ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wakilai Daga Jihohi 19 Sun Isa Ibadan Don Taron PDP Na Ƙasa

by Abubakar Sulaiman
7 months ago
PDP

Wakilai daga jihohi 19 sun isa Ibadan, babban birnin jihar Oyo, a ranar Juma’a, domin halartar taron ƙasa na jam’iyyar PDP wanda za a gudanar a ranar Asabar 15 ga Nuwamba da Lahadi 16 ga Nuwamba. Jihohin da suka halarta sun haɗa da Adamawa, da Akwa Ibom, da Anambra, da Bauchi, da Bayelsa, da Benue, da Borno, da Cross River, da Delta, da Edo, da Ebonyi, da Enugu, da FCT, da Imo, da Kaduna, da Jigawa, da Kano, da Katsina, da kuma Ekiti.

Taron na zuwa ne yayin da jam’iyyar ke fuskantar rikice-rikice na cikin gida da kuma shari’a a kotu. Kwamitin aiki na ƙasa (NWC), ƙarƙashin jagorancin Shugaban jam’iyyar na ƙasa, Umar Damagum, ya dakatar da Sakatare na ƙasa, Sanata Samuel Anyanwu; Sakatare mai Shirya taro, Umar Bature; da Lauyan jam’iyyar na ƙasa, Kamaldeen Ajibade, bisa zargin aikata abubuwan da suka saɓawa jam’iyya. Wannan mataki ya biyo bayan hukuncin kotun tarayya wanda ya dakatar da taron na ɗan lokaci saboda rashin bin ƙa’idojin gudanarwa, ciki har da gazawar isar da sanarwar taron ga INEC.

  • Rikicin PDP: Fiye Da Wakilai 3,000 Ne Za Su Raba Gardama A Babban Taron Jam’iyyar
  • Atiku Ya Fice Daga PDP Saboda Na Ƙi Bari Ya Lalata Mana Jam’iyya – Wike

Sai dai umarnin Alƙali Akintola ya baiwa jam’iyyar dama ta ci gaba da taron. An kammala shirye-shiryen wajen taron a Filin Wasanni na Lekan Salami, inda aka ƙawata shi da launukan jam’iyyar. Ana sa ran wakilai sama da 3,000 daga jihohin tarayya 36 da FCT, tare da shugabanni, masu ruwa da tsaki, da kuma masu sanya ido daga ƙasashen waje zasu halarci taron.

ADVERTISEMENT

Za a gudanar da zaɓen manyan muƙamai na kasa a wannan taro, ciki har da zaɓen Shugaban jam’iyyar na ƙasa, Sakatare, da sauran manyan jami’an NWC da mataimakansu. A wajen taron, aiyuka na tafiya a ƙarshe, inda aka ɗora tallace-tallace da hotunan yaƙin neman zabe a wurare masu muhimmanci a ciki da wajen filin wasa.

An yi hasashen wannan taro a matsayin ɗaya daga cikin masu jawo cece-kuce mafi girma a tarihin PDP, musamman ma ganin cewa wani ɓangare na jam’iyyar ya janye daga halarta, wanda hakan ya ƙara tsananta yanayin siyasar zaɓen.

LABARAI MASU NASABA

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM

PDP
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000
  • Abubakar Sulaiman
    Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato
  • Abubakar Sulaiman
    Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
  • Abubakar Sulaiman
    Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2, Sun Yi Garkuwa Da 30 A Kogi

MASU ALAKA

Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe
Siyasa

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM
Siyasa

‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM

June 3, 2026
Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada
Siyasa

Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada

June 1, 2026
Next Post
Masu Kokarin Kashe Kansu Na Kara Karuwa A Nijeriya

Masu Kokarin Kashe Kansu Na Kara Karuwa A Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.