ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Fayemi Ga Ganduje: Ka Rika Fada Wa Tinubu Gaskiyar Halin Da APC Ke Ciki

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
Fayemi

Tsohon gwamnan Jihar Ekiti, Dakta Kayode Fayemi, ya bukaci shugaban jam’iyyar APC na kasa, Dakta Abdullahi Umar Ganduje, da ya fito fili ya fada wa shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ainihin halin da ake ciki a APC, ba bayanin da yake samu a cikin fadar shugaban kasa ba.

Fayemi wanda ya kasance tsohon shugaban kungiyar gwamnonin Nijeriya (NGF), ya yi wannan kira ne ga Ganduje a yayin kaddamar da wani littafi mai suna “Yadda APC ke gudanar da siyasarta”, wanda tsohon mataimakin shugaban jam’iyyar APC na kasa na yankin  Arewa maso yamma, Salihu Mohammed Lukman ya rubuta, da ya gudana a Abuja.

  • Kamfanonin Jamus 22 Za Su Zuba Jarin Fam Biliyan 3 A Nijeriya
  • Kwankwaso A Sikeli Bayan Hukuncin Kotun Koli

Taron ya samu halartar fitattun jagororin jam’iyyar APC da suka hada da Ganduje da tsaffin shugabannin jam’iyyar APC na kasa, Adams Oshiomhole da Cif Bisi Akande da wakilan mataimakin shugaban kasa, Farfesa Yemi Osinbajo da na shugaban majalisar wakilai, Tajuddeen Abbas da mambobin kwamitin gudanarwa na kasa da sauransu.

ADVERTISEMENT

Fayemi ya ce, “Na yi farin ciki da shugaban jam’iyyarmu ya zo wannan wuri. Wannan jam’iyyar bai kamata ta zama ‘yar kallo ba wajen tsara manufofin gwamnati. Ya kamata jam’iyya ta zama ita ce za ta tsara manufofin gwamnati. Ya kamata wannan gwamnati da dinga bin manufofin jam’iyya wajen aiwatar da tsare-tsarenta wadanda suka dace domin kawo wa al’umma sauki, ba wai abin da shugaban kasa yake ji a fadar shugaban kasa ba.

“Dukkanmu mun taba rike mukamin gwamnati kuma mun san yadda al’amura suke. Na yi farin ciki da shugabanmu ya tabbatar da cewa zai karanta wannan littafin. Kamata ya yi ya zama wajibi a karanta wa dukkan ‘ya’yan kwamitin gudanarwa na jam’iyyar APC da shugabanni a matakin jiha da na unguwanni domin mu fara aikin sake gina jam’iyyarmu wadda na yi imanin Dakta Abdullahi Umar Ganduje zai jajirce a kai.”

LABARAI MASU NASABA

Zaben Fitar Da Gwani Na APC: Tinubu Zai Shiga Tsakani Wajen Warware Rikicin Jam’iyyar

2027:Gwamnoni Na Fuskantar Turjiya Wajen Gwagwarmayar Kare Kujerunsu Da Kuma Samar Da Magadansu

A nasa jawabin, Ganduje ya ce jam’iyyar APC na bukatar a samar da tsari mai kyau tare da mayar da hankali wajen biyan bukatun al’ummar Nijeriya.

Fayemi
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Matsalar Tsaro Da Tsadar Kayan Noma Na Barazana Ga Samar Da Abinci A Daminar Bana
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Zaben Fitar Da Gwani Na APC: Tinubu Zai Shiga Tsakani Wajen Warware Rikicin Jam’iyyar
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027:Gwamnoni Na Fuskantar Turjiya Wajen Gwagwarmayar Kare Kujerunsu Da Kuma Samar Da Magadansu
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Masana Tattalin Arziki Sun Yi Watsi Da Rahoton NBS Kan Tattalin Arziki

MASU ALAKA

Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP
Tambarin Dimokuradiyya

Zaben Fitar Da Gwani Na APC: Tinubu Zai Shiga Tsakani Wajen Warware Rikicin Jam’iyyar

June 5, 2026
2027:Gwamnoni Na Fuskantar Turjiya Wajen Gwagwarmayar Kare Kujerunsu Da Kuma Samar Da Magadansu
Tambarin Dimokuradiyya

2027:Gwamnoni Na Fuskantar Turjiya Wajen Gwagwarmayar Kare Kujerunsu Da Kuma Samar Da Magadansu

June 5, 2026
Fayemi
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Rashin Hadin Kan Atiku Da Obi Da Kwankwaso Na Iya Taimaka Wa Tazarcen Tinubu

May 16, 2026
Next Post
Sauran Gwarazan Shekara Na Kamfanin LEADERSHIP A 2023

Sauran Gwarazan Shekara Na Kamfanin LEADERSHIP A 2023

LABARAI MASU NASABA

An Kashe ’Yan Bindiga Biyu A Abuja

An Kashe ’Yan Bindiga Biyu A Abuja

June 10, 2026
Ko Me Ya Sa Alkaluman Rahotan Cinikayyar Waje Na Sin Suka Nuna Karuwar Nasarori Fiye Da Yadda Aka Yi Tsammani?

Ko Me Ya Sa Alkaluman Rahotan Cinikayyar Waje Na Sin Suka Nuna Karuwar Nasarori Fiye Da Yadda Aka Yi Tsammani?

June 10, 2026
Mamakon Ruwan Sama Da Iska Mai Ƙarfi Ya Kashe Kaka Da Jikarta A Bauchi

Mamakon Ruwan Sama Da Iska Mai Ƙarfi Ya Kashe Kaka Da Jikarta A Bauchi

June 10, 2026
An Bude Bikin Kasa Da Kasa Na Makon Nuna Fina-Finan Zane Mai Motsi Na Chongqing Na 2026

An Bude Bikin Kasa Da Kasa Na Makon Nuna Fina-Finan Zane Mai Motsi Na Chongqing Na 2026

June 10, 2026
Babban Yankin Kasar Sin Ta Soki ‘Yan Jam’iyyar DPP Na Taiwan Kan Yadda Suka Kaskantar Da Kansu Ga Kasashen Waje

Babban Yankin Kasar Sin Ta Soki ‘Yan Jam’iyyar DPP Na Taiwan Kan Yadda Suka Kaskantar Da Kansu Ga Kasashen Waje

June 10, 2026
An Gudanar Da Taron Kirkire-Kirkire Na Duniya Na Kafafen Yada Labarai Karo Na Biyar

An Gudanar Da Taron Kirkire-Kirkire Na Duniya Na Kafafen Yada Labarai Karo Na Biyar

June 10, 2026
Hakimin Da Aka Sace A Jihar Kogi Ya Shaki Iskar ‘Yanci

An Daƙile Yunƙurin Sace Ɗalibai Masu Zana Jarabawar WASSCE A Kogi

June 10, 2026
Kamfanin Kasar Sin Ya Kammala Wani Muhimmin Titi A Fadar Mulkin Nijeriya

Kamfanin Kasar Sin Ya Kammala Wani Muhimmin Titi A Fadar Mulkin Nijeriya

June 10, 2026
Cudanyar Al’Adu Tana Tabbatar Da Kyakkyawar Makomar Sin Da Afirka 

Cudanyar Al’Adu Tana Tabbatar Da Kyakkyawar Makomar Sin Da Afirka 

June 10, 2026
’Yansanda Sun Kama ’Yan Bindiga 17 Tare Da Kashe 3 A Abuja

Babu Makarantar Da Aka Kai Wa Hari A Neja – ‘Yansanda

June 10, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.