

LABARAI MASU NASABA

2027: Magoya Bayan Tinubu Sun Yi Watsi Da Sukar Takarar Musulmi-Musulmi Da Kwankwaso Ya Yi

Kabiru Gaya Ya Amince Zai Sauya Sheƙa Zuwa APC

PDP
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Tinubu Zai Ƙara Wa Sojoji Albashi Nan Ba Da Jimawa Ba – Ministan Tsaro
  • Abubakar Sulaiman
    Taimakon Ƴan Bindiga: Kotu Ta Yanke Wa Mata 3 Hukuncin Shekaru 14 A Magarƙama
  • Abubakar Sulaiman
    NSCDC Ta Cafke Mutane 2 Da Ake Zargi Da Sace Kayan Titin Jirgin Kasa A Kano
  • Abubakar Sulaiman
    Obi-Kwankwaso Obasanjo Yake Goyon Baya, Amma Atiku Zai Iya Lashe Zabe – Momodu

MASU ALAKA

Kwankwaso Zai Koma ADC Ranar Litinin
Manyan Labarai

2027: Magoya Bayan Tinubu Sun Yi Watsi Da Sukar Takarar Musulmi-Musulmi Da Kwankwaso Ya Yi

July 22, 2026
Kabiru Gaya Ya Amince Zai Sauya Sheƙa Zuwa APC
Labarai

Kabiru Gaya Ya Amince Zai Sauya Sheƙa Zuwa APC

July 21, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai
Siyasa

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

July 16, 2026
Next Post
Masu Kokarin Kashe Kansu Na Kara Karuwa A Nijeriya

Masu Kokarin Kashe Kansu Na Kara Karuwa A Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

PDP

Tinubu Zai Ƙara Wa Sojoji Albashi Nan Ba Da Jimawa Ba – Ministan Tsaro

July 27, 2026
Har Kullum Sin Na Adawa Da Yadda Amurka Ke Siyasantar Da Batutuwan Fasaha Da Na Tattalin Arziki

Har Kullum Sin Na Adawa Da Yadda Amurka Ke Siyasantar Da Batutuwan Fasaha Da Na Tattalin Arziki

July 27, 2026
Kasar Sin Ta Gabatar Da Matsaya Game Da Matakan Karshe Na Bincike Mai Lamba 301 Kan Tilasta Yin Kwadago Da Amurka Ta Fitar

Kasar Sin Ta Gabatar Da Matsaya Game Da Matakan Karshe Na Bincike Mai Lamba 301 Kan Tilasta Yin Kwadago Da Amurka Ta Fitar

July 27, 2026
PDP

Taimakon Ƴan Bindiga: Kotu Ta Yanke Wa Mata 3 Hukuncin Shekaru 14 A Magarƙama

July 27, 2026
Sin Za Ta Ci Gaba Da Ingiza Kyakkyawan Yanayin Cinikayya Tsakaninta Da Nahiyar Afirka

Sin Za Ta Ci Gaba Da Ingiza Kyakkyawan Yanayin Cinikayya Tsakaninta Da Nahiyar Afirka

July 27, 2026
Sakamakon Dangantakar Sin Da Afrika Na Taba Mutane Masu Rauni Da Karamin Karfi

Sakamakon Dangantakar Sin Da Afrika Na Taba Mutane Masu Rauni Da Karamin Karfi

July 27, 2026
PDP

WAFU B 2026: Nijeriya Ta Doke Ghana Da Ci 4-2 A Wasan Farko

July 27, 2026
An Samu Karin Sabbin Abubuwa Da Sin Ke Fitar Wa Waje Da Ake Wa Lakabi Da “New New Three”

An Samu Karin Sabbin Abubuwa Da Sin Ke Fitar Wa Waje Da Ake Wa Lakabi Da “New New Three”

July 27, 2026
PDP

NSCDC Ta Cafke Mutane 2 Da Ake Zargi Da Sace Kayan Titin Jirgin Kasa A Kano

July 27, 2026
Saura Kwanaki 100 A Bude CIIE Karo Na 9

Saura Kwanaki 100 A Bude CIIE Karo Na 9

July 27, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.