• English
  • Business News
Friday, October 31, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Faidar Tattaunawar Baya-bayan Nan Ta Shugabannin Sin Da Amurka

by CGTN Hausa
2 years ago
Amurka

Masharhanta da dama na ci gaba da tofa albarkacin bakin su, game da tattaunawar da shugaban kasar Sin Xi Jinping ya yi ta wayar tarho da takwaransa na Amurka Joe Biden da yammacin ranar Talata, zantawar da ta shiga muhimmin tarihi a kokarin da kasashen biyu ke yi na aiwatar da matakan yaukaka dangantaka da fahimtar juna. Kafin tattaunawar ta baya bayan nan, shugaba Xi da Biden sun gana keke-da-keke a tsibirin Bali na Indonesia a shekarar 2022, sun kuma gana a birnin San Francisco na Amurka a watan Nuwamban bara, kana sun zanta sau 5 ta wayar tarho.

Wannan dai tattaunawa ita ce ta farko a tsakanin shugabannin biyu, tun bayan da suka yi ganawar ido da ido a watan Nuwamban bara a birnin San Francisco, kuma ko shakka babu ana sa ran zantawar ta wannan karo za ta taimaka, wajen ingiza cimma burin da duniya ke da shi game da cimma daidaiton dangantaka tsakanin kasashen biyu mafiya karfin tattalin arziki a duniya.

  • Bloomberg: Damuwa Game Da Karfin Sin Wajen Samar Da Hajoji Ba Ta Da Tushe
  • Sin Ta Musanta Rahoton Amurka Game Da Harkokin Cinikayya

Daga tattaunawar shugaba Xi da mista Biden, muna iya fahimtar burin sassan biyu na fatan cimma wasu muhimman kudurori a bana, tare da burin kaucewa sake shiga wata sabuwar turka-turka tsakanin kasashen biyu.

Shugaba Xi dai ya bayyana manyan kudurorin kasar Sin don gane da dangantakarta da Amurka a bana, yana mai fatan sassan biyu za su martaba matakan wanzar da zaman lafiya, da fifita daidaito, da goyon bayan matakan amincewa juna.

Ko shakka babu idan har kasashen biyu sun amince, tare da aiwatar da alkawuran da suka daukawa juna a ganawar San Francisco, da kuma tattaunawar baya bayan nan, hakan zai ingiza cimma nasarar alakar dake tsakanin Sin da Amurka.

LABARAI MASU NASABA

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Kirkire-kirkire Da Bude Kofa Da Raba Damar Samun Ci Gaba A Colombo

Sin Ta Fitar Da Jerin Sakamakon Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Tawagar Kasar Da Ta Amurka Suka Cimma 

Masu fashin baki na ganin idan har kasashen biyu za su kai ga nasarar kyautata alaka, to wajibi ne su sauke nauyin dake wuyan su, ta hanyar martaba juna, su yi cudanya cikin lumana, kana su rungumi hadin gwiwar cimma moriyar juna, kana su ci gaba da yaukaka alaka bisa daidaito.

Muna iya cewa faidar ganawar shugabannin biyu ta kara fito da burin kasar Sin na jaddadawa bangaren Amurka muhimmancin inganta dangantakarsu, da fatan Amurka za ta dakatar da yunkurin danne kamfanonin Sin, kana ta nuna sanin ya kamata don gane da batun zirin Taiwan da tekun kudancin Sin.

A daya bangaren, shugaba Biden ya sha alwashin cika alkawuran da Amurka ta dauka a baya, inda ya jaddada muhimmancin dangantakar Amurka da Sin, yana mai nanata cewa Amurka ba ta neman tada sabon yakin cacar baka, kuma ba ta da muradin sauya tsarin kasar Sin, haka kuma kawancen da take yi da sauran sassa ba ya nufin yi wa Sin taron dangi ko mayar da ita saniyar ware.

Muna iya cewa, idan har kalaman shugaba Biden suka dace da matakan zahiri da Amurka za ta dauka a nan gaba, ko shakka babu sassan biyu za su kai ga cimma nasarar bunkasa kan su, da kuma haifar da babbar faida ga bunkasar tattalin arzikin duniya baki daya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Kirkire-kirkire Da Bude Kofa Da Raba Damar Samun Ci Gaba A Colombo
Daga Birnin Sin

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Kirkire-kirkire Da Bude Kofa Da Raba Damar Samun Ci Gaba A Colombo

October 30, 2025
Sin Ta Fitar Da Jerin Sakamakon Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Tawagar Kasar Da Ta Amurka Suka Cimma 
Daga Birnin Sin

Sin Ta Fitar Da Jerin Sakamakon Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Tawagar Kasar Da Ta Amurka Suka Cimma 

October 30, 2025
Babban Daraktan Sakatariyar APEC: Sin Tana Ba Da Gudummawar Ba Da Jagoranci A APEC
Daga Birnin Sin

Babban Daraktan Sakatariyar APEC: Sin Tana Ba Da Gudummawar Ba Da Jagoranci A APEC

October 30, 2025
Next Post
Xi Ya Taya Sabuwar Shugabar Malta Murnar Kama Aiki

Xi Ya Taya Sabuwar Shugabar Malta Murnar Kama Aiki

LABARAI MASU NASABA

Matsalar Talauci Da Rashin Tsawon Rai Da ‘Yan Nijeriya Ke Fuskanta

Matsalar Talauci Da Rashin Tsawon Rai Da ‘Yan Nijeriya Ke Fuskanta

October 31, 2025
Matsalar Tsaro: Ko Sabbin Shugabannin Rundunar Soji Za Su Kawo Sauyi?

Matsalar Tsaro: Ko Sabbin Shugabannin Rundunar Soji Za Su Kawo Sauyi?

October 31, 2025
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Kirkire-kirkire Da Bude Kofa Da Raba Damar Samun Ci Gaba A Colombo

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Kirkire-kirkire Da Bude Kofa Da Raba Damar Samun Ci Gaba A Colombo

October 30, 2025
An Yi Wa Yara Sama Da Miliyan Biyu Allurar Rigakafin Mashaƙo Da Sankarau A Zamfara

An Yi Wa Yara Sama Da Miliyan Biyu Allurar Rigakafin Mashaƙo Da Sankarau A Zamfara

October 30, 2025
Sin Ta Fitar Da Jerin Sakamakon Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Tawagar Kasar Da Ta Amurka Suka Cimma 

Sin Ta Fitar Da Jerin Sakamakon Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Tawagar Kasar Da Ta Amurka Suka Cimma 

October 30, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

‘Yansanda Sun Ceto Mutum Ɗaya, Sun Kama Mace Da Zargin Garkuwa Da Mutane A Dajin Kwara 

October 30, 2025
Babban Daraktan Sakatariyar APEC: Sin Tana Ba Da Gudummawar Ba Da Jagoranci A APEC

Babban Daraktan Sakatariyar APEC: Sin Tana Ba Da Gudummawar Ba Da Jagoranci A APEC

October 30, 2025
Barcelona Na Shirin Ɗauko Victor Osimhen Na Galatasaray

Barcelona Na Shirin Ɗauko Victor Osimhen Na Galatasaray

October 30, 2025
Kasar Sin Ce Ke Da Sama Da Rabin Muhimman Makaloli Na Duniya

Kasar Sin Ce Ke Da Sama Da Rabin Muhimman Makaloli Na Duniya

October 30, 2025
Tinubu Ya Yi Wa Shugabannin Tsaro Ado Da Sabbin Muƙamai

Tinubu Ya Yi Wa Shugabannin Tsaro Ado Da Sabbin Muƙamai

October 30, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.