ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 20, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Fasahar Amfani Da ’Yan Sandan Mutum-Mutumi Ta Kasar Sin Na Iya Taimaka Wa Tsaro A Afirka

by CGTN Hausa and Sulaiman
11 months ago
Afirka

Ko makaho ya shafa, ya san yadda kimiyya da fasaha ke ci gaba taka gagarumar muhimmiyar rawa wajen kawo sauyi a daukacin sassan rayuwar bil’adama ta yau da kullum a duk fadin duniya. Kasar Sin na ci gaba da amfani da fasahohinta na zamanantarwa wajen kirkire-kirkire da kawo sabbin salo.

Da yake kasar tana shirin karbar bakuncin gasar wasannin motsa jiki ta duniya ta shekarar 2025 daga ranar 7 zuwa 17 ga Agusta, yanzu haka ta kera wasu mutum-mutumi na ’yan sanda da suka fara sintiri a hukumance a birnin Chengdu dake lardin Sichuan na yankin kudu maso yammacin kasar.

  • ‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
  • An Fara Binciken Mutuwar Wasu Ɗalibai 2 A Makarantar Kwana A Kano

’Yan sandan mutum-mutumin sun tsunduma aiki tare da jami’ai abokan aikinsu a dandalin Tianfu, daya daga cikin wuraren da aka fi samun kai-komon mutane da kafa a kalla 100,000 a kullum. Da kansu suke sauya wurin aiki a tsakaninsu duk bayan awa biyu zuwa uku inda suke nadar murya da bidiyon abubuwan dake faruwa tare da aikawa nan take ga jami’an ’yan sandan dake kusa. A ranar 16 ga Yunin da ya gabata ne aka fara gwada ayyukan ’yan sandan na mutum-mutumi da nufin kara inganta amfani da su a birane.

ADVERTISEMENT

An saya musu fasahar iya sadarwa, da yadda za su iya ba da taimakon aikin ’yan sanda ga masu yawon bude ido, da kula da zirga-zirgar ababen hawa, sannan da kansu suke kai kansu wurin caji don tabbatar da cewa aikinsu bai tsaya ba. Akwai abubuwan mamaki da yawa da wadannan ’yan sanda ke iya yi ciki har da gano mara lafiya a cikin masu yawon bude ido tare da kiran tawagar kawo daukin gaggawa.

Wannan fasaha za ta iya taimakon kasashenmu na Afirka wajen shawo kan matsalolin tsaro da dama duba da cewa har yanzu muna da karancin jami’an tsaro. Kididdigar da na gani daga shafin rumbun bayanai na Wikipedia na nuna cewa, a Nijeriya, mai yawan al’umma fiye da miliyan 230, duk dan sanda daya yana ba da tsaro ne ga kusan mutane 1000 ko kuma a ce duk ’yan sanda biyu suna kula ne da tsaron mutum 2,000. Kazalika, idan aka leka sauran kasashenmu na Afirka ma za a ga irin wannan gibin.

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Ziyartar Kasar Sin Sau 13 Shugaban Myanmar Na Da Mahanga Dangane Da Salon Zamanantarwa Irin Ta Sin

Kamfanonin Kasa Da Kasa Na Rungumar Manufar Hadin Gwiwa Da Samun Ci Gaba Tare Da Kasar Sin A Fannin Kirkire-kirkire

Idan za a yi amfani da wannan fasaha ta ’yan sandan mutum-mutumin inji ana iya rage yawan jami’ai da ake jibgewa a wuraren shafaffu da mai tare da kai su yankunan da ake fama da matsalar tsaro musamman na karkara.

Kar wani ya yi tunanin ko idan an dauki ’yan sanda daga birane zuwa karkara kamar an yi musu ba daidai ba, a’a, a ko ina aiki ya kama dole a je. Kuma da kudin kasa ake biyansu albashi ba kudin ’yan birni ba kawai. Su ma mazauna birane za su ci gajiyar hakan, don ’yan sandan mutum-mutumin za su yi aiki babu kakkautawa, tun da ba su bukatar barci, ko cin abinci, ko zaga bayi, da sauran wasu abubuwa na lalurorin dan’adam. Tabbas, amfani da su, zai kara yalwata jami’an ’yan sanda da ake bukata wurin gudanar da ayyukan tsaro ta yadda za a share wa al’umma hawaye ta fuskar matsalar tsaron da ake fama da ita.

Afirka
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sakamakon Ziyartar Kasar Sin Sau 13 Shugaban Myanmar Na Da Mahanga Dangane Da Salon Zamanantarwa Irin Ta Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Kamfanonin Kasa Da Kasa Na Rungumar Manufar Hadin Gwiwa Da Samun Ci Gaba Tare Da Kasar Sin A Fannin Kirkire-kirkire
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Na Kira Ga Al’ummun Kasa Da Kasa Da Su Himmatu Wajen Tallafawa Ayyukan Jin kai
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Jarin Waje Ya Inganta Hada-hadar Zuba Jari A Kasar Sin
Afirka
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Duk Da Rashin Halartar ‘Super Eagles’ Gasar Kofin Duniya, Nijeriya Ba Ta Rasa Wakilai Ba
  • Sulaiman
    Sakamakon Ziyartar Kasar Sin Sau 13 Shugaban Myanmar Na Da Mahanga Dangane Da Salon Zamanantarwa Irin Ta Sin
  • Sulaiman
    Hijira: Malaman Musulunci Sun Buƙaci  Musulmi Su Yi Riƙo Da Gaskiya Da Adalci
  • Sulaiman
    Kamfanonin Kasa Da Kasa Na Rungumar Manufar Hadin Gwiwa Da Samun Ci Gaba Tare Da Kasar Sin A Fannin Kirkire-kirkire

MASU ALAKA

Sakamakon Ziyartar Kasar Sin Sau 13 Shugaban Myanmar Na Da Mahanga Dangane Da Salon Zamanantarwa Irin Ta Sin
Daga Birnin Sin

Sakamakon Ziyartar Kasar Sin Sau 13 Shugaban Myanmar Na Da Mahanga Dangane Da Salon Zamanantarwa Irin Ta Sin

June 20, 2026
Kamfanonin Kasa Da Kasa Na Rungumar Manufar Hadin Gwiwa Da Samun Ci Gaba Tare Da Kasar Sin A Fannin Kirkire-kirkire
Daga Birnin Sin

Kamfanonin Kasa Da Kasa Na Rungumar Manufar Hadin Gwiwa Da Samun Ci Gaba Tare Da Kasar Sin A Fannin Kirkire-kirkire

June 20, 2026
Sin Na Kira Ga Al’ummun Kasa Da Kasa Da Su Himmatu Wajen Tallafawa Ayyukan Jin kai
Daga Birnin Sin

Sin Na Kira Ga Al’ummun Kasa Da Kasa Da Su Himmatu Wajen Tallafawa Ayyukan Jin kai

June 20, 2026
Next Post
PDP Ba Za Ta Damu Da Rashin Atiku Ba – Gwamna Makinde

PDP Ba Za Ta Damu Da Rashin Atiku Ba – Gwamna Makinde

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Wasa 23 Da Eric Chelle Ya Gayyata Domin Buga Wasannin Sada Zumunci 

Duk Da Rashin Halartar ‘Super Eagles’ Gasar Kofin Duniya, Nijeriya Ba Ta Rasa Wakilai Ba

June 20, 2026
Sakamakon Ziyartar Kasar Sin Sau 13 Shugaban Myanmar Na Da Mahanga Dangane Da Salon Zamanantarwa Irin Ta Sin

Sakamakon Ziyartar Kasar Sin Sau 13 Shugaban Myanmar Na Da Mahanga Dangane Da Salon Zamanantarwa Irin Ta Sin

June 20, 2026
Darussan Da Suka Fi Dacewa A Fahimta Daga Alkur’ani A Wannan Zamanin (2)

Hijira: Malaman Musulunci Sun Buƙaci  Musulmi Su Yi Riƙo Da Gaskiya Da Adalci

June 20, 2026
Kamfanonin Kasa Da Kasa Na Rungumar Manufar Hadin Gwiwa Da Samun Ci Gaba Tare Da Kasar Sin A Fannin Kirkire-kirkire

Kamfanonin Kasa Da Kasa Na Rungumar Manufar Hadin Gwiwa Da Samun Ci Gaba Tare Da Kasar Sin A Fannin Kirkire-kirkire

June 20, 2026
Nijeriya

An Nemi Shugabanni Su Rungumi Tafarkin Adalci A Tsakanin Al’ummunsu

June 20, 2026
Sin Na Kira Ga Al’ummun Kasa Da Kasa Da Su Himmatu Wajen Tallafawa Ayyukan Jin kai

Sin Na Kira Ga Al’ummun Kasa Da Kasa Da Su Himmatu Wajen Tallafawa Ayyukan Jin kai

June 20, 2026
Sojoji Sun Kashe Mayakan Boko Haram 6, Sun Kama Wasu A Borno

Sojoji Sun Ceto Mutane 22 A Jihar Sakkwato

June 20, 2026
A Duba Halin Da Masu Buƙata Ta Musamman Ke Ciki

A Duba Halin Da Masu Buƙata Ta Musamman Ke Ciki

June 20, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto

Ƴan Bindiga Sun Tilasta Wa Ƙauyukan Sakkwato Biyan Sabon Haraji

June 20, 2026
IMF

Tattalin Arziƙin Ƙasa: Masana Sun Buƙaci Tinubu Ya Yi Hattara Da Shawarar IMF

June 20, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.