Farfesa Haruna Musa ya samu nasarar zama wanda ya lashe zaben kujerar Mataimakin Shugaban Jami’ar Bayero da ke Kano (BUK) bayan nasarar da ya samu a babban taron jami’ar. Farfesan ya samu ƙuri’u 853, ya doke sauran ‘yan takara a zaben da ya ja hankalin al’ummar jami’ar.
Jami’ar ta tabbatar da sakamakon zaben ta hannun shafinta na Facebook, inda ta bayyana nasarar Farfesa Musa a hukumance, alamar buɗe sabon babi a shugabancin ɗaya daga cikin manyan cibiyoyin ilimi a Nijeriya.
- Jigawa Za Ta Samar Da Kashi 25 Na Shinkafar Da Nijeriya Ke Bukata – Hon Abdurahman
- Faɗuwar Darajar Naira Ta Sa Bashin Nijeriya Ya Ƙaru Zuwa Naira Tiriliyan 149
Farfesa Musa, wanda ke matsayin Mataimakin Shugaban Jami’a mai kula da harkokin karatu (Academics) a halin yanzu, ya fara karatunsa ne a makarantar Sakandaren Gwamnati da ke Danbatta a shekarar 1985. Ya samu digiri na farko a fannin Chemistry daga BUK a 1991, sai digirin digirgir (Master’s) a fannin Polymer Chemistry a 1999, sannan ya kammala babban digirin digirgir (PhD) a fannin guda daga Jami’ar Bristol a Birtaniya a 2009.
A tsawon shekarun aikinsa, Farfesa Musa ya riƙe muhimman muƙamai a jami’ar, kamar Shugaban sashin Pure and Industrial Chemistry, Shugaban reshen ASUU na BUK, da kuma Mataimakin Darakta a Cibiyar Bunƙasa Makamashi da Sauyin Mai Ɗorewa (CREST). Ƙwarewarsa da jajircewarsa wajen inganta ilimi sun ba shi girmamawa daga abokan aiki da ɗalibai.
Sakamakon wannan zaɓe muhimmin ci gaba ne a tafiyar aikinsa, kuma yana nuna yarda da amincewar al’ummar jami’a da hangen nesansa. Ana sa ran jagorancinsa zai kai BUK mataki na gaba wajen ci gaban ilimi da kyakkyawan gudanarwa.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp