ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Manoman Da Suka Ci Bashin ‘Anchor Borrowers’ Na Cikin Tsaka Mai Wuya

by Abubakar Abba
3 years ago
Bashin

Shirin nan na bayar da rance a harkar noma na ‘Anchor Borrowers’, wanda Babban Bankin Nijeriya ya kirkiro tare da jagoranta, domin kara bunkasa harkokin noma a Nijeriya ya fuskanci matukar koma baya, sakamakon kin dawo da kudaden da Manoman suka yi a matsayin rance.

Wannan hali na kin biyan wadannan kudade da wasu daga cikin Manoman da suka amfana da shirin suka yi, ya janyo wa sauran Manoman da ba su amfana da shirin ba tasgaro wajen samun wannan rance, lamarin da ya jefa su cikin tsaka mai wuya.

  • NIS Reshen Jihar Ribas Ta Nada Queen Stephanie Jakadiyar Fasfo
  • Ma’aikatan Kiwon Lafiya 83 Aka Yi Garkuwa Da Su A Katsina Cikin Shekara 8 – MHWUN

Daga cikin Naira tiriliyan 1.1, wanda Babban Bankin Nijeriya ya raba wa Manoma a matsayin rance, tun bayan kafa wannan shiri, kasa da Naira biliyan 546 kacal aka iya dawo da su, inda kimanin Naira biliyan 577 kuma, suka makale a hannun Manoman suka ki maido da su.

ADVERTISEMENT

Wadannan makudan kudaden, sun makale ne a hannun Bankunan Hada-hadar Kudi, Gwamnatocin Jihohi, Kungiyoyin Manoma, daidaikun mutane, da kuma kamfanoni, wanda hakan ya harzuka Fadar Shugaban Kasa tare da bayyana cewa, hakan ya yi sanadiyyar gaza cimma burin da aka sanya a gaba ainahin manufar shirin.

Wata majiya mai karfi, ta sheda wa Jaridar Banguard cewa, an yi wa Shugaba Kasa Bola Ahmed Tinubu bayani a kan lamarin, inda ya yi matukar nuna bacin ransa a kan wadanda suka amfana da shirin suka kuma ki maido da wadannan kudade da aka ba su a matsayin rance. A cewar tasa, da sun maido da wadannan kudade, akwai yiwuwar wadanda ba su samu ba, su ma su samu.

LABARAI MASU NASABA

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa

Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

Bugu da kari, daya daga cikin hukumomin tsaron ya bayyana cewa, Tinubu ya umarci daukan dukkanin matakan da suka dace na dawo da wadannan kudade daga wurin wadanda suka amfana da su, suka kuma ki maidowa daga nan zuwa ranar 18 ga watan Satumban 2023, musamman domin ainahin Manoman su amfana da su, a samu wadataccen abinci a fadin wannan kasa.

Haka zalika, an kuma shaida wa shugaban kasar cewa, Babban Bankin Nijeriya tare da ‘yan barandansa, sun karkatar da kimanin Naira miliyan 255, wadanda ya kamata a rabawa wa sauran Manoman da ba su samu ba.

Bugu da kari, an sake zargin bankuna da sauran wasu kungiyoyi a matsayin wadanda suka karkatar da naira miliyan 255, da aka karbo daga wurin wadanda suka amfana da wannan rance, amma suka ki mika wa Babban Bankin wadannan kudade.

Har ila yau, wasu daga cikin wadanda suka amfana da rancen kudaden, sun ki maido da su ne tare da yin ikirarin cewa, sun yi noman amma ba su samu wata rabar a zo a gani ba, inda suke sake bukatar a kara musu wani wa’adin, domin mayar da rance ga Babban Bankin Nijeriyar.

Tuni dai jami’ain tsaro suka fara tuhumar wasu daga cikin Manajojin Bankuna da dama a kan rikita-rikitar ta kin maido da wadannan kudade na rance, wanda akasarinsu sun amsa saba ka’idar da aka ginidaya ta maido da rancen kudaden.

Wasu daga cikin kungiyoyin da suka amfana da rancen a karkashin shirin na ‘Anchor Borrowers’, sun hada da Kungiyar Manoman Masara, Waken Suya da kuma Noman Auduga.

Kazalika, binciken Jaridar Banguard din ya sake nuna cewa, Kungiyar Manoman Masara ta karbi rancen naira  biliyan 39 daga Babban Bankin Nijeriya, a karkashin wannan shiri na ‘Anchor Borrowers’.

Haka nan ita ma, Kungiyar Manoman Auduga ta karbi rancen naira biliyan 14, sannan ta maido da naira biliyan 5 daga ciki.

Har wa yau, an yi kokarin jin ta bakin mai magana da yawun Hukumomin Tsaro da ke Abuja a kan umarnin da Shugaban Kasar ya bayar  na karbo wadannan kudade, amma bai ce komai ba.

Haka nan, shi ma Kakakin Hukumar Tsaro ta farin kaya (DSS), Dakta  Peter Afunanya; da aka tuntube shi don jin ta bakinsa, bai ce uffan ba, sai dai ya ce, batun bayar da umarnin Shugaban Kasa; ba wani sabon abu ne ga Hukomin Tsaron Kasa.

Bashin
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

MASU ALAKA

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa

June 20, 2026
Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
Noma Da Kiwo

Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

June 20, 2026
Kungiyar Manoman Citta Ta Kasa Ta Yaba Wa Gwamnatin Tarayya Kan Tallafin Da Take Ba Su
Noma Da Kiwo

Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

June 19, 2026
Next Post
Xi

Xi Ya Jaddada Yin Kokari Wajen Farfado Da Yankin Arewa Maso Gabashin Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.