Karamin Ministan Tsaro, Dakta Bello Matawalle ya bayyana cewa, sauye-sauyen da Shugaba Bola Tinubu ya yi na inganta manufofin tattalin arziki sun fara haifar da sakamako mai kyau.
Wannan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da Daraktan yada labarai da hulda da jama’a na ma’aikatar tsaro, Mista Henshaw Ogubike, ya fitar ranar Alhamis a Abuja.
- NEMA Ta Bayar Da Tallafin Kayan Agaji Ga Wadanda Harin ‘Yan Bindiga Ya Shafa A Zamfara
- Shirin NG-CARES: Gwamna Lawal Ya Tallafawa Mutane 44,000 Da Fiye Da Naira Biliyan 4
Matawalle ya ce, wadannan tsare-tsare da suka hada da sabbin sauye-sauyen haraji da kuma nasarori da dama da aka samu a bangarori daban-daban sun ba da gudummawa wajen kawo sauyi a tattalin arzikin kasar nan.
Ya kara da cewa, wannan sauyin da aka samu a fannin tattalin arziki zai amfanar da dukkan ‘yan Nijeriya nan gaba.
Don haka, ya bukaci masu sukar gwamnatin Tinubu, musamman daga sassan Arewacin Nijeriya da su kasance masu kyakkyawar fata.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp