• English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Fayemi Ga Ganduje: Ka Rika Fada Wa Tinubu Gaskiyar Halin Da APC Ke Ciki

byYusuf Shuaibu
2 years ago
Fayemi

Tsohon gwamnan Jihar Ekiti, Dakta Kayode Fayemi, ya bukaci shugaban jam’iyyar APC na kasa, Dakta Abdullahi Umar Ganduje, da ya fito fili ya fada wa shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ainihin halin da ake ciki a APC, ba bayanin da yake samu a cikin fadar shugaban kasa ba.

Fayemi wanda ya kasance tsohon shugaban kungiyar gwamnonin Nijeriya (NGF), ya yi wannan kira ne ga Ganduje a yayin kaddamar da wani littafi mai suna “Yadda APC ke gudanar da siyasarta”, wanda tsohon mataimakin shugaban jam’iyyar APC na kasa na yankin  Arewa maso yamma, Salihu Mohammed Lukman ya rubuta, da ya gudana a Abuja.

  • Kamfanonin Jamus 22 Za Su Zuba Jarin Fam Biliyan 3 A Nijeriya
  • Kwankwaso A Sikeli Bayan Hukuncin Kotun Koli

Taron ya samu halartar fitattun jagororin jam’iyyar APC da suka hada da Ganduje da tsaffin shugabannin jam’iyyar APC na kasa, Adams Oshiomhole da Cif Bisi Akande da wakilan mataimakin shugaban kasa, Farfesa Yemi Osinbajo da na shugaban majalisar wakilai, Tajuddeen Abbas da mambobin kwamitin gudanarwa na kasa da sauransu.

Fayemi ya ce, “Na yi farin ciki da shugaban jam’iyyarmu ya zo wannan wuri. Wannan jam’iyyar bai kamata ta zama ‘yar kallo ba wajen tsara manufofin gwamnati. Ya kamata jam’iyya ta zama ita ce za ta tsara manufofin gwamnati. Ya kamata wannan gwamnati da dinga bin manufofin jam’iyya wajen aiwatar da tsare-tsarenta wadanda suka dace domin kawo wa al’umma sauki, ba wai abin da shugaban kasa yake ji a fadar shugaban kasa ba.

“Dukkanmu mun taba rike mukamin gwamnati kuma mun san yadda al’amura suke. Na yi farin ciki da shugabanmu ya tabbatar da cewa zai karanta wannan littafin. Kamata ya yi ya zama wajibi a karanta wa dukkan ‘ya’yan kwamitin gudanarwa na jam’iyyar APC da shugabanni a matakin jiha da na unguwanni domin mu fara aikin sake gina jam’iyyarmu wadda na yi imanin Dakta Abdullahi Umar Ganduje zai jajirce a kai.”

LABARAI MASU NASABA

ADC Ta Umarci Dukkan Mambobinta Su Yi Murabus Daga Tsoffin Jam’iyyunsu

Dage Zaben Shugabannin PDP Na Jihohi Ya Kara Ruruta Wutar Rikici A Jam’iyyar

A nasa jawabin, Ganduje ya ce jam’iyyar APC na bukatar a samar da tsari mai kyau tare da mayar da hankali wajen biyan bukatun al’ummar Nijeriya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

ADC Ta Dakatar Da Shugabanta Da Wasu Jiga-jigai 3 A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ta Umarci Dukkan Mambobinta Su Yi Murabus Daga Tsoffin Jam’iyyunsu

October 3, 2025
Dage Zaben Shugabannin PDP Na Jihohi Ya Kara Ruruta Wutar Rikici A Jam’iyyar
Tambarin Dimokuradiyya

Dage Zaben Shugabannin PDP Na Jihohi Ya Kara Ruruta Wutar Rikici A Jam’iyyar

October 3, 2025
Yadda Na Kawo Karshen Yajin Aikin ASUU Cikin Kwana Daya – Jonathan
Tambarin Dimokuradiyya

Lalacewar Tsarin Zabe Babbar Barazana Ce Ga Dorewar Dimokuradiyyar Afirka — Jonathan

September 27, 2025
Next Post
Sauran Gwarazan Shekara Na Kamfanin LEADERSHIP A 2023

Sauran Gwarazan Shekara Na Kamfanin LEADERSHIP A 2023

LABARAI MASU NASABA

An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025
Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

October 7, 2025
Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

October 7, 2025
Tinubu

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Kan Karɓo Bashin Dala Biliyan $2.347 Da $500m Na Sukuk 

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version