• English
  • Business News
Saturday, July 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Faidar Tattaunawar Baya-bayan Nan Ta Shugabannin Sin Da Amurka

by CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Faidar Tattaunawar Baya-bayan Nan Ta Shugabannin Sin Da Amurka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Masharhanta da dama na ci gaba da tofa albarkacin bakin su, game da tattaunawar da shugaban kasar Sin Xi Jinping ya yi ta wayar tarho da takwaransa na Amurka Joe Biden da yammacin ranar Talata, zantawar da ta shiga muhimmin tarihi a kokarin da kasashen biyu ke yi na aiwatar da matakan yaukaka dangantaka da fahimtar juna. Kafin tattaunawar ta baya bayan nan, shugaba Xi da Biden sun gana keke-da-keke a tsibirin Bali na Indonesia a shekarar 2022, sun kuma gana a birnin San Francisco na Amurka a watan Nuwamban bara, kana sun zanta sau 5 ta wayar tarho.

Wannan dai tattaunawa ita ce ta farko a tsakanin shugabannin biyu, tun bayan da suka yi ganawar ido da ido a watan Nuwamban bara a birnin San Francisco, kuma ko shakka babu ana sa ran zantawar ta wannan karo za ta taimaka, wajen ingiza cimma burin da duniya ke da shi game da cimma daidaiton dangantaka tsakanin kasashen biyu mafiya karfin tattalin arziki a duniya.

  • Bloomberg: Damuwa Game Da Karfin Sin Wajen Samar Da Hajoji Ba Ta Da Tushe
  • Sin Ta Musanta Rahoton Amurka Game Da Harkokin Cinikayya

Daga tattaunawar shugaba Xi da mista Biden, muna iya fahimtar burin sassan biyu na fatan cimma wasu muhimman kudurori a bana, tare da burin kaucewa sake shiga wata sabuwar turka-turka tsakanin kasashen biyu.

Shugaba Xi dai ya bayyana manyan kudurorin kasar Sin don gane da dangantakarta da Amurka a bana, yana mai fatan sassan biyu za su martaba matakan wanzar da zaman lafiya, da fifita daidaito, da goyon bayan matakan amincewa juna.

Ko shakka babu idan har kasashen biyu sun amince, tare da aiwatar da alkawuran da suka daukawa juna a ganawar San Francisco, da kuma tattaunawar baya bayan nan, hakan zai ingiza cimma nasarar alakar dake tsakanin Sin da Amurka.

Labarai Masu Nasaba

Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa

Binciken Jin Raayoyi Na CGTN: Duniya Ta Saba Da “Kauracewar” Amurka

Masu fashin baki na ganin idan har kasashen biyu za su kai ga nasarar kyautata alaka, to wajibi ne su sauke nauyin dake wuyan su, ta hanyar martaba juna, su yi cudanya cikin lumana, kana su rungumi hadin gwiwar cimma moriyar juna, kana su ci gaba da yaukaka alaka bisa daidaito.

Muna iya cewa faidar ganawar shugabannin biyu ta kara fito da burin kasar Sin na jaddadawa bangaren Amurka muhimmancin inganta dangantakarsu, da fatan Amurka za ta dakatar da yunkurin danne kamfanonin Sin, kana ta nuna sanin ya kamata don gane da batun zirin Taiwan da tekun kudancin Sin.

A daya bangaren, shugaba Biden ya sha alwashin cika alkawuran da Amurka ta dauka a baya, inda ya jaddada muhimmancin dangantakar Amurka da Sin, yana mai nanata cewa Amurka ba ta neman tada sabon yakin cacar baka, kuma ba ta da muradin sauya tsarin kasar Sin, haka kuma kawancen da take yi da sauran sassa ba ya nufin yi wa Sin taron dangi ko mayar da ita saniyar ware.

Muna iya cewa, idan har kalaman shugaba Biden suka dace da matakan zahiri da Amurka za ta dauka a nan gaba, ko shakka babu sassan biyu za su kai ga cimma nasarar bunkasa kan su, da kuma haifar da babbar faida ga bunkasar tattalin arzikin duniya baki daya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Wani Dansanda Mai Rakiyar Jirgin Kasan Kaduna Zuwa Abuja Ya Rasu Acikin Jirgin

Next Post

Xi Ya Taya Sabuwar Shugabar Malta Murnar Kama Aiki

Related

Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa
Daga Birnin Sin

Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa

15 hours ago
Binciken Jin Raayoyi Na CGTN: Duniya Ta Saba Da “Kauracewar” Amurka
Daga Birnin Sin

Binciken Jin Raayoyi Na CGTN: Duniya Ta Saba Da “Kauracewar” Amurka

16 hours ago
Xi Jinping Ya Karbi Takardun Nadi Daga Sabbin Jakadun Kasashen Waje
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Karbi Takardun Nadi Daga Sabbin Jakadun Kasashen Waje

17 hours ago
Wakilin Sin Ya Karyata Amurka Game Da Batun Yankin Xinjiang Na Sin a Taron Kwamitin Sulhun MDD
Daga Birnin Sin

Wakilin Sin Ya Karyata Amurka Game Da Batun Yankin Xinjiang Na Sin a Taron Kwamitin Sulhun MDD

18 hours ago
Kamfanin Sinotruk Na Kasar Sin Ya Kaddamar Da Sabbin Motocin Dakon Kaya A Kenya
Daga Birnin Sin

Kamfanin Sinotruk Na Kasar Sin Ya Kaddamar Da Sabbin Motocin Dakon Kaya A Kenya

19 hours ago
An Amince Da Biranen Kasar Sin 9 A Matsayin Biranen Dausayi Na Kasa Da Kasa
Daga Birnin Sin

An Amince Da Biranen Kasar Sin 9 A Matsayin Biranen Dausayi Na Kasa Da Kasa

20 hours ago
Next Post
Xi Ya Taya Sabuwar Shugabar Malta Murnar Kama Aiki

Xi Ya Taya Sabuwar Shugabar Malta Murnar Kama Aiki

LABARAI MASU NASABA

An Harbe Fitaccen Dan Bindigan Da Ya Addabi Mazauna Abuja A Sansaninsa

Edo Da Taraba : ‘Yansanda Sun Ceto Mutum 31 Da Aka Yi Garkuwa Da Su Bayan Musayar Wuta

July 26, 2025
WAFCON 2025: Yau Nijeriya Za Ta Kece Raini Da Moroko A Wasan Ƙarshe

WAFCON 2025: Yau Nijeriya Za Ta Kece Raini Da Moroko A Wasan Ƙarshe

July 26, 2025
Kotu

NSCDC Ta Gurfanar Da Wanda Ake Zargi Da Badakalar Naira Miliyan 159

July 26, 2025
Fasakwauri: ‘Yansandan Indiya Sun Kama ‘Yar Nijeriya Da Kwayar Dala Miliyan 4

Fasakwauri: ‘Yansandan Indiya Sun Kama ‘Yar Nijeriya Da Kwayar Dala Miliyan 4

July 26, 2025
Sin Ta Gaggauta Aikin Gyara Da Kyautata Ababen Aikin Gona

Asusun NADF, OCP Da Gwamnatin Katsina Sun Kaddamar Da Noman Hekta 50

July 26, 2025
Gwamnatin Kano Ta Gabatar Da Buƙatu 10 A Gaban Kwamitin Gyaran Tsarin Mulkin Nijeriya

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincikar Kwamishinan Sufuri Kan Karɓar Belin Dilan Ƙwaya A Kano

July 26, 2025
Manyan Nasarorin Da Dakta Dantsoho Ya Samar Tun Darewarsa Shugabancin NPA

Manyan Nasarorin Da Dakta Dantsoho Ya Samar Tun Darewarsa Shugabancin NPA

July 26, 2025
Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare

Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare

July 26, 2025
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

ADC Ga Tinubu: Ina Wutar Lantarki Ta Awa 24 Da Ka Yi Wa ‘Yan Nijeriya Alkawari?

July 26, 2025
Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa

Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa

July 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.