ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Faidar Tattaunawar Baya-bayan Nan Ta Shugabannin Sin Da Amurka

by CGTN Hausa
2 years ago
Amurka

Masharhanta da dama na ci gaba da tofa albarkacin bakin su, game da tattaunawar da shugaban kasar Sin Xi Jinping ya yi ta wayar tarho da takwaransa na Amurka Joe Biden da yammacin ranar Talata, zantawar da ta shiga muhimmin tarihi a kokarin da kasashen biyu ke yi na aiwatar da matakan yaukaka dangantaka da fahimtar juna. Kafin tattaunawar ta baya bayan nan, shugaba Xi da Biden sun gana keke-da-keke a tsibirin Bali na Indonesia a shekarar 2022, sun kuma gana a birnin San Francisco na Amurka a watan Nuwamban bara, kana sun zanta sau 5 ta wayar tarho.

Wannan dai tattaunawa ita ce ta farko a tsakanin shugabannin biyu, tun bayan da suka yi ganawar ido da ido a watan Nuwamban bara a birnin San Francisco, kuma ko shakka babu ana sa ran zantawar ta wannan karo za ta taimaka, wajen ingiza cimma burin da duniya ke da shi game da cimma daidaiton dangantaka tsakanin kasashen biyu mafiya karfin tattalin arziki a duniya.

  • Bloomberg: Damuwa Game Da Karfin Sin Wajen Samar Da Hajoji Ba Ta Da Tushe
  • Sin Ta Musanta Rahoton Amurka Game Da Harkokin Cinikayya

Daga tattaunawar shugaba Xi da mista Biden, muna iya fahimtar burin sassan biyu na fatan cimma wasu muhimman kudurori a bana, tare da burin kaucewa sake shiga wata sabuwar turka-turka tsakanin kasashen biyu.

ADVERTISEMENT

Shugaba Xi dai ya bayyana manyan kudurorin kasar Sin don gane da dangantakarta da Amurka a bana, yana mai fatan sassan biyu za su martaba matakan wanzar da zaman lafiya, da fifita daidaito, da goyon bayan matakan amincewa juna.

Ko shakka babu idan har kasashen biyu sun amince, tare da aiwatar da alkawuran da suka daukawa juna a ganawar San Francisco, da kuma tattaunawar baya bayan nan, hakan zai ingiza cimma nasarar alakar dake tsakanin Sin da Amurka.

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Masu fashin baki na ganin idan har kasashen biyu za su kai ga nasarar kyautata alaka, to wajibi ne su sauke nauyin dake wuyan su, ta hanyar martaba juna, su yi cudanya cikin lumana, kana su rungumi hadin gwiwar cimma moriyar juna, kana su ci gaba da yaukaka alaka bisa daidaito.

Muna iya cewa faidar ganawar shugabannin biyu ta kara fito da burin kasar Sin na jaddadawa bangaren Amurka muhimmancin inganta dangantakarsu, da fatan Amurka za ta dakatar da yunkurin danne kamfanonin Sin, kana ta nuna sanin ya kamata don gane da batun zirin Taiwan da tekun kudancin Sin.

A daya bangaren, shugaba Biden ya sha alwashin cika alkawuran da Amurka ta dauka a baya, inda ya jaddada muhimmancin dangantakar Amurka da Sin, yana mai nanata cewa Amurka ba ta neman tada sabon yakin cacar baka, kuma ba ta da muradin sauya tsarin kasar Sin, haka kuma kawancen da take yi da sauran sassa ba ya nufin yi wa Sin taron dangi ko mayar da ita saniyar ware.

Muna iya cewa, idan har kalaman shugaba Biden suka dace da matakan zahiri da Amurka za ta dauka a nan gaba, ko shakka babu sassan biyu za su kai ga cimma nasarar bunkasa kan su, da kuma haifar da babbar faida ga bunkasar tattalin arzikin duniya baki daya.

Amurka
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

MASU ALAKA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
Daga Birnin Sin

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
Daga Birnin Sin

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos
Daga Birnin Sin

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Next Post
Xi Ya Taya Sabuwar Shugabar Malta Murnar Kama Aiki

Xi Ya Taya Sabuwar Shugabar Malta Murnar Kama Aiki

LABARAI MASU NASABA

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.