• English
  • Business News
Sunday, June 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Farin Ciki Ya Lullube Manoma A Taraba Sakamakon Tashin Farashin Agushi

by Abubakar Abba
2 years ago
in Labarai
0
Dalibai 4000 Ne Suka Shiga Noman Kayan Lambu Na Zamani – Dakta Bello
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Manoman Agushi a Jihar Taraba, na cikin murna da farin ciki sakamakon tashin gwauron zabi da farashinsa ya yi a kasuwannin jihar.

Bincike ya tabbatar da cewa, buhun Agushin mai nauyin kilo 100, ana sayar da shi a kan farashin Naira 100,000.

  • GORON JUMA’A
  • Kasar Sin Na Marawa AU Baya Wajen Kara Taka Rawar Gani A Harkokin Duniya

Har ila yau, binciken ya sake tabbatar da cewa, baya ga tashin farashin nasa, manoman sun sake samun amfani mai dimbin yawa bayan sun girbe shi a Jihar ta Taraba.

Bugu da kari, a gona daya tak an girbe buhu kimanin goma a shekarar da ta gabata, sama da buhu 25 aka girbe a irin wannan gonar.

Daruruwan manoman a garuruwan Bali, Gassol, Gashaka, Donga da kuma Karim-Lamido da ke a Karamar Hukumar  Wukari ta Jihar Taraba, akasari sun rungumi yin noman Agushin, sakamaon karin bukatarsa da ake yi a ‘yan shekarun nan.

Labarai Masu Nasaba

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

An rawaito cewa, wasu daga cikin manoman a garuruwan Bali da Gassol, sun girbe sama da buhu 100 na Agushin a kakar nomansa ta bana, wanda hakan ya sa suka samu miliyoyin nairori a matsayin kudin shiga.

Sakamakon  samun irin wannan gagarumar riba ne, wasu manoma da dama a jihar, su ma suka fara yin wannan noma na Agushi, wanda a cikin watanni uku kacal masu zuwa suke sa ran fara girbe shi.

Daya daga cikin manoma Agushin mai suna Musa Saidu, ya sanar da cewa, a shekarar da ta gabata, ya girbe kimanin buhu 60, inda kuma a kakar noman bana ya girbe buhu 95, duk dai a cikin wannan gonar tasa.

Haka zalika, Musa ya kara da cewa, Agushi na samun karbuwa a daukacin kasuwannin da ke cikin Jihar Taraba, ya kuma kara da cewa, a kasuwannin Garba, Chede Maihula da kuma sauran kasuwanni, akwai dillalansa daga sassa daban-daban na wannan kasa.

Har ila yau, bincike ya nuna cewa, shi kansa Iri na Agushin kala biyu ne wanda aka fi bukata, wadanda kuma ake sayar da su da matukar tsada, sannan ya sanar da cewa, Iri na samfurin China ana kara nuna bukatarsa, wanda a yanzu ya buhu mai cin kilo 100, ya kai daga naira   90,000 zuwa naira 100,000.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Wata Girgizar Kasa Mai Karfi Ta Kashe Fiye Da Mutum 820 A Morocco

Next Post

Manoman Da Suka Ci Bashin ‘Anchor Borrowers’ Na Cikin Tsaka Mai Wuya

Related

‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi
Labarai

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

3 hours ago
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote
Labarai

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

5 hours ago
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne
Ra'ayi Riga

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

6 hours ago
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno
Labarai

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

10 hours ago
Taraba
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

11 hours ago
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023
Labarai

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

12 hours ago
Next Post
Manoman Da Suka Ci Bashin ‘Anchor Borrowers’ Na Cikin Tsaka Mai Wuya

Manoman Da Suka Ci Bashin ‘Anchor Borrowers’ Na Cikin Tsaka Mai Wuya

LABARAI MASU NASABA

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

June 7, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.