• English
  • Business News
Wednesday, July 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Fasahar Amfani Da ’Yan Sandan Mutum-Mutumi Ta Kasar Sin Na Iya Taimaka Wa Tsaro A Afirka

by CGTN Hausa and Sulaiman
4 hours ago
in Daga Birnin Sin
0
Fasahar Amfani Da ’Yan Sandan Mutum-Mutumi Ta Kasar Sin Na Iya Taimaka Wa Tsaro A Afirka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ko makaho ya shafa, ya san yadda kimiyya da fasaha ke ci gaba taka gagarumar muhimmiyar rawa wajen kawo sauyi a daukacin sassan rayuwar bil’adama ta yau da kullum a duk fadin duniya. Kasar Sin na ci gaba da amfani da fasahohinta na zamanantarwa wajen kirkire-kirkire da kawo sabbin salo.

Da yake kasar tana shirin karbar bakuncin gasar wasannin motsa jiki ta duniya ta shekarar 2025 daga ranar 7 zuwa 17 ga Agusta, yanzu haka ta kera wasu mutum-mutumi na ’yan sanda da suka fara sintiri a hukumance a birnin Chengdu dake lardin Sichuan na yankin kudu maso yammacin kasar.

  • ‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
  • An Fara Binciken Mutuwar Wasu Ɗalibai 2 A Makarantar Kwana A Kano

’Yan sandan mutum-mutumin sun tsunduma aiki tare da jami’ai abokan aikinsu a dandalin Tianfu, daya daga cikin wuraren da aka fi samun kai-komon mutane da kafa a kalla 100,000 a kullum. Da kansu suke sauya wurin aiki a tsakaninsu duk bayan awa biyu zuwa uku inda suke nadar murya da bidiyon abubuwan dake faruwa tare da aikawa nan take ga jami’an ’yan sandan dake kusa. A ranar 16 ga Yunin da ya gabata ne aka fara gwada ayyukan ’yan sandan na mutum-mutumi da nufin kara inganta amfani da su a birane.

An saya musu fasahar iya sadarwa, da yadda za su iya ba da taimakon aikin ’yan sanda ga masu yawon bude ido, da kula da zirga-zirgar ababen hawa, sannan da kansu suke kai kansu wurin caji don tabbatar da cewa aikinsu bai tsaya ba. Akwai abubuwan mamaki da yawa da wadannan ’yan sanda ke iya yi ciki har da gano mara lafiya a cikin masu yawon bude ido tare da kiran tawagar kawo daukin gaggawa.

Wannan fasaha za ta iya taimakon kasashenmu na Afirka wajen shawo kan matsalolin tsaro da dama duba da cewa har yanzu muna da karancin jami’an tsaro. Kididdigar da na gani daga shafin rumbun bayanai na Wikipedia na nuna cewa, a Nijeriya, mai yawan al’umma fiye da miliyan 230, duk dan sanda daya yana ba da tsaro ne ga kusan mutane 1000 ko kuma a ce duk ’yan sanda biyu suna kula ne da tsaron mutum 2,000. Kazalika, idan aka leka sauran kasashenmu na Afirka ma za a ga irin wannan gibin.

Labarai Masu Nasaba

Zambia Na Maraba Da Tawaga Ta 26 Ta Jami’an Lafiya Ta Sin

Jarin Kasar Sin Ya Bada Gudunmawa Ga Ci Gaban Tattalin Arzikin Zimbabwe

Idan za a yi amfani da wannan fasaha ta ’yan sandan mutum-mutumin inji ana iya rage yawan jami’ai da ake jibgewa a wuraren shafaffu da mai tare da kai su yankunan da ake fama da matsalar tsaro musamman na karkara.

Kar wani ya yi tunanin ko idan an dauki ’yan sanda daga birane zuwa karkara kamar an yi musu ba daidai ba, a’a, a ko ina aiki ya kama dole a je. Kuma da kudin kasa ake biyansu albashi ba kudin ’yan birni ba kawai. Su ma mazauna birane za su ci gajiyar hakan, don ’yan sandan mutum-mutumin za su yi aiki babu kakkautawa, tun da ba su bukatar barci, ko cin abinci, ko zaga bayi, da sauran wasu abubuwa na lalurorin dan’adam. Tabbas, amfani da su, zai kara yalwata jami’an ’yan sanda da ake bukata wurin gudanar da ayyukan tsaro ta yadda za a share wa al’umma hawaye ta fuskar matsalar tsaron da ake fama da ita.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Farashin Kayayyaki Sun Sauka A Watan Yuni 2025

Next Post

PDP Ba Za Ta Damu Da Rashin Atiku Ba – Gwamna Makinde

Related

Zambia Na Maraba Da Tawaga Ta 26 Ta Jami’an Lafiya Ta Sin
Daga Birnin Sin

Zambia Na Maraba Da Tawaga Ta 26 Ta Jami’an Lafiya Ta Sin

34 minutes ago
Jarin Kasar Sin Ya Bada Gudunmawa Ga Ci Gaban Tattalin Arzikin Zimbabwe
Daga Birnin Sin

Jarin Kasar Sin Ya Bada Gudunmawa Ga Ci Gaban Tattalin Arzikin Zimbabwe

2 hours ago
An Gudanar Da Taron Ministocin Wajen Kasashe Mambobin SCO A Tianjin
Daga Birnin Sin

An Gudanar Da Taron Ministocin Wajen Kasashe Mambobin SCO A Tianjin

3 hours ago
Kasar Sin Na Inganta Samun Nasara Ga Kowane Bangare A Fannin Masana’antu Da Samar Da Kayayyaki A Duniya
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Na Inganta Samun Nasara Ga Kowane Bangare A Fannin Masana’antu Da Samar Da Kayayyaki A Duniya

5 hours ago
Xi Jinping Ya Mika Sakon Ta’aziyya Zuwa Ga Takwaransa Na Najeriya Bisa Rasuwar Muhammadu Buhari
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Mika Sakon Ta’aziyya Zuwa Ga Takwaransa Na Najeriya Bisa Rasuwar Muhammadu Buhari

6 hours ago
Sin Ta Yi Nasarar Harba Kumbon Dakon Kaya Na Tianzhou-9
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Nasarar Harba Kumbon Dakon Kaya Na Tianzhou-9

1 day ago
Next Post
PDP Ba Za Ta Damu Da Rashin Atiku Ba – Gwamna Makinde

PDP Ba Za Ta Damu Da Rashin Atiku Ba – Gwamna Makinde

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kashe Kwamandan Ƙungiyar Haram/ISWAP Da Wasu 5 A Chadi

Sojoji Sun Kashe Kwamandan Ƙungiyar Haram/ISWAP Da Wasu 5 A Chadi

July 16, 2025
Zambia Na Maraba Da Tawaga Ta 26 Ta Jami’an Lafiya Ta Sin

Zambia Na Maraba Da Tawaga Ta 26 Ta Jami’an Lafiya Ta Sin

July 16, 2025
Dubun Wasu Mutane 20 Da Ake Zargi Da Safarar Makamai A Kwara Ta Cika

Dubun Wasu Mutane 20 Da Ake Zargi Da Safarar Makamai A Kwara Ta Cika

July 16, 2025
Jarin Kasar Sin Ya Bada Gudunmawa Ga Ci Gaban Tattalin Arzikin Zimbabwe

Jarin Kasar Sin Ya Bada Gudunmawa Ga Ci Gaban Tattalin Arzikin Zimbabwe

July 16, 2025
Kwalejin Digiri Na Biyu Ta ABU Ta Ƙaddamar Da Sabbin Ɗalibai A Zariya

Kwalejin Digiri Na Biyu Ta ABU Ta Ƙaddamar Da Sabbin Ɗalibai A Zariya

July 16, 2025
An Gudanar Da Taron Ministocin Wajen Kasashe Mambobin SCO A Tianjin

An Gudanar Da Taron Ministocin Wajen Kasashe Mambobin SCO A Tianjin

July 16, 2025
PDP Ba Za Ta Damu Da Rashin Atiku Ba – Gwamna Makinde

PDP Ba Za Ta Damu Da Rashin Atiku Ba – Gwamna Makinde

July 16, 2025
Fasahar Amfani Da ’Yan Sandan Mutum-Mutumi Ta Kasar Sin Na Iya Taimaka Wa Tsaro A Afirka

Fasahar Amfani Da ’Yan Sandan Mutum-Mutumi Ta Kasar Sin Na Iya Taimaka Wa Tsaro A Afirka

July 16, 2025
Farashin Kayayyaki Sun Sauka A Watan Yuni 2025

Farashin Kayayyaki Sun Sauka A Watan Yuni 2025

July 16, 2025
Kasar Sin Na Inganta Samun Nasara Ga Kowane Bangare A Fannin Masana’antu Da Samar Da Kayayyaki A Duniya

Kasar Sin Na Inganta Samun Nasara Ga Kowane Bangare A Fannin Masana’antu Da Samar Da Kayayyaki A Duniya

July 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.