• English
  • Business News
Saturday, September 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Fintiri Ya Gabatar Da Kasafin Kudi Fiye Da Naira Biliyan 486 Ga Majalisar Dokokin Adamawa

by Muh'd Shafi'u Saleh and Sulaiman
9 months ago
in Manyan Labarai
0
Fintiri Ya Gabatar Da Kasafin Kudi Fiye Da Naira Biliyan 486 Ga Majalisar Dokokin Adamawa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan jihar Adamawa, Ahmadu Umaru Fintiri, ya gabatar da kudirin kasafin kudin shekarar 2025 na Naira biliyan 486.218 a gaban majalisar dokokin jihar a ranar Litinin. 

 

A cewar Gwamnan, a lokacin da yake gabatar da kasafin mai taken “Budget of Service” ga majalisar dokokin jihar ya ce kasafin kudin da ake shirin yi ya nuna karin kashi dari bisa dari idan aka kwatanta da kasafin kudin shekarar 2024.

  • Da Ɗumi-ɗumi: Majalisar Dokokin Jihar Adamawa Ta Amince Da Ƙudirin Ƙirƙiro Sabbin Gundumomi

Finitiri ya ce daga cikin kasafin kudi na naira biliyan 486 na kudaden da ake kashewa a kai a kai za su kai naira biliyan 137, wato kashi 28.23%, ragowar Naira biliyan 348, wato kashi 71.77%, za a kashesu ga manyan ayyuka.

 

Labarai Masu Nasaba

Mutanen Gari Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Wasu A Sakkwato

NUPENG Za Ta Fara Yajin Aiki, Dangote Na Shirin Shiga Harkar Sufurin Mai

Ya ce gwamnatinsa ta yi alkawarin cimma manufofinta guda takwas, wato tsaro, samar da ababen more rayuwa, kiwon lafiya, wadatar abinci, da ilimi a cikin wannan kasafin kudin 2025.

 

Gwamna Fintiri ya ce an kuma ware kasafin Naira biliyan 88 domin gina tituna a fadin jihar, ya bayyana kudirin gwamnatin na inganta hanyoyin sufurin kayayyaki a jihar.

 

“Muna sa ne da muhimmancin da ya wajaba a kanmu na hada garuruwa da hanyoyin mota domin saukaka wa da fadada tattalin arzikinmu cikin gaggawa,” in ji shi.

 

Majalisar karkashin jagorancin kakakin majalisar Rt. Hon Bathiya Wesley, tun daga lokacin ta karanto kudirin dokar a karo na 2 kuma ta mika kudurin kasafin ga kwamitin kudi, da kasafin kudi domin tantancewa.

 

Karatu na biyu ya biyo bayan kudirin da shugaban masu rinjaye Hon. Kate Raymond Mamuno (Mazabar Demsa) da Hon. Musa Mahmud Kallamu (Mayo Belwa).

 

Da yake jawabi a takaice gabatar da kasafin kudin, shugaban majalisar Rt. Hon Bathiya Wesley, ta yabawa gwamnan bisa nasarar gabatar da kasafin kudin shekarar 2025.

 

Haka kuma ya bada tabbacin shirye shiryen majalisar karkashin jagorancinsa na yin duk abin da ya dace domin ganin an gaggauta zartar da kasafin kudin da ake son aiwatarwa a shekarar 2025.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Xi Ya Yi Kira Da A Kara Azamar Cimma Sabbin Nasarori A Fannin Zamanantarwa Yayin Da Ake Bikin Cikar Qiao Shi Shekaru 100 Da Haihuwa

Next Post

Gwamnan Kano Ya Naɗa Tsohon Shugaban Ma’aikatan Jihar Da Wasu 5 A Matsayin Kwamishinoni

Related

Mutanen Gari Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Wasu A Sakkwato
Manyan Labarai

Mutanen Gari Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Wasu A Sakkwato

2 hours ago
NUPENG Za Ta Fara Yajin Aiki, Dangote Na Shirin Shiga Harkar Sufurin Mai
Manyan Labarai

NUPENG Za Ta Fara Yajin Aiki, Dangote Na Shirin Shiga Harkar Sufurin Mai

9 hours ago
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 2 Da Wasu 156 Kan Aikata Laifuka A Jigawa

24 hours ago
Sojoji Sun Kwato Makamai Da Babura, Sun Ceto Mutane 3 A Kaduna 
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kama Ɗan Bindiga Ɗauke Da Makamai A Jihar Filato

1 day ago
Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai
Da ɗumi-ɗuminsa

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai

1 day ago
Ministan Tsaro
Manyan Labarai

Dawowar Matsalar Tsaro: Ta Haifar Da Cece-kuce Kan Daukar Matakin Kare Kai

2 days ago
Next Post
Kano

Gwamnan Kano Ya Naɗa Tsohon Shugaban Ma’aikatan Jihar Da Wasu 5 A Matsayin Kwamishinoni

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Fara Binciken Yadda Matasa Suka Kone Wata Mata Har Lahira A Neja

‘Yansanda Sun Fara Binciken Yadda Matasa Suka Kone Wata Mata Har Lahira A Neja

September 6, 2025
Mutanen Gari Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Wasu A Sakkwato

Mutanen Gari Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Wasu A Sakkwato

September 6, 2025
Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa

Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa

September 6, 2025
Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON

Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON

September 6, 2025
Gwamnatin Kogi Ta Jaddada Aniyar Magance Ambaliya Da Zaizayar Ƙasa

Gwamnatin Kogi Ta Jaddada Aniyar Magance Ambaliya Da Zaizayar Ƙasa

September 6, 2025
Zulum Ya Ba Da Tallafin ₦300,000 Ga Iyaye, Da Ciyar Da Ɗalibai 90 Kyauta A Borno

Zulum Ya Ba Da Tallafin ₦300,000 Ga Iyaye, Da Ciyar Da Ɗalibai 90 Kyauta A Borno

September 6, 2025
A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho

Kungiyoyi Da Abokan Arziki Na Ci Gaba Da Taya Dantsoho Murna

September 6, 2025
Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC

Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC

September 6, 2025
Tsohon Mataimakin Gwamnan Gombe Da Wasu jigogin PDP Sun Koma APC

Tsohon Mataimakin Gwamnan Gombe Da Wasu jigogin PDP Sun Koma APC

September 6, 2025

Ilimi Shi Ne Matakin Nasarar Rayuwar Duniya Da Lahira – Yerima Shettima

September 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.