• English
  • Business News
Saturday, September 20, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Fasahar Amfani Da ’Yan Sandan Mutum-Mutumi Ta Kasar Sin Na Iya Taimaka Wa Tsaro A Afirka

by CGTN Hausa and Sulaiman
2 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Fasahar Amfani Da ’Yan Sandan Mutum-Mutumi Ta Kasar Sin Na Iya Taimaka Wa Tsaro A Afirka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ko makaho ya shafa, ya san yadda kimiyya da fasaha ke ci gaba taka gagarumar muhimmiyar rawa wajen kawo sauyi a daukacin sassan rayuwar bil’adama ta yau da kullum a duk fadin duniya. Kasar Sin na ci gaba da amfani da fasahohinta na zamanantarwa wajen kirkire-kirkire da kawo sabbin salo.

Da yake kasar tana shirin karbar bakuncin gasar wasannin motsa jiki ta duniya ta shekarar 2025 daga ranar 7 zuwa 17 ga Agusta, yanzu haka ta kera wasu mutum-mutumi na ’yan sanda da suka fara sintiri a hukumance a birnin Chengdu dake lardin Sichuan na yankin kudu maso yammacin kasar.

  • ‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
  • An Fara Binciken Mutuwar Wasu Ɗalibai 2 A Makarantar Kwana A Kano

’Yan sandan mutum-mutumin sun tsunduma aiki tare da jami’ai abokan aikinsu a dandalin Tianfu, daya daga cikin wuraren da aka fi samun kai-komon mutane da kafa a kalla 100,000 a kullum. Da kansu suke sauya wurin aiki a tsakaninsu duk bayan awa biyu zuwa uku inda suke nadar murya da bidiyon abubuwan dake faruwa tare da aikawa nan take ga jami’an ’yan sandan dake kusa. A ranar 16 ga Yunin da ya gabata ne aka fara gwada ayyukan ’yan sandan na mutum-mutumi da nufin kara inganta amfani da su a birane.

An saya musu fasahar iya sadarwa, da yadda za su iya ba da taimakon aikin ’yan sanda ga masu yawon bude ido, da kula da zirga-zirgar ababen hawa, sannan da kansu suke kai kansu wurin caji don tabbatar da cewa aikinsu bai tsaya ba. Akwai abubuwan mamaki da yawa da wadannan ’yan sanda ke iya yi ciki har da gano mara lafiya a cikin masu yawon bude ido tare da kiran tawagar kawo daukin gaggawa.

Wannan fasaha za ta iya taimakon kasashenmu na Afirka wajen shawo kan matsalolin tsaro da dama duba da cewa har yanzu muna da karancin jami’an tsaro. Kididdigar da na gani daga shafin rumbun bayanai na Wikipedia na nuna cewa, a Nijeriya, mai yawan al’umma fiye da miliyan 230, duk dan sanda daya yana ba da tsaro ne ga kusan mutane 1000 ko kuma a ce duk ’yan sanda biyu suna kula ne da tsaron mutum 2,000. Kazalika, idan aka leka sauran kasashenmu na Afirka ma za a ga irin wannan gibin.

Labarai Masu Nasaba

Kamfanin Kasar Sin Ya Bayar Da Gudunmuwar Kayayyaki Ga Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Sudan Ta Kudu

An Kammala Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan

Idan za a yi amfani da wannan fasaha ta ’yan sandan mutum-mutumin inji ana iya rage yawan jami’ai da ake jibgewa a wuraren shafaffu da mai tare da kai su yankunan da ake fama da matsalar tsaro musamman na karkara.

Kar wani ya yi tunanin ko idan an dauki ’yan sanda daga birane zuwa karkara kamar an yi musu ba daidai ba, a’a, a ko ina aiki ya kama dole a je. Kuma da kudin kasa ake biyansu albashi ba kudin ’yan birni ba kawai. Su ma mazauna birane za su ci gajiyar hakan, don ’yan sandan mutum-mutumin za su yi aiki babu kakkautawa, tun da ba su bukatar barci, ko cin abinci, ko zaga bayi, da sauran wasu abubuwa na lalurorin dan’adam. Tabbas, amfani da su, zai kara yalwata jami’an ’yan sanda da ake bukata wurin gudanar da ayyukan tsaro ta yadda za a share wa al’umma hawaye ta fuskar matsalar tsaron da ake fama da ita.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Farashin Kayayyaki Sun Sauka A Watan Yuni 2025

Next Post

PDP Ba Za Ta Damu Da Rashin Atiku Ba – Gwamna Makinde

Related

Kamfanin Kasar Sin Ya Bayar Da Gudunmuwar Kayayyaki Ga Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Sudan Ta Kudu
Daga Birnin Sin

Kamfanin Kasar Sin Ya Bayar Da Gudunmuwar Kayayyaki Ga Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Sudan Ta Kudu

2 hours ago
An Kammala Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan
Daga Birnin Sin

An Kammala Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan

3 hours ago
Firaministan Sin Zai Halarci Babban Taron Mahawara Na MDD Karo Na 80
Daga Birnin Sin

Firaministan Sin Zai Halarci Babban Taron Mahawara Na MDD Karo Na 80

4 hours ago
Shugaba Xi ya zanta ta wayar tarho da takwaransa na Amurka
Daga Birnin Sin

Shugaba Xi ya zanta ta wayar tarho da takwaransa na Amurka

5 hours ago
Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Bunkasa Ci Gaban Mata
Daga Birnin Sin

Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Bunkasa Ci Gaban Mata

6 hours ago
Ofishin Yada Labarai Na Majalisar Gudanarwar Kasar Sin Ya Fitar Da Takardar Bayani Mai Taken “Nasarar Aiwatar Da Manufar JKS A Xinjiang A Sabon Zamani”
Daga Birnin Sin

Ofishin Yada Labarai Na Majalisar Gudanarwar Kasar Sin Ya Fitar Da Takardar Bayani Mai Taken “Nasarar Aiwatar Da Manufar JKS A Xinjiang A Sabon Zamani”

7 hours ago
Next Post
PDP Ba Za Ta Damu Da Rashin Atiku Ba – Gwamna Makinde

PDP Ba Za Ta Damu Da Rashin Atiku Ba – Gwamna Makinde

LABARAI MASU NASABA

Kamfanin Kasar Sin Ya Bayar Da Gudunmuwar Kayayyaki Ga Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Sudan Ta Kudu

Kamfanin Kasar Sin Ya Bayar Da Gudunmuwar Kayayyaki Ga Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Sudan Ta Kudu

September 19, 2025
Yadda Ciwon Hanta Ke Yaɗuwa Tsakanin Ma’aurauta

Yadda Ciwon Hanta Ke Yaɗuwa Tsakanin Ma’aurauta

September 19, 2025
An Kammala Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan

An Kammala Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan

September 19, 2025
Firaministan Sin Zai Halarci Babban Taron Mahawara Na MDD Karo Na 80

Firaministan Sin Zai Halarci Babban Taron Mahawara Na MDD Karo Na 80

September 19, 2025
Shugaba Xi ya zanta ta wayar tarho da takwaransa na Amurka

Shugaba Xi ya zanta ta wayar tarho da takwaransa na Amurka

September 19, 2025
Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

September 19, 2025
Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

September 19, 2025
Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Bunkasa Ci Gaban Mata

Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Bunkasa Ci Gaban Mata

September 19, 2025
Ofishin Yada Labarai Na Majalisar Gudanarwar Kasar Sin Ya Fitar Da Takardar Bayani Mai Taken “Nasarar Aiwatar Da Manufar JKS A Xinjiang A Sabon Zamani”

Ofishin Yada Labarai Na Majalisar Gudanarwar Kasar Sin Ya Fitar Da Takardar Bayani Mai Taken “Nasarar Aiwatar Da Manufar JKS A Xinjiang A Sabon Zamani”

September 19, 2025
Afirka

Tarihin Ahmadu Bello Sardaunan Sakkwato Firimiyan Arewa

September 19, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.